< Maimaitawar Shari’a 12 >

1 Waɗannan su ne ƙa’idodi da kuma dokokin da za ku lura, ku kuma kiyaye a ƙasar da Ubangiji, Allahn kakanninku, yake ba ku don ku ci gādonta, muddin kuna zama a ƙasar.
اینهاست فرایض و احکامی که شما درتمامی روزهایی که بر زمین زنده خواهید ماند، می‌باید متوجه شده، به عمل آرید، در زمینی که یهوه خدای پدرانت به تو داده است، تا در آن تصرف نمایی.۱
2 Ku hallaka dukan wuraren da al’umman da kuke kora suke yi wa allolinsu sujada, a kan duwatsu masu tsawo, da a kan tuddai, da kuma ƙarƙashin kowane itace gaba ɗaya.
جمیع اماکن امتهایی را که در آنها خدایان خود را عبادت می‌کنند و شما آنها را اخراج می‌نمایید خراب نمایید، خواه بر کوههای بلندخواه بر تلها و خواه زیر هر درخت سبز.۲
3 Ku rurrushe bagadansu, ku farfashe keɓaɓɓun duwatsunsu, ku kuma ƙone ginshiƙan Asheransu da wuta; ku yayyanka gumakan allolinsu, ku kuma shafe sunayensu daga waɗannan wurare.
مذبحهای ایشان را بشکنید و ستونهای ایشان راخرد کنید، و اشیره های ایشان را به آتش بسوزانید، و بتهای تراشیده شده خدایان ایشان راقطع نمایید، و نامهای ایشان را از آنجا محوسازید.۳
4 Ba za ku yi wa Ubangiji Allahnku sujada a hanyar da suke yi ba.
با یهوه خدای خود چنین عمل منمایید.۴
5 Amma sai ku nemi wurin da Ubangiji Allahnku zai zaɓa daga cikin dukan kabilanku, inda zai sa Sunansa, yă mai wurin mazauninsa. A wannan wuri ne za ku tafi;
بلکه به مکانی که یهوه خدای شما از جمیع اسباط شما برگزیند تا نام خود را در آنجا بگذارد، یعنی مسکن او را بطلبید و به آنجا بروید.۵
6 a can ne kuma za ku kawo hadayun ƙonawa da sadakoki, zakkarku da kyautai na musamman, da abin da kuka yi alkawari za ku bayar, da hadayunku na yardar rai, da kuma’ya’yan farin garkunanku na shanu da na tumaki.
و به آنجا قربانی های سوختنی و ذبایح و عشرهای خود، و هدایای افراشتنی دستهای خویش، ونذرها و نوافل خود و نخست زاده های رمه و گله خویش را ببرید.۶
7 A can, a gaban Ubangiji Allahnku, ku da iyalanku za su ci, su kuma yi farin ciki a kome da kuka sa hannunku a kai, domin Ubangiji Allahnku zai albarkace ku.
و در آنجا بحضور یهوه خدای خود بخورید، و شما و اهل خانه شما در هر شغل دست خود که یهوه خدای شما، شما را در آن برکت دهد، شادی نمایید.۷
8 Kada ku yi kamar yadda muke yi a nan yau, yadda kowa yake yin abin da ya ga dama.
موافق هرآنچه ما امروز در اینجا می‌کنیم، یعنی آنچه در نظر هرکس پسند آید، نکنید.۸
9 Gama ba ku kai wurin hutawa wanda Ubangiji Allahnku zai ba ku gādo ba tukuna.
زیرا که هنوز به آرامگاه و نصیبی که یهوه خدای شما، به شما می‌دهد داخل نشده‌اید.۹
10 Amma sa’ad da kuka haye Urdun, kuka zauna a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku ita gādo, zai kuwa ba ku hutu daga dukan abokan gābanku da suke kewaye da ku, kuka sami zaman lafiya,
اما چون از اردن عبور کرده، در زمینی که یهوه، خدای شما، برای شما تقسیم می‌کند، ساکن شوید، و اوشما را از جمیع دشمنان شما از هرطرف آرامی دهد تا در امنیت سکونت نمایید.۱۰
11 sai ku kai dukan abin da na umarce ku ku kai, wato, hadayu na ƙonawa, da sadakokinku, da zakkarku, da hadayunku na ɗagawa, da hadayunku na alkawarin da kuka yi wa Ubangiji a wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa yă sa sunansa.
آنگاه به مکانی که یهوه خدای شما برگزیند تا نام خود رادر آن ساکن سازد، به آنجا هرچه را که من به شماامر فرمایم بیاورید، از قربانی های سوختنی وذبایح و عشرهای خود، و هدایای افراشتنی دستهای خویش، و همه نذرهای بهترین خود که برای خداوند نذر نمایید.۱۱
12 A can kuma za ku yi farin ciki a gaban Ubangiji Allahnku, ku da’ya’yanku maza da mata, da bayinku maza da mata, da kuma Lawiyawa daga biranenku, waɗanda ba a ba su rabo ba, ba su kuma da gādo na kansu.
و به حضور یهوه خدای خود شادی نمایید، شما با پسران ودختران و غلامان و کنیزان خود، و لاویانی که درون دروازه های شما باشند، چونکه ایشان را باشما حصه‌ای و نصیبی نیست.۱۲
13 Ku kula fa kada ku miƙa hadayun ƙonawa a wani wurin da kuka ga dama.
با حذر باش که در هر جایی که می‌بینی قربانی های سوختنی خود را نگذرانی،۱۳
14 Ku miƙa su kawai a wurin da Ubangiji zai zaɓa a cikin ɗaya daga kabilanku, a can za ku yi kowane abin da na umarce ku.
بلکه درمکانی که خداوند در یکی از اسباط تو برگزیند درآنجا قربانی های سوختنی خود را بگذرانی، و درآنجا هرچه من به تو امر فرمایم، به عمل آوری.۱۴
15 Amma kwa iya yanka nama ku ci a garuruwanku, a duk lokacin da ranku yake so, kamar yadda ake yi da gada ko barewa, bisa ga albarkar da Ubangiji Allahnku yake sa muku. Marar tsarki da mai tsarki, duka za ku iya ci.
لیکن گوشت را برحسب تمامی آرزوی دلت، موافق برکتی که یهوه خدایت به تو دهد، درهمه دروازه هایت ذبح کرده، بخور؛ اشخاص نجس و طاهر از آن بخورند چنانکه از غزال و آهومی خورند.۱۵
16 Amma kada ku ci jini, ku zubar da shi a ƙasa kamar ruwa.
ولی خون را نخور؛ آن را مثل آب بر زمین بریز.۱۶
17 Kada ku ci zakkar hatsi, da na sabon inabi, da kuma na mai a biranenku, ko kuwa na’ya’yan fari na garkunanku na shanu da na tumaki, ko kuwa duk wani abin da kuka yi alkawari za ku bayar, ko hadayunku na yardar rai, ko kyautai na musamman.
عشر غله و شیره و روغن ونخست زاده رمه و گله خود را در دروازه های خودمخور، و نه هیچ‌یک از نذرهای خود را که نذرمی کنی و از نوافل خود و هدایای افراشتنی دست خود را.۱۷
18 A maimakon haka, sai ku ci su a gaban Ubangiji Allahnku a wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa, da ku da’ya’yanku maza da mata, da bayinku maza da mata, da kuma Lawiyawa daga biranenku, ku kuwa yi farin ciki a gaban Ubangiji Allahnku a kowane abin da kuka sa hannunku.
بلکه آنها را به حضور یهوه خدایت درمکانی که یهوه خدایت برگزیند، بخور، تو وپسرت و دخترت و غلامت و کنیزت و لاویانی که درون دروازه های تو باشند، و به هرچه دست خود را برآن بگذاری به حضور یهوه خدایت شادی نما.۱۸
19 Ku yi hankali, kada ku manta da Lawiyawa, muddin kuna zaune a ƙasarku.
با حذر باش که لاویان را در تمامی روزهایی که در زمین خود باشی، ترک ننمایی.۱۹
20 Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya fadada iyakarku kamar yadda ya yi muku alkawari, kuka kuma ji marmarin nama, kuka kuma ce, “Muna so mu ci nama,” to, za ku iya cin yadda kuke so.
چون یهوه، خدایت، حدود تو را بطوری که تو را وعده داده است، وسیع گرداند، و بگویی که گوشت خواهم خورد، زیرا که دل تو به گوشت خوردن مایل است، پس موافق همه آرزوی دلت گوشت را بخور.۲۰
21 In wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa don yă sa Sunansa yana da nisa sosai daga inda kuke, za ku iya yankan dabbobi daga garkunanku na shanu da na tumakin da Ubangiji ya ba ku, kamar yadda na umarce ku, a cikin biranenku kuma za ku iya ci, yadda kuke so.
و اگر مکانی که یهوه، خدایت، برگزیند تا اسم خود را در آن بگذارد ازتو دور باشد، آنگاه از رمه و گله خود که خداوندبه تو دهد ذبح کن، چنانکه به تو امر فرموده‌ام و ازهرچه دلت بخواهد در دروازه هایت بخور.۲۱
22 Ku ci su yadda akan ci barewa ko mariri. Marar tsarki da mai tsarki, za ku iya ci.
چنانکه غزال و آهو خورده شود، آنها را چنین بخور؛ شخص نجس و شخص طاهر از آن برابربخورند.۲۲
23 Amma ku tabbata ba ku ci jinin ba, domin jini ne rai, ba kuwa za ku ci rai cikin naman ba.
لیکن هوشیار باش که خون را نخوری زیرا خون جان است و جان را با گوشت نخوری.۲۳
24 Ba za ku ci jini ba, ku zubar da shi a ƙasa kamar ruwa.
آن را مخور، بلکه مثل آب برزمینش بریز.۲۴
25 Kada ku ci shi, don ku zauna lafiya, da ku da’ya’yanku bayanku, gama za ku riƙa aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji.
آن را مخور تا برای تو و بعد از تو برای پسرانت نیکو باشد هنگامی که آنچه در نظرخداوند راست است، بجا آوری.۲۵
26 Amma ku ɗauki abubuwa masu tsarki, da kuma duk abin da kuka yi alkawari za ku bayar, ku tafi inda Ubangiji ya zaɓa.
لیکن موقوفات خود را که داری و نذرهای خود رابرداشته، به مکانی که خداوند برگزیند، برو.۲۶
27 Ku miƙa hadayunku na ƙonawa a bagaden Ubangiji Allahnku, da naman da kuma jinin. Dole a zub da jinin hadayunku a gindin bagaden Ubangiji Allahnku, amma za ku iya cin naman.
وگوشت و خون قربانی های سوختنی خود را برمذبح یهوه خدایت بگذران و خون ذبایح توبرمذبح یهوه خدایت ریخته شود و گوشت رابخور.۲۷
28 Ku yi hankali, ku yi biyayya da dukan waɗannan umarnan da nake ba ku, da kuma’ya’yanku, don ku zauna lafiya, da ku da’ya’yanku a bayanku, gama za ku riƙa aikata abin da yake daidai da kuma yake mai kyau a gaban Ubangiji Allahnku.
متوجه باش که همه این سخنانی را که من به تو امر می‌فرمایم بشنوی تا برای تو و بعد از توبرای پسرانت هنگامی که آنچه در نظر یهوه، خدایت، نیکو و راست است بجا آوری تا به ابدنیکو باشد.۲۸
29 Ubangiji Allahnku zai kawar muku da al’umman nan da kuke niyyar shiga cikin ƙasarsu don ku kore su, bayan kuka kore su, kuka kuma zauna a ƙasarsu,
وقتی که یهوه، خدایت، امتهایی را که به جهت گرفتن آنها به آنجا می‌روی، از حضور تومنقطع سازد، و ایشان را اخراج نموده، در زمین ایشان ساکن شوی.۲۹
30 to, sai ku lura, kada ku jarrabtu ku kwaikwaye su bayan da an riga an shafe su daga gabanku, kada ku tambayi kome game da allolinsu, kuna cewa, “Yaya waɗannan al’ummai suke bauta wa allolinsu? Mu ma za mu yi kamar yadda suka yi.”
آنگاه باحذر باش، مبادا بعداز آنکه از حضور تو هلاک شده باشند به دام گرفته شده، ایشان را پیروی نمایی و درباره خدایان ایشان دریافت کرده، بگویی که این امتها خدایان خود را چگونه عبادت کردند تا من نیز چنین کنم.۳۰
31 Ba za ku yi wa Ubangiji Allahnku sujada a hanyar da suke yi ba, gama a cikin yin sujada wa allolinsu, sun yi dukan abubuwan banƙyaman da Ubangiji yake ƙi. Har ma sukan ƙone’ya’yansu maza da mata a wuta a matsayin hadayu.
با یهوه، خدای خود، چنین عمل منما، زیراهرچه را که نزد خداوند مکروه است و از آن نفرت دارد، ایشان برای خدایان خود می‌کردند، حتی اینکه پسران و دختران خود را نیز برای خدایان خود به آتش می‌سوزانیدند.۳۱
32 Ku lura, ku aikata dukan abin da na umarce ku; kada ku ƙara, kada ku rage daga cikin.
هر‌آنچه من به شما امر می‌فرمایم متوجه شوید، تا آن را به عمل آورید، چیزی برآن میفزایید و چیزی از آن کم نکنید.۳۲

< Maimaitawar Shari’a 12 >