< Maimaitawar Shari’a 12 >
1 Waɗannan su ne ƙa’idodi da kuma dokokin da za ku lura, ku kuma kiyaye a ƙasar da Ubangiji, Allahn kakanninku, yake ba ku don ku ci gādonta, muddin kuna zama a ƙasar.
Voici les statuts et les rites que vous garderez pour les pratiquer dans le pays que t'a donné pour en faire la conquête l'Éternel, Dieu de tes pères, aussi longtemps que vous vivrez sur la terre.
2 Ku hallaka dukan wuraren da al’umman da kuke kora suke yi wa allolinsu sujada, a kan duwatsu masu tsawo, da a kan tuddai, da kuma ƙarƙashin kowane itace gaba ɗaya.
Vous détruirez tous les lieux où les nations que vous allez chasser, rendaient un culte à leurs dieux sur les montagnes élevées, et sur les collines et sous tous les arbres verdoyants;
3 Ku rurrushe bagadansu, ku farfashe keɓaɓɓun duwatsunsu, ku kuma ƙone ginshiƙan Asheransu da wuta; ku yayyanka gumakan allolinsu, ku kuma shafe sunayensu daga waɗannan wurare.
et vous mettrez leurs autels en ruine, et briserez leurs colonnes et brûlerez au feu leurs Aschères, et mettrez en pièces les effigies de leurs dieux, et effacerez leurs noms de ces lieux-là.
4 Ba za ku yi wa Ubangiji Allahnku sujada a hanyar da suke yi ba.
Ce n'est pas de la sorte que vous en agirez avec l'Éternel, votre Dieu;
5 Amma sai ku nemi wurin da Ubangiji Allahnku zai zaɓa daga cikin dukan kabilanku, inda zai sa Sunansa, yă mai wurin mazauninsa. A wannan wuri ne za ku tafi;
mais vous chercherez le lieu que choisira l'Éternel, votre Dieu, dans toutes vos Tribus pour y fixer son nom et y résider, et il sera votre Rendez-vous:
6 a can ne kuma za ku kawo hadayun ƙonawa da sadakoki, zakkarku da kyautai na musamman, da abin da kuka yi alkawari za ku bayar, da hadayunku na yardar rai, da kuma’ya’yan farin garkunanku na shanu da na tumaki.
et là vous amènerez vos holocaustes et vos victimes et vos dîmes et les élévations de vos mains et vos oblations votives et volontaires et les premiers-nés de votre gros et de votre menu bétail;
7 A can, a gaban Ubangiji Allahnku, ku da iyalanku za su ci, su kuma yi farin ciki a kome da kuka sa hannunku a kai, domin Ubangiji Allahnku zai albarkace ku.
et là vous ferez vos banquets devant l'Éternel, votre Dieu, vous réjouissant de tout le travail de vos mains, vous et les familles dont t'aura béni l'Éternel, ton Dieu.
8 Kada ku yi kamar yadda muke yi a nan yau, yadda kowa yake yin abin da ya ga dama.
Vous ne ferez pas tout ce que nous faisons ici aujourd'hui, où chacun agit à son gré.
9 Gama ba ku kai wurin hutawa wanda Ubangiji Allahnku zai ba ku gādo ba tukuna.
Car jusqu'ici vous n'êtes point encore entrés dans le lieu de repos et dans la propriété que te donnera l'Éternel, ton Dieu.
10 Amma sa’ad da kuka haye Urdun, kuka zauna a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku ita gādo, zai kuwa ba ku hutu daga dukan abokan gābanku da suke kewaye da ku, kuka sami zaman lafiya,
Mais ayant une fois passé le Jourdain, et vous étant établis dans le pays dont l'Éternel, votre Dieu, veut vous mettre en possession après vous avoir débarrassés de tous vos ennemis d'alentour, et parvenus ainsi à un état de sécurité,
11 sai ku kai dukan abin da na umarce ku ku kai, wato, hadayu na ƙonawa, da sadakokinku, da zakkarku, da hadayunku na ɗagawa, da hadayunku na alkawarin da kuka yi wa Ubangiji a wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa yă sa sunansa.
alors, au lieu que vous choisira l'Éternel, votre Dieu, pour y fixer son nom, vous amènerez tout ce que je vous ai commandé, vos holocaustes et vos victimes, vos dîmes et les élévations de vos mains et le choix entier de vos oblations votives que vous aurez vouées à l'Éternel,
12 A can kuma za ku yi farin ciki a gaban Ubangiji Allahnku, ku da’ya’yanku maza da mata, da bayinku maza da mata, da kuma Lawiyawa daga biranenku, waɗanda ba a ba su rabo ba, ba su kuma da gādo na kansu.
et vous vous réjouirez en présence de l'Éternel, votre Dieu, vous et vos fils et vos filles et vos serviteurs et vos servantes et le Lévite qui sera dans vos Portes, car il n'a ni portion ni lot parmi vous.
13 Ku kula fa kada ku miƙa hadayun ƙonawa a wani wurin da kuka ga dama.
Garde-toi de sacrifier tes holocaustes dans tous les lieux que tu auras en vue;
14 Ku miƙa su kawai a wurin da Ubangiji zai zaɓa a cikin ɗaya daga kabilanku, a can za ku yi kowane abin da na umarce ku.
mais c'est au lieu que choisira l'Éternel dans l'une de tes Tribus; c'est là que tu sacrifieras tes holocaustes, là que tu feras, tout ce que je te prescris.
15 Amma kwa iya yanka nama ku ci a garuruwanku, a duk lokacin da ranku yake so, kamar yadda ake yi da gada ko barewa, bisa ga albarkar da Ubangiji Allahnku yake sa muku. Marar tsarki da mai tsarki, duka za ku iya ci.
Cependant toutes les fois que tu en auras le désir en ton âme, tue, et mange de la viande selon l'abondance dont l'Éternel, ton Dieu, te bénira, dans toutes tes Portes; on en pourra manger dans l'état de pureté ou d'impureté, comme de la gazelle et du cerf;
16 Amma kada ku ci jini, ku zubar da shi a ƙasa kamar ruwa.
seulement le sang vous ne le mangerez pas, vous le verserez sur la terre comme de l'eau.
17 Kada ku ci zakkar hatsi, da na sabon inabi, da kuma na mai a biranenku, ko kuwa na’ya’yan fari na garkunanku na shanu da na tumaki, ko kuwa duk wani abin da kuka yi alkawari za ku bayar, ko hadayunku na yardar rai, ko kyautai na musamman.
Tu ne pourras manger dans tes Portes les dîmes de ton blé et de ton moût et de ton huile, ni les premiers-nés de ton gros et menu bétail, ni aucune de tes oblations votives que tu voueras et de tes dons volontaires, ni les élévations de tes mains;
18 A maimakon haka, sai ku ci su a gaban Ubangiji Allahnku a wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa, da ku da’ya’yanku maza da mata, da bayinku maza da mata, da kuma Lawiyawa daga biranenku, ku kuwa yi farin ciki a gaban Ubangiji Allahnku a kowane abin da kuka sa hannunku.
mais c'est devant l'Éternel, ton Dieu, que tu les mangeras dans le lieu que choisira l'Éternel, ton Dieu, toi et ton fils et ta fille et ton serviteur et ta servante et le Lévite qui est dans tes Portes; et tu te réjouiras en présence de l'Éternel, ton Dieu, de tout le travail de tes mains.
19 Ku yi hankali, kada ku manta da Lawiyawa, muddin kuna zaune a ƙasarku.
Garde-toi de négliger le Lévite durant tout ton séjour dans ton pays.
20 Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya fadada iyakarku kamar yadda ya yi muku alkawari, kuka kuma ji marmarin nama, kuka kuma ce, “Muna so mu ci nama,” to, za ku iya cin yadda kuke so.
Lorsque l'Éternel, ton Dieu, aura étendu tes frontières, comme Il te l'a promis, et que tu diras: Je veux manger de la viande; parce que ton désir sera d'en manger, tu pourras manger de la viande suivant tout le désir de ton âme.
21 In wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa don yă sa Sunansa yana da nisa sosai daga inda kuke, za ku iya yankan dabbobi daga garkunanku na shanu da na tumakin da Ubangiji ya ba ku, kamar yadda na umarce ku, a cikin biranenku kuma za ku iya ci, yadda kuke so.
Si le lieu choisi par l'Éternel, ton Dieu, pour y fixer son nom, est trop éloigné de toi, tue une pièce du gros et du menu bétail que t'aura donné l'Éternel, ainsi que je te l'ai commandé, et manges-en dans tes Portes suivant tout le désir de ton âme;
22 Ku ci su yadda akan ci barewa ko mariri. Marar tsarki da mai tsarki, za ku iya ci.
seulement tu devras en user comme on use de la gazelle et du cerf; on en mangera dans l'état de pureté et dans l'état d'impureté également.
23 Amma ku tabbata ba ku ci jinin ba, domin jini ne rai, ba kuwa za ku ci rai cikin naman ba.
Seulement tiens ferme à ne pas manger le sang, car le sang est l'âme, et tu ne dois pas manger l'âme avec la chair;
24 Ba za ku ci jini ba, ku zubar da shi a ƙasa kamar ruwa.
tu ne le mangeras pas, tu le verseras sur la terre comme l'eau;
25 Kada ku ci shi, don ku zauna lafiya, da ku da’ya’yanku bayanku, gama za ku riƙa aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji.
tu ne le mangeras pas, pour que tu sois heureux, toi et tes fils après toi, en faisant ce qui est droit aux yeux de l'Éternel.
26 Amma ku ɗauki abubuwa masu tsarki, da kuma duk abin da kuka yi alkawari za ku bayar, ku tafi inda Ubangiji ya zaɓa.
D'ailleurs, quant aux choses saintes et aux oblations votives que tu auras, prends-les et rends-toi au lieu qu'aura choisi l'Éternel,
27 Ku miƙa hadayunku na ƙonawa a bagaden Ubangiji Allahnku, da naman da kuma jinin. Dole a zub da jinin hadayunku a gindin bagaden Ubangiji Allahnku, amma za ku iya cin naman.
et sacrifie tes holocaustes, la chair et le sang, sur l'Autel, de l'Éternel, ton Dieu, et que le sang de tes victimes soit versé à l'Autel de l'Éternel, ton Dieu; quant à la chair, mange-la.
28 Ku yi hankali, ku yi biyayya da dukan waɗannan umarnan da nake ba ku, da kuma’ya’yanku, don ku zauna lafiya, da ku da’ya’yanku a bayanku, gama za ku riƙa aikata abin da yake daidai da kuma yake mai kyau a gaban Ubangiji Allahnku.
Garde et observe toutes ces choses que je te prescris, pour que tu sois heureux, toi et tes fils après toi, jusqu'à l'éternité, en faisant ce qui est bien et droit aux yeux de l'Éternel, ton Dieu.
29 Ubangiji Allahnku zai kawar muku da al’umman nan da kuke niyyar shiga cikin ƙasarsu don ku kore su, bayan kuka kore su, kuka kuma zauna a ƙasarsu,
Lorsque l'Éternel, ton Dieu, aura extirpé les nations que tu viens chasser devant toi, et que tu les auras chassées, et que tu seras assis dans leur pays,
30 to, sai ku lura, kada ku jarrabtu ku kwaikwaye su bayan da an riga an shafe su daga gabanku, kada ku tambayi kome game da allolinsu, kuna cewa, “Yaya waɗannan al’ummai suke bauta wa allolinsu? Mu ma za mu yi kamar yadda suka yi.”
garde-toi de te laisser prendre au piège de leur exemple, une fois qu'elles auront été détruites par toi, ni attirer vers leurs dieux, pour dire: Le culte que ces nations rendent à leurs dieux, je veux l'imiter, moi aussi;
31 Ba za ku yi wa Ubangiji Allahnku sujada a hanyar da suke yi ba, gama a cikin yin sujada wa allolinsu, sun yi dukan abubuwan banƙyaman da Ubangiji yake ƙi. Har ma sukan ƙone’ya’yansu maza da mata a wuta a matsayin hadayu.
n'agis pas ainsi envers l'Éternel, ton Dieu; car elles faisaient pour leurs dieux tout ce qui est l'abomination de l'Éternel et qu'il déteste, allant jusqu'à brûler dans les flammes, à leurs dieux, leurs fils et leurs filles.
32 Ku lura, ku aikata dukan abin da na umarce ku; kada ku ƙara, kada ku rage daga cikin.
Gardez pour les pratiquer tous les préceptes que je vous prescris, et n'y faites ni addition ni retranchement.