< Maimaitawar Shari’a 13 >

1 In wani annabi ko mai mafarkai, ya bayyana a cikinku, ya kuma yi muku shelar wata alama mai banmamaki ko al’ajabi,
Ako ustane meðu vama prorok ili koji sne sanja, i kaže ti znak ili èudo,
2 in kuwa alamar, ko al’ajabin da annabin ya yi faɗin ya faru, ya kuma ce, “Bari mu bi waɗansu alloli (allolin da ba ku sani ba) mu kuma yi musu sujada,”
Pa se zbude taj znak ili èudo koje ti kaže, i on ti reèe: hajde da idemo za drugim bogovima, kojih ne znaš, i njima da služimo,
3 kada ku saurari kalmomin wannan annabi ko mai mafarki. Ubangiji Allahnku yana gwada ku ne don yă sani ko kuna ƙaunarsa da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku.
Nemoj poslušati što ti kaže taj prorok ili sanjaè, jer vas kuša Gospod Bog vaš da bi se znalo ljubite li Gospoda Boga svojega iz svega srca svojega i sve duše svoje.
4 Ubangiji Allahnku ne za ku bi, shi ne kuma za ku girmama. Ku kiyaye umarnansa, ku kuma yi masa biyayya; ku bauta masa, ku kuma manne masa.
Za Gospodom Bogom svojim idite, i njega se bojte; njegove zapovijesti èuvajte, i glas njegov slušajte, i njemu služite i njega se držite.
5 Dole a kashe wannan annabi ko mai mafarki, domin ya yi wa’azin tawaye ga Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar, ya fanshe ku daga ƙasar bauta; gama annabin nan ya yi ƙoƙari yă juye daga hanyar da Ubangiji Allahnku ya umarce ku, ku bi. Dole ku fid da mugu daga cikinku.
A onaj prorok ili sanjaè da se pogubi, jer vas je nagovarao da se odmetnete Gospoda Boga svojega, koji vas izvede iz zemlje Misirske i iskupi vas iz kuæe ropske, i odvraæao od puta koji ti je zapovjedio Gospod Bog tvoj da ideš njim; tako istrijebi zlo iz sebe.
6 In ɗan’uwanka, ko ɗanka, ko’yarka, ko matar da kake ƙauna, ko abokinka na kusa, a ɓoye ya ruɗe ka, yana cewa, “Mu je mu yi wa waɗansu alloli sujada” (allolin da ko kai, ko kakanninka ba su sani ba,
Ako bi te podbadao brat tvoj, sin matere tvoje, ili sin tvoj ili kæi tvoja, ili žena tvoja mila, ili prijatelj tvoj koji ti je kao duša tvoja, govoreæi ti tajno: hajde da služimo drugim bogovima, kojih nijesi znao ni ti ni oci tvoji,
7 allolin mutanen kewayenku, ko na kusa, ko na nisa, daga wannan ƙarshen ƙasar zuwa wancan),
Izmeðu bogova drugih naroda koji su oko vas, blizu ili daleko od tebe, od jednoga kraja zemlje do drugoga,
8 kada ka yarda da shi, kada ma ka saurare shi. Kada ka ji tausayinsa. Kada ka haƙura da shi, ko ka tsare shi.
Ne pristaj s njim niti ga poslušaj; neka ga ne žali oko tvoje, i nemoj mu se smilovati niti ga taji,
9 Dole ka kashe shi. Dole hannunka yă zama na farko a kisansa, sa’an nan hannuwan sauran dukan mutane.
Nego ga ubij: tvoja ruka nek se prva digne na nj da ga ubiješ, pa onda ruka svega naroda.
10 Ku jajjefe shi da duwatsu har sai ya mutu, domin ya yi ƙoƙari yă juye ku daga Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar, daga ƙasar bauta kuma.
Zaspi ga kamenjem da pogine; jer te šæaše odvratiti od Gospoda Boga tvojega, koji te je izveo iz zemlje Misirske, iz kuæe ropske;
11 Sa’an nan dukan Isra’ila za su ji su kuma tsorata, babu kuma wani a cikinku da zai ƙara yin irin wannan mugun abu.
Da sav Izrailj èuje i boji se, i da se više ne uèini tako zlo meðu vama.
12 In kuka ji an yi magana a kan wani daga cikin biranen da Ubangiji Allahnku yake ba ku ku zauna a ciki
Ako za kakav grad svoj, koji ti Gospod Bog tvoj da da u njemu živiš, èuješ gdje govore:
13 cewa mugaye sun taso a cikinku, suna rikitar da mutane a birni, suna cewa, “Mu je mu yi wa waɗansu alloli sujada” (allolin da ba ku sani ba),
Izidoše ljudi nevaljali izmeðu tebe i otpadiše sve koji žive u gradu njihovu, govoreæi: hajde da služimo drugim bogovima, kojih ne poznajete,
14 to, sai ku bincike labarin sosai a hankali. In kuwa gaskiya ne, an kuma tabbatar wannan abin ƙyama ya faru a cikinku,
Tada istraži i raspitaj, izvidi dobro, pa ako bude istina i doista se uèinila ona gadna stvar meðu vama,
15 dole a karkashe dukan waɗanda suke zama a wannan birni da takobi. Ku hallaka su ƙaƙaf, ku karkashe mutanen birnin da kuma dabbobinsa.
Pobij maèem sve koji žive u gradu onom, i zatri i njega i sve što bi u njemu bilo, i stoku maèem pobij.
16 Ku tattara dukan ganimar birnin a tsakiyar gari, ku ƙone birnin da kuma ganimar ƙurmus a matsayin hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji Allahnku. Birnin zai kasance kufai har abada, kada a sāke gina shi.
I sav plijen iz njega skupi nasred ulice njegove, spali ognjem i onaj grad i sav plijen iz njega Gospodu Bogu svojemu, da bude gomila dovijeka i da se više ne sazida.
17 Ba za a iske wani daga cikin abubuwan nan da aka haramta a hannuwanku ba, saboda Ubangiji yă juya daga fushinsa mai ƙuna, yă nuna jinƙai, yă ji tausayinku, yă kuma ƙara yawanku, kamar yadda ya alkawarta da rantsuwa ga kakanninku,
I neka ti od prokletijeh stvari ne prione ništa za ruku, eda bi se Gospod povratio od žestine gnjeva svojega, uèinio ti milost i smilovao se na te, i umnožio te, kao što se zakleo ocima tvojim,
18 domin kun yi biyayya da Ubangiji Allahnku, kuna kiyaye dukan umarnan da nake ba ku a yau, kuna kuma aikata abin da yake daidai a idanunsa.
Kad slušaš glas Gospoda Boga svojega držeæi sve zapovijesti njegove, koje ti ja danas zapovijedam, da bi èinio što je pravo pred Gospodom Bogom tvojim.

< Maimaitawar Shari’a 13 >