< Maimaitawar Shari’a 12 >

1 Waɗannan su ne ƙa’idodi da kuma dokokin da za ku lura, ku kuma kiyaye a ƙasar da Ubangiji, Allahn kakanninku, yake ba ku don ku ci gādonta, muddin kuna zama a ƙasar.
Estas son las leyes y las decisiones que deben tomar con cuidado en la tierra que el Señor, el Dios de sus padres, les ha dado para que sea su herencia todos los días de su vida en la tierra.
2 Ku hallaka dukan wuraren da al’umman da kuke kora suke yi wa allolinsu sujada, a kan duwatsu masu tsawo, da a kan tuddai, da kuma ƙarƙashin kowane itace gaba ɗaya.
Destruirán por completo en todos aquellos lugares donde las naciones, a quienes ustedes van expulsar, adoran a sus dioses, en las montañas altas y las colinas y debajo de cada árbol frondoso:
3 Ku rurrushe bagadansu, ku farfashe keɓaɓɓun duwatsunsu, ku kuma ƙone ginshiƙan Asheransu da wuta; ku yayyanka gumakan allolinsu, ku kuma shafe sunayensu daga waɗannan wurare.
Sus altares y sus pilares serán derribados, y sus árboles sagrados serán quemados con fuego, y las imágenes de sus dioses serán derribadas; Deben borrar sus nombres de ese lugar.
4 Ba za ku yi wa Ubangiji Allahnku sujada a hanyar da suke yi ba.
No deben adorar al Señor su Dios de esta manera.
5 Amma sai ku nemi wurin da Ubangiji Allahnku zai zaɓa daga cikin dukan kabilanku, inda zai sa Sunansa, yă mai wurin mazauninsa. A wannan wuri ne za ku tafi;
Pero vuelvan sus corazones al lugar que será escogido por el Señor su Dios, entre sus tribus, para poner su nombre allí y ustedes podrán ir adorarlo;
6 a can ne kuma za ku kawo hadayun ƙonawa da sadakoki, zakkarku da kyautai na musamman, da abin da kuka yi alkawari za ku bayar, da hadayunku na yardar rai, da kuma’ya’yan farin garkunanku na shanu da na tumaki.
Y allí tienes que llevar sus ofrendas quemadas y otras ofrendas, y la décima parte de sus bienes, y las ofrendas para ser levantadas al Señor, y las ofrendas de sus juramentos, y las que ofreces libremente por el impulso de sus corazones y los primeros nacimientos entre sus vacas y sus ovejas;
7 A can, a gaban Ubangiji Allahnku, ku da iyalanku za su ci, su kuma yi farin ciki a kome da kuka sa hannunku a kai, domin Ubangiji Allahnku zai albarkace ku.
Allí, ustedes y todas sus familias deben hacer una fiesta delante del Señor su Dios, con gozo en todo lo que pones, porque el Señor les ha dado su bendición.
8 Kada ku yi kamar yadda muke yi a nan yau, yadda kowa yake yin abin da ya ga dama.
No deben hacer las cosas de la manera en que ahora las hacemos aquí, cada hombre como le parezca correcto:
9 Gama ba ku kai wurin hutawa wanda Ubangiji Allahnku zai ba ku gādo ba tukuna.
Porque no han venido al descanso ni a la herencia que el Señor su Dios les está dando.
10 Amma sa’ad da kuka haye Urdun, kuka zauna a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku ita gādo, zai kuwa ba ku hutu daga dukan abokan gābanku da suke kewaye da ku, kuka sami zaman lafiya,
Pero cuando hayan cruzado el Jordán y estén viviendo en la tierra que el Señor su Dios les está dando como su herencia, y cuando los haya librado de todos los que luchan contra ustedes, y ustedes estén viviendo allí a salvo;
11 sai ku kai dukan abin da na umarce ku ku kai, wato, hadayu na ƙonawa, da sadakokinku, da zakkarku, da hadayunku na ɗagawa, da hadayunku na alkawarin da kuka yi wa Ubangiji a wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa yă sa sunansa.
Entonces habrá un lugar escogido por el Señor su Dios como lugar de descanso para su nombre, y allí ofrecerán todas las cosas que les he ordenado: sus ofrendas quemadas y sacrificios, y la décima parte de sus bienes, y las ofrendas para ser levantadas, y las ofrendas de sus juramentos que hacen al Señor;
12 A can kuma za ku yi farin ciki a gaban Ubangiji Allahnku, ku da’ya’yanku maza da mata, da bayinku maza da mata, da kuma Lawiyawa daga biranenku, waɗanda ba a ba su rabo ba, ba su kuma da gādo na kansu.
Y te alegrarás delante del Señor su Dios, ustedes y sus hijos y sus hijas, y sus siervos y sus siervas, y el levita que está entre ustedes en su casa, porque no tiene parte ni herencia entre ustedes.
13 Ku kula fa kada ku miƙa hadayun ƙonawa a wani wurin da kuka ga dama.
Tengan cuidado de no hacer sus ofrendas quemadas en cualquier lugar que vean:
14 Ku miƙa su kawai a wurin da Ubangiji zai zaɓa a cikin ɗaya daga kabilanku, a can za ku yi kowane abin da na umarce ku.
Pero en el lugar señalado por el Señor en una de tus tribus, que se ofrezcan sus ofrendas quemadas, y haz lo que te he ordenado que hagas.
15 Amma kwa iya yanka nama ku ci a garuruwanku, a duk lokacin da ranku yake so, kamar yadda ake yi da gada ko barewa, bisa ga albarkar da Ubangiji Allahnku yake sa muku. Marar tsarki da mai tsarki, duka za ku iya ci.
Solo pueden matar animales, como la gacela y él ciervo, para tu alimento en cualquiera de tus pueblos, según el deseo de tu alma, de acuerdo con la bendición del Señor tu Dios que él les ha dado. Él impuro y él limpio lo comerá.
16 Amma kada ku ci jini, ku zubar da shi a ƙasa kamar ruwa.
Pero no pueden tomar la sangre como alimento, se debe drenar en la tierra como el agua.
17 Kada ku ci zakkar hatsi, da na sabon inabi, da kuma na mai a biranenku, ko kuwa na’ya’yan fari na garkunanku na shanu da na tumaki, ko kuwa duk wani abin da kuka yi alkawari za ku bayar, ko hadayunku na yardar rai, ko kyautai na musamman.
En tus ciudades no debes tomar como alimento la décima parte de tu grano, o de tu vino o tu aceite, o los primeros nacimientos de tu ganado o de tus rebaños, o cualquier cosa ofrecida bajo un juramento, o libremente ofrecido al Señor, o dado como ofrenda mecida;
18 A maimakon haka, sai ku ci su a gaban Ubangiji Allahnku a wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa, da ku da’ya’yanku maza da mata, da bayinku maza da mata, da kuma Lawiyawa daga biranenku, ku kuwa yi farin ciki a gaban Ubangiji Allahnku a kowane abin da kuka sa hannunku.
Pero comerán su alimento delante del Señor tu Dios en el lugar de su elección, donde podrán alegrarse delante de él, con su hijo y su hija, y su sirviente y su sierva, y el levita quien vive entre ustedes: y tendrán gozo delante del Señor su Dios por todo lo que pone en su mano.
19 Ku yi hankali, kada ku manta da Lawiyawa, muddin kuna zaune a ƙasarku.
Asegúrense de no dejar de cuidar al levita mientras vivas en tu tierra.
20 Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya fadada iyakarku kamar yadda ya yi muku alkawari, kuka kuma ji marmarin nama, kuka kuma ce, “Muna so mu ci nama,” to, za ku iya cin yadda kuke so.
Cuando el Señor tu Dios amplíe el límite de tu tierra, como él ha dicho, y ustedes digan: Tomaré carne por mi comida, porque la deseo; entonces pueden comer cualquier carne que deseen.
21 In wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa don yă sa Sunansa yana da nisa sosai daga inda kuke, za ku iya yankan dabbobi daga garkunanku na shanu da na tumakin da Ubangiji ya ba ku, kamar yadda na umarce ku, a cikin biranenku kuma za ku iya ci, yadda kuke so.
Si el lugar señalado por el Señor tu Dios como lugar de descanso para su nombre está lejos de ustedes, entonces podrás matar de tu ganado y de tus rebaños que el Señor les ha dado, como he dicho, y Coman en los pueblos donde están viviendo todo lo que desee su corazón.
22 Ku ci su yadda akan ci barewa ko mariri. Marar tsarki da mai tsarki, za ku iya ci.
Será tu comida, como la gacela y el ciervo; él impuro y limpio podrán comer de ello.
23 Amma ku tabbata ba ku ci jinin ba, domin jini ne rai, ba kuwa za ku ci rai cikin naman ba.
Pero mira que no tomes la sangre para comer; porque la sangre es la vida; y no podrás hacer uso de la vida como alimento con la carne.
24 Ba za ku ci jini ba, ku zubar da shi a ƙasa kamar ruwa.
No la comerás como alimento, sino que lo derramarás en la tierra como el agua.
25 Kada ku ci shi, don ku zauna lafiya, da ku da’ya’yanku bayanku, gama za ku riƙa aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji.
No la tomes por comida; para que les vaya bien a ti y a tus hijos después de ustedes, mientras hacen lo correcto ante los ojos del Señor.
26 Amma ku ɗauki abubuwa masu tsarki, da kuma duk abin da kuka yi alkawari za ku bayar, ku tafi inda Ubangiji ya zaɓa.
Pero las cosas santas que tienes, y las ofrendas de tus juramentos, deben llevarlas al lugar que será escogido por el Señor:
27 Ku miƙa hadayunku na ƙonawa a bagaden Ubangiji Allahnku, da naman da kuma jinin. Dole a zub da jinin hadayunku a gindin bagaden Ubangiji Allahnku, amma za ku iya cin naman.
Ofrecerán la carne y la sangre de tus holocaustos sobre el altar del Señor tu Dios; y la sangre de sus ofrendas será derramada sobre el altar del Señor tu Dios, y podrás comer la carne.
28 Ku yi hankali, ku yi biyayya da dukan waɗannan umarnan da nake ba ku, da kuma’ya’yanku, don ku zauna lafiya, da ku da’ya’yanku a bayanku, gama za ku riƙa aikata abin da yake daidai da kuma yake mai kyau a gaban Ubangiji Allahnku.
Toma nota de todas estas órdenes que te estoy dando y presten atención a ellas, para que te vaya bien a ti y a tus hijos después de ustedes, mientras hacen lo que es bueno y correcto a los ojos del Señor su Dios.
29 Ubangiji Allahnku zai kawar muku da al’umman nan da kuke niyyar shiga cikin ƙasarsu don ku kore su, bayan kuka kore su, kuka kuma zauna a ƙasarsu,
Cuando el pueblo de la tierra a la que se dirigen haya sido destruida por el Señor tu Dios, y hayan tomado su tierra y estén viviendo en ella;
30 to, sai ku lura, kada ku jarrabtu ku kwaikwaye su bayan da an riga an shafe su daga gabanku, kada ku tambayi kome game da allolinsu, kuna cewa, “Yaya waɗannan al’ummai suke bauta wa allolinsu? Mu ma za mu yi kamar yadda suka yi.”
Después de su destrucción, cuídate de no seguir sus caminos y de no pensar en sus dioses, diciendo: Cómo adoraron estas naciones a sus dioses Haré lo que ellos hicieron.
31 Ba za ku yi wa Ubangiji Allahnku sujada a hanyar da suke yi ba, gama a cikin yin sujada wa allolinsu, sun yi dukan abubuwan banƙyaman da Ubangiji yake ƙi. Har ma sukan ƙone’ya’yansu maza da mata a wuta a matsayin hadayu.
No hagan esto al Señor tu Dios: porque todo lo que es repugnante para el Señor y odiado por él, lo han hecho en honor de sus dioses: incluso quemando a sus hijos e hijas en el fuego a sus dioses.
32 Ku lura, ku aikata dukan abin da na umarce ku; kada ku ƙara, kada ku rage daga cikin.
Deben guardar con cuidado todas las palabras que les doy, sin agregar nada y sin quitarle nada.

< Maimaitawar Shari’a 12 >