< Maimaitawar Shari’a 12 >

1 Waɗannan su ne ƙa’idodi da kuma dokokin da za ku lura, ku kuma kiyaye a ƙasar da Ubangiji, Allahn kakanninku, yake ba ku don ku ci gādonta, muddin kuna zama a ƙasar.
Estes são os estatutos e as ordenanças que você deve observar para fazer na terra que Iavé, o Deus de seus pais, lhe deu para possuir todos os dias que você vive na terra.
2 Ku hallaka dukan wuraren da al’umman da kuke kora suke yi wa allolinsu sujada, a kan duwatsu masu tsawo, da a kan tuddai, da kuma ƙarƙashin kowane itace gaba ɗaya.
Certamente destruireis todos os lugares em que as nações que despojardes serviram seus deuses: nas altas montanhas, nas colinas, e debaixo de toda árvore verde.
3 Ku rurrushe bagadansu, ku farfashe keɓaɓɓun duwatsunsu, ku kuma ƙone ginshiƙan Asheransu da wuta; ku yayyanka gumakan allolinsu, ku kuma shafe sunayensu daga waɗannan wurare.
Derrubarás seus altares, despedaçarás seus pilares e queimarás seus bastões de Cinzas com fogo. Cortareis as imagens gravadas de seus deuses. Destruireis o nome deles daquele lugar.
4 Ba za ku yi wa Ubangiji Allahnku sujada a hanyar da suke yi ba.
Não o farás a Javé, teu Deus.
5 Amma sai ku nemi wurin da Ubangiji Allahnku zai zaɓa daga cikin dukan kabilanku, inda zai sa Sunansa, yă mai wurin mazauninsa. A wannan wuri ne za ku tafi;
Mas para o lugar que Javé, vosso Deus, escolherá dentre todas as vossas tribos, para ali colocar seu nome, procurareis sua morada, e ali vireis.
6 a can ne kuma za ku kawo hadayun ƙonawa da sadakoki, zakkarku da kyautai na musamman, da abin da kuka yi alkawari za ku bayar, da hadayunku na yardar rai, da kuma’ya’yan farin garkunanku na shanu da na tumaki.
Levareis vossas ofertas queimadas, vossos sacrifícios, vossos dízimos, a oferta de mão, vossos votos, vossas ofertas de livre vontade, e o primogênito de vosso rebanho e de vosso rebanho ali.
7 A can, a gaban Ubangiji Allahnku, ku da iyalanku za su ci, su kuma yi farin ciki a kome da kuka sa hannunku a kai, domin Ubangiji Allahnku zai albarkace ku.
Ali comereis perante Javé vosso Deus, e vos alegrareis com tudo a que puserdes vossa mão, vós e vossas famílias, nas quais Javé vosso Deus vos abençoou.
8 Kada ku yi kamar yadda muke yi a nan yau, yadda kowa yake yin abin da ya ga dama.
Você não fará todas as coisas que fazemos aqui hoje, cada homem o que quer que seja certo aos seus próprios olhos;
9 Gama ba ku kai wurin hutawa wanda Ubangiji Allahnku zai ba ku gādo ba tukuna.
pois você ainda não chegou ao resto e à herança que Yahweh seu Deus lhe dá.
10 Amma sa’ad da kuka haye Urdun, kuka zauna a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku ita gādo, zai kuwa ba ku hutu daga dukan abokan gābanku da suke kewaye da ku, kuka sami zaman lafiya,
Mas quando atravessares o Jordão e habitares a terra que Javé teu Deus te faz herdar, e ele te der descanso de todos os teus inimigos ao teu redor, para que habites em segurança,
11 sai ku kai dukan abin da na umarce ku ku kai, wato, hadayu na ƙonawa, da sadakokinku, da zakkarku, da hadayunku na ɗagawa, da hadayunku na alkawarin da kuka yi wa Ubangiji a wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa yă sa sunansa.
então acontecerá que ao lugar que Javé teu Deus escolher, para fazer habitar ali o seu nome, ali trarás tudo o que eu te ordeno: tuas ofertas queimadas, teus sacrifícios, teus dízimos, a oferta da tua mão, e todos os teus votos de escolha que fizeres a Javé.
12 A can kuma za ku yi farin ciki a gaban Ubangiji Allahnku, ku da’ya’yanku maza da mata, da bayinku maza da mata, da kuma Lawiyawa daga biranenku, waɗanda ba a ba su rabo ba, ba su kuma da gādo na kansu.
Alegrar-vos-eis perante Iavé vosso Deus - vós e vossos filhos, vossas filhas, vossos servos, vossas servas, vossas servas e o levita que está dentro de vossos portões, porque ele não tem parte nem herança convosco.
13 Ku kula fa kada ku miƙa hadayun ƙonawa a wani wurin da kuka ga dama.
Tenha cuidado para não oferecer suas ofertas queimadas em todos os lugares que você vê;
14 Ku miƙa su kawai a wurin da Ubangiji zai zaɓa a cikin ɗaya daga kabilanku, a can za ku yi kowane abin da na umarce ku.
mas no lugar que Javé escolher em uma de suas tribos, lá você oferecerá suas ofertas queimadas, e lá você fará tudo o que eu lhe ordenar.
15 Amma kwa iya yanka nama ku ci a garuruwanku, a duk lokacin da ranku yake so, kamar yadda ake yi da gada ko barewa, bisa ga albarkar da Ubangiji Allahnku yake sa muku. Marar tsarki da mai tsarki, duka za ku iya ci.
No entanto, você pode matar e comer carne dentro de todos os seus portões, depois de todo o desejo de sua alma, de acordo com Yahweh, a bênção de seu Deus que Ele lhe deu. O impuro e o limpo podem comer dela, como da gazela e do cervo.
16 Amma kada ku ci jini, ku zubar da shi a ƙasa kamar ruwa.
Somente vós não comereis o sangue. Derramá-lo-ás sobre a terra como água.
17 Kada ku ci zakkar hatsi, da na sabon inabi, da kuma na mai a biranenku, ko kuwa na’ya’yan fari na garkunanku na shanu da na tumaki, ko kuwa duk wani abin da kuka yi alkawari za ku bayar, ko hadayunku na yardar rai, ko kyautai na musamman.
Não poderás comer dentro de tuas portas o dízimo de teu grão, ou de teu vinho novo, ou de teu óleo, ou o primogênito de teu rebanho ou de teu rebanho, nem qualquer de teus votos que fizeres, nem tuas ofertas de livre vontade, nem a oferta de onda de tua mão;
18 A maimakon haka, sai ku ci su a gaban Ubangiji Allahnku a wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa, da ku da’ya’yanku maza da mata, da bayinku maza da mata, da kuma Lawiyawa daga biranenku, ku kuwa yi farin ciki a gaban Ubangiji Allahnku a kowane abin da kuka sa hannunku.
mas as comerás diante de Javé teu Deus no lugar que Javé teu Deus escolher: tu, teu filho, tua filha, teu servo macho, tua serva fêmea e o levita que está dentro de tuas portas. Você se alegrará diante de Javé, seu Deus, em tudo a que puser sua mão.
19 Ku yi hankali, kada ku manta da Lawiyawa, muddin kuna zaune a ƙasarku.
Tenha cuidado para não abandonar o Levita enquanto viver em sua terra.
20 Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya fadada iyakarku kamar yadda ya yi muku alkawari, kuka kuma ji marmarin nama, kuka kuma ce, “Muna so mu ci nama,” to, za ku iya cin yadda kuke so.
Quando Yahweh seu Deus amplia sua fronteira, como Ele lhe prometeu, e você diz: “Eu quero comer carne”, porque sua alma deseja comer carne, você pode comer carne, depois de todo o desejo de sua alma.
21 In wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa don yă sa Sunansa yana da nisa sosai daga inda kuke, za ku iya yankan dabbobi daga garkunanku na shanu da na tumakin da Ubangiji ya ba ku, kamar yadda na umarce ku, a cikin biranenku kuma za ku iya ci, yadda kuke so.
Se o lugar que Javé seu Deus escolher para colocar seu nome estiver muito longe de você, então você matará de seu rebanho e de seu rebanho, que Javé lhe deu, como eu lhe ordenei; e você poderá comer dentro de seus portões, depois de todo o desejo de sua alma.
22 Ku ci su yadda akan ci barewa ko mariri. Marar tsarki da mai tsarki, za ku iya ci.
Mesmo como a gazela e como o cervo é comido, assim comereis dele. O imundo e o limpo podem comer dela da mesma forma.
23 Amma ku tabbata ba ku ci jinin ba, domin jini ne rai, ba kuwa za ku ci rai cikin naman ba.
Tenha certeza apenas de que você não come o sangue; pois o sangue é a vida. Você não deve comer a vida com a carne.
24 Ba za ku ci jini ba, ku zubar da shi a ƙasa kamar ruwa.
Você não comerá dela. Você o derramará sobre a terra como água.
25 Kada ku ci shi, don ku zauna lafiya, da ku da’ya’yanku bayanku, gama za ku riƙa aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji.
Não o comerá, para que ele possa ir bem com você e com seus filhos depois de você, quando fizer o que é certo aos olhos de Javé.
26 Amma ku ɗauki abubuwa masu tsarki, da kuma duk abin da kuka yi alkawari za ku bayar, ku tafi inda Ubangiji ya zaɓa.
Somente suas coisas sagradas que você tem, e seus votos, você tomará e irá para o lugar que Yahweh escolher.
27 Ku miƙa hadayunku na ƙonawa a bagaden Ubangiji Allahnku, da naman da kuma jinin. Dole a zub da jinin hadayunku a gindin bagaden Ubangiji Allahnku, amma za ku iya cin naman.
Vocês oferecerão seus holocaustos, a carne e o sangue, no altar de Yahweh, vosso Deus. O sangue de seus sacrifícios será derramado sobre o altar de Yahweh seu Deus, e você comerá a carne.
28 Ku yi hankali, ku yi biyayya da dukan waɗannan umarnan da nake ba ku, da kuma’ya’yanku, don ku zauna lafiya, da ku da’ya’yanku a bayanku, gama za ku riƙa aikata abin da yake daidai da kuma yake mai kyau a gaban Ubangiji Allahnku.
Observe e ouça todas estas palavras que eu lhe ordeno, para que possa ir bem com você e com seus filhos depois de você para sempre, quando você fizer o que é bom e correto aos olhos de Iavé seu Deus.
29 Ubangiji Allahnku zai kawar muku da al’umman nan da kuke niyyar shiga cikin ƙasarsu don ku kore su, bayan kuka kore su, kuka kuma zauna a ƙasarsu,
Quando Yahweh seu Deus cortar as nações de antes de você onde você entra para desapropriá-las, e você as desapropriar e habitar em suas terras,
30 to, sai ku lura, kada ku jarrabtu ku kwaikwaye su bayan da an riga an shafe su daga gabanku, kada ku tambayi kome game da allolinsu, kuna cewa, “Yaya waɗannan al’ummai suke bauta wa allolinsu? Mu ma za mu yi kamar yadda suka yi.”
tenha cuidado para não ser ludibriado a segui-las depois de serem destruídas de antes de você, e para não perguntar depois de seus deuses, dizendo: “Como estas nações servem a seus deuses? Eu farei o mesmo”.
31 Ba za ku yi wa Ubangiji Allahnku sujada a hanyar da suke yi ba, gama a cikin yin sujada wa allolinsu, sun yi dukan abubuwan banƙyaman da Ubangiji yake ƙi. Har ma sukan ƙone’ya’yansu maza da mata a wuta a matsayin hadayu.
Não o farás a Javé teu Deus; por toda abominação a Javé, que ele odeia, eles fizeram aos seus deuses; pois até queimam seus filhos e suas filhas no fogo aos seus deuses.
32 Ku lura, ku aikata dukan abin da na umarce ku; kada ku ƙara, kada ku rage daga cikin.
Whatever coisa que eu vos ordeno, que observem para fazer. Não lhe acrescentarás, nem lhe tirarás nada.

< Maimaitawar Shari’a 12 >