< Maimaitawar Shari’a 12 >
1 Waɗannan su ne ƙa’idodi da kuma dokokin da za ku lura, ku kuma kiyaye a ƙasar da Ubangiji, Allahn kakanninku, yake ba ku don ku ci gādonta, muddin kuna zama a ƙasar.
Desse äro de bud och rätter, som I hålla skolen, så att I gören derefter uti landena, som Herren dina fäders Gud dig gifvit hafver till att intaga, så länge I på jordene lefven.
2 Ku hallaka dukan wuraren da al’umman da kuke kora suke yi wa allolinsu sujada, a kan duwatsu masu tsawo, da a kan tuddai, da kuma ƙarƙashin kowane itace gaba ɗaya.
Förgörer all de rum, der Hedningarna, som I intagen, sina gudar tjent hafva, vare sig på hög berg, på backar, eller under grön trä;
3 Ku rurrushe bagadansu, ku farfashe keɓaɓɓun duwatsunsu, ku kuma ƙone ginshiƙan Asheransu da wuta; ku yayyanka gumakan allolinsu, ku kuma shafe sunayensu daga waɗannan wurare.
Och bryter neder deras altare, och slår sönder deras stodar; och deras lundar uppbränner med eld, och deras afgudabeläte kaster bort, och tager bort deras namn utu det rummet.
4 Ba za ku yi wa Ubangiji Allahnku sujada a hanyar da suke yi ba.
I skolen icke så göra Herranom edrom Gud;
5 Amma sai ku nemi wurin da Ubangiji Allahnku zai zaɓa daga cikin dukan kabilanku, inda zai sa Sunansa, yă mai wurin mazauninsa. A wannan wuri ne za ku tafi;
Utan på det rum, som Herren edar Gud utväljer af allom edrom slägtom, att han vill låta sitt Namn der bo, der skolen I fråga, och dit komma;
6 a can ne kuma za ku kawo hadayun ƙonawa da sadakoki, zakkarku da kyautai na musamman, da abin da kuka yi alkawari za ku bayar, da hadayunku na yardar rai, da kuma’ya’yan farin garkunanku na shanu da na tumaki.
Och göra edart bränneoffer, och edor annor offer, och edor tiond, och edra händers häfoffer, och edor löfte, och edor friviljoga offer, och förstfödningena af edart fä och får.
7 A can, a gaban Ubangiji Allahnku, ku da iyalanku za su ci, su kuma yi farin ciki a kome da kuka sa hannunku a kai, domin Ubangiji Allahnku zai albarkace ku.
Och der skolen I äta för Herranom edrom Gud, och vara glade öfver allt det I och edor hus förvärfven, der Herren din Gud dig uti välsignat hafver.
8 Kada ku yi kamar yadda muke yi a nan yau, yadda kowa yake yin abin da ya ga dama.
I skolen intet göra af det vi i dag här görom, hvar och en som honom tycker rätt vara;
9 Gama ba ku kai wurin hutawa wanda Ubangiji Allahnku zai ba ku gādo ba tukuna.
Ty I ären ännu härtilldags icke komne till ro, eller till arfvedelen, som Herren din Gud dig gifva skall;
10 Amma sa’ad da kuka haye Urdun, kuka zauna a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku ita gādo, zai kuwa ba ku hutu daga dukan abokan gābanku da suke kewaye da ku, kuka sami zaman lafiya,
Men I måsten gå öfver Jordan, och bo i de landena, som Herren edar Gud eder till arfs utskiftandes varder; och han skall låta eder få ro för alla edra fiendar omkring eder, och I skolen bo trygge.
11 sai ku kai dukan abin da na umarce ku ku kai, wato, hadayu na ƙonawa, da sadakokinku, da zakkarku, da hadayunku na ɗagawa, da hadayunku na alkawarin da kuka yi wa Ubangiji a wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa yă sa sunansa.
När nu Herren din Gud utväljer ett rum, att hans Namn der bo skall, dit skolen I bära allt det jag bjuder eder: edart bränneoffer, edor annor offer, edor tiond, edra händers häfoffer, och all edor fri löfte, som I Herranom lofven;
12 A can kuma za ku yi farin ciki a gaban Ubangiji Allahnku, ku da’ya’yanku maza da mata, da bayinku maza da mata, da kuma Lawiyawa daga biranenku, waɗanda ba a ba su rabo ba, ba su kuma da gādo na kansu.
Och skolen vara glade för Herranom edrom Gud, I och edre söner, och edra döttrar, och edre tjenare, och edra tjenarinnor, och Leviterna, som i edra portar äro; förty de hafva ingen lott eller arfvedel med eder.
13 Ku kula fa kada ku miƙa hadayun ƙonawa a wani wurin da kuka ga dama.
Tag dig vara, att du icke offrar ditt bränneoffer i all de rum som du ser;
14 Ku miƙa su kawai a wurin da Ubangiji zai zaɓa a cikin ɗaya daga kabilanku, a can za ku yi kowane abin da na umarce ku.
Utan i det rum, som Herren utväljer, uti någro af dina slägter, der skall du offra ditt bränneoffer, och göra allt det jag bjuder dig.
15 Amma kwa iya yanka nama ku ci a garuruwanku, a duk lokacin da ranku yake so, kamar yadda ake yi da gada ko barewa, bisa ga albarkar da Ubangiji Allahnku yake sa muku. Marar tsarki da mai tsarki, duka za ku iya ci.
Dock må du slagta, och äta kött i alla dina portar, efter all dine själs begärelse, efter Herrans dins Guds välsignelse, som han dig gifvit hafver; både rene och orene måga det äta, såsom en rå eller en hjort.
16 Amma kada ku ci jini, ku zubar da shi a ƙasa kamar ruwa.
Men blodet skall du icke äta; utan gjuta det på jordena såsom vatten.
17 Kada ku ci zakkar hatsi, da na sabon inabi, da kuma na mai a biranenku, ko kuwa na’ya’yan fari na garkunanku na shanu da na tumaki, ko kuwa duk wani abin da kuka yi alkawari za ku bayar, ko hadayunku na yardar rai, ko kyautai na musamman.
Men icke må du äta i dina portar utaf tionden af din säd, dino vine, dine oljo, ej heller af den förstfödning af dino fä, af din får, eller af något ditt löfte, som du lofvat hafver, eller af ditt friviljoge offer, eller af dine hands häfoffer;
18 A maimakon haka, sai ku ci su a gaban Ubangiji Allahnku a wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa, da ku da’ya’yanku maza da mata, da bayinku maza da mata, da kuma Lawiyawa daga biranenku, ku kuwa yi farin ciki a gaban Ubangiji Allahnku a kowane abin da kuka sa hannunku.
Utan för Herranom dinom Gud skall du sådant äta på de rumme, som Herren din Gud utväljer, du och dine söner, dina döttrar, dine tjenare, dina tjenarinnor, och Leviten, som i dina portar är; och skall vara glad för Herranom dinom Gud, öfver allt det du dig företager.
19 Ku yi hankali, kada ku manta da Lawiyawa, muddin kuna zaune a ƙasarku.
Och tag dig vara, att du icke öfvergifver Leviten, så länge du lefver på jordene.
20 Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya fadada iyakarku kamar yadda ya yi muku alkawari, kuka kuma ji marmarin nama, kuka kuma ce, “Muna so mu ci nama,” to, za ku iya cin yadda kuke so.
När nu Herren din Gud varder förvidgandes dina landsändar, såsom han dig sagt hafver, och du säger: Jag vill äta kött; efter din själ lyster äta kött, så ät kött efter alla dine själs begärelse.
21 In wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa don yă sa Sunansa yana da nisa sosai daga inda kuke, za ku iya yankan dabbobi daga garkunanku na shanu da na tumakin da Ubangiji ya ba ku, kamar yadda na umarce ku, a cikin biranenku kuma za ku iya ci, yadda kuke so.
Är rummet långt ifrå dig, som Herren din Gud utvalt hafver, att han der vill låta bo sitt Namn, så slagta af ditt fä eller får, som Herren dig gifvit hafver, såsom jag dig budit hafver, och ät det i dinom portom, efter all dine själs begärelse.
22 Ku ci su yadda akan ci barewa ko mariri. Marar tsarki da mai tsarki, za ku iya ci.
Såsom man äter en rå eller en hjort, må du ätat; både rene och orene måga lika väl ätat.
23 Amma ku tabbata ba ku ci jinin ba, domin jini ne rai, ba kuwa za ku ci rai cikin naman ba.
Allenast vakta, att du icke äter blodet; ty blodet är själen, derföre skall du icke äta själena med köttet;
24 Ba za ku ci jini ba, ku zubar da shi a ƙasa kamar ruwa.
Utan skall gjuta det på jordena såsom vatten;
25 Kada ku ci shi, don ku zauna lafiya, da ku da’ya’yanku bayanku, gama za ku riƙa aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji.
Och skall fördenskull icke ätat, att dig må väl gå, och dinom barnom efter dig, deraf att du gjort hafver det som rätt är för Herranom.
26 Amma ku ɗauki abubuwa masu tsarki, da kuma duk abin da kuka yi alkawari za ku bayar, ku tafi inda Ubangiji ya zaɓa.
Men när du helgar något det ditt är, eller lofvar, så skall du tagat, och bära till det rum, som Herren utvalt hafver;
27 Ku miƙa hadayunku na ƙonawa a bagaden Ubangiji Allahnku, da naman da kuma jinin. Dole a zub da jinin hadayunku a gindin bagaden Ubangiji Allahnku, amma za ku iya cin naman.
Och göra ditt bränneoffer, med kött och blod, på Herrans dins Guds altare; blodet af ditt offer skall du gjuta på Herrans dins Guds altare, och äta köttet.
28 Ku yi hankali, ku yi biyayya da dukan waɗannan umarnan da nake ba ku, da kuma’ya’yanku, don ku zauna lafiya, da ku da’ya’yanku a bayanku, gama za ku riƙa aikata abin da yake daidai da kuma yake mai kyau a gaban Ubangiji Allahnku.
Se till, och hör alla dessa orden, som jag bjuder dig; på det dig må väl gå, och dinom barnom efter dig till evig tid, deraf att du gjort hafver det rätt är, och Herranom dinom Gud behageligit.
29 Ubangiji Allahnku zai kawar muku da al’umman nan da kuke niyyar shiga cikin ƙasarsu don ku kore su, bayan kuka kore su, kuka kuma zauna a ƙasarsu,
När Herren din Gud utrotar Hedningarna för dig, der du inkommer till att intaga dem, och du dem intagit hafver, och bor i deras land;
30 to, sai ku lura, kada ku jarrabtu ku kwaikwaye su bayan da an riga an shafe su daga gabanku, kada ku tambayi kome game da allolinsu, kuna cewa, “Yaya waɗannan al’ummai suke bauta wa allolinsu? Mu ma za mu yi kamar yadda suka yi.”
Så tag dig vara, att du icke faller i snarona efter dem, sedan de fördrefne äro för dig; och att du intet söker efter deras gudar, och säger: Såsom detta folk hafver tjent deras gudar, så vill jag ock göra.
31 Ba za ku yi wa Ubangiji Allahnku sujada a hanyar da suke yi ba, gama a cikin yin sujada wa allolinsu, sun yi dukan abubuwan banƙyaman da Ubangiji yake ƙi. Har ma sukan ƙone’ya’yansu maza da mata a wuta a matsayin hadayu.
Du skall icke således göra Herranom dinom Gud; förty de hafva gjort sinom gudom allt det Herranom stygges vid, och det han hatar; ty de hafva ock uppbränt i elde sina söner och döttrar till sina gudar.
32 Ku lura, ku aikata dukan abin da na umarce ku; kada ku ƙara, kada ku rage daga cikin.
Allt det jag bjuder eder, det skolen I hålla, så att I gören derefter. I skolen intet lägga dertill, och intet taga derifrå.