< Maimaitawar Shari’a 12 >

1 Waɗannan su ne ƙa’idodi da kuma dokokin da za ku lura, ku kuma kiyaye a ƙasar da Ubangiji, Allahn kakanninku, yake ba ku don ku ci gādonta, muddin kuna zama a ƙasar.
These [are] the statutes and the judgments which you will take care! to observe in the land which he has given Yahweh [the] God of ancestors your to you to take possession of it all the days which you [are] alive on the land.
2 Ku hallaka dukan wuraren da al’umman da kuke kora suke yi wa allolinsu sujada, a kan duwatsu masu tsawo, da a kan tuddai, da kuma ƙarƙashin kowane itace gaba ɗaya.
Certainly you will destroy! all the places where they have served there the nations whom you [are] about to dispossess them gods their on the mountains high and on the hills and under every tree luxuriant.
3 Ku rurrushe bagadansu, ku farfashe keɓaɓɓun duwatsunsu, ku kuma ƙone ginshiƙan Asheransu da wuta; ku yayyanka gumakan allolinsu, ku kuma shafe sunayensu daga waɗannan wurare.
And you will break down altars their and you will shatter sacred pillars their and Asherah poles their you will burn! with fire and [the] images of gods their you will cut down! and you will destroy name their from the place that.
4 Ba za ku yi wa Ubangiji Allahnku sujada a hanyar da suke yi ba.
Not you will do! thus to Yahweh God your.
5 Amma sai ku nemi wurin da Ubangiji Allahnku zai zaɓa daga cikin dukan kabilanku, inda zai sa Sunansa, yă mai wurin mazauninsa. A wannan wuri ne za ku tafi;
That except to the place where he will choose Yahweh God your from all tribes your to put name his there to dwelling its you will resort and you will go there towards.
6 a can ne kuma za ku kawo hadayun ƙonawa da sadakoki, zakkarku da kyautai na musamman, da abin da kuka yi alkawari za ku bayar, da hadayunku na yardar rai, da kuma’ya’yan farin garkunanku na shanu da na tumaki.
And you will bring there towards burnt offerings your and sacrifices your and tithes your and [the] contribution of hand your and votive offerings your and freewill offerings your and [the] firstborn of herd[s] your and flock[s] your.
7 A can, a gaban Ubangiji Allahnku, ku da iyalanku za su ci, su kuma yi farin ciki a kome da kuka sa hannunku a kai, domin Ubangiji Allahnku zai albarkace ku.
And you will eat there before Yahweh God your and you will rejoice in every undertaking of hand your you and households your which he has blessed you Yahweh God your.
8 Kada ku yi kamar yadda muke yi a nan yau, yadda kowa yake yin abin da ya ga dama.
Not you must do! according to all that we [are] doing here this day everyone all the right in own eyes his.
9 Gama ba ku kai wurin hutawa wanda Ubangiji Allahnku zai ba ku gādo ba tukuna.
For not you have come until now to the resting place and to the inheritance which Yahweh God your [is] about to give to you.
10 Amma sa’ad da kuka haye Urdun, kuka zauna a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku ita gādo, zai kuwa ba ku hutu daga dukan abokan gābanku da suke kewaye da ku, kuka sami zaman lafiya,
And you will pass over the Jordan and you will dwell in the land which Yahweh God your [is] giving as an inheritance you and he will give rest to you from all enemies your from round about and you will dwell security.
11 sai ku kai dukan abin da na umarce ku ku kai, wato, hadayu na ƙonawa, da sadakokinku, da zakkarku, da hadayunku na ɗagawa, da hadayunku na alkawarin da kuka yi wa Ubangiji a wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa yă sa sunansa.
And it will be the place which he will choose Yahweh God your it to cause to dwell name his there there towards you will bring all that I [am] commanding you burnt offerings your and sacrifices your tithes your and [the] contribution of hand your and all [the] choicest of votive offerings your which you will vow to Yahweh.
12 A can kuma za ku yi farin ciki a gaban Ubangiji Allahnku, ku da’ya’yanku maza da mata, da bayinku maza da mata, da kuma Lawiyawa daga biranenku, waɗanda ba a ba su rabo ba, ba su kuma da gādo na kansu.
And you will rejoice before Yahweh God your you and sons your and daughters your and [male] servants your and female servants your and the Levite who [is] in gates your for not [belongs] to him a portion and an inheritance with you.
13 Ku kula fa kada ku miƙa hadayun ƙonawa a wani wurin da kuka ga dama.
Take heed to yourself lest you should offer up burnt offerings your in every place which you will see.
14 Ku miƙa su kawai a wurin da Ubangiji zai zaɓa a cikin ɗaya daga kabilanku, a can za ku yi kowane abin da na umarce ku.
That except in the place which he will choose Yahweh in one of tribes your there you will offer up burnt offerings your and there you will do all that I [am] commanding you.
15 Amma kwa iya yanka nama ku ci a garuruwanku, a duk lokacin da ranku yake so, kamar yadda ake yi da gada ko barewa, bisa ga albarkar da Ubangiji Allahnku yake sa muku. Marar tsarki da mai tsarki, duka za ku iya ci.
Only in all [the] desire of self your you will slaughter - and you will eat meat according to [the] blessing of Yahweh God your which he has given to you in all gates your the unclean and the clean he will eat it like gazelle and like deer.
16 Amma kada ku ci jini, ku zubar da shi a ƙasa kamar ruwa.
Only the blood not you must eat on the ground you will pour out it like water.
17 Kada ku ci zakkar hatsi, da na sabon inabi, da kuma na mai a biranenku, ko kuwa na’ya’yan fari na garkunanku na shanu da na tumaki, ko kuwa duk wani abin da kuka yi alkawari za ku bayar, ko hadayunku na yardar rai, ko kyautai na musamman.
Not you will be able to eat in gates your [the] tithe of grain your and new wine your and fresh oil your and [the] firstborn of herd your and flock your and all votive offerings your which you will vow and freewill offerings your and [the] contribution of hand your.
18 A maimakon haka, sai ku ci su a gaban Ubangiji Allahnku a wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa, da ku da’ya’yanku maza da mata, da bayinku maza da mata, da kuma Lawiyawa daga biranenku, ku kuwa yi farin ciki a gaban Ubangiji Allahnku a kowane abin da kuka sa hannunku.
That except before Yahweh God your you will eat it in the place which he will choose Yahweh God your it you and son your and daughter your and [male] servant your and female servant your and the Levite who [is] in gates your and you will rejoice before Yahweh God your in every undertaking of hand your.
19 Ku yi hankali, kada ku manta da Lawiyawa, muddin kuna zaune a ƙasarku.
Take heed to yourself lest you should neglect the Levite all days your on land your.
20 Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya fadada iyakarku kamar yadda ya yi muku alkawari, kuka kuma ji marmarin nama, kuka kuma ce, “Muna so mu ci nama,” to, za ku iya cin yadda kuke so.
If he will enlarge Yahweh God your territory your just as he spoke to you and you will say I want to eat meat for it will desire appetite your to eat meat in all [the] desire appetite your you will eat meat.
21 In wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa don yă sa Sunansa yana da nisa sosai daga inda kuke, za ku iya yankan dabbobi daga garkunanku na shanu da na tumakin da Ubangiji ya ba ku, kamar yadda na umarce ku, a cikin biranenku kuma za ku iya ci, yadda kuke so.
If it will be [too] far for you the place where he will choose Yahweh God your to put name his there and you will slaughter some of herd your and some of flock your which he has given Yahweh to you just as I commanded you and you will eat in gates your in all [the] desire of self your.
22 Ku ci su yadda akan ci barewa ko mariri. Marar tsarki da mai tsarki, za ku iya ci.
Surely just as it is eaten the gazelle and the deer so you will eat it the unclean and the clean alike he will eat it.
23 Amma ku tabbata ba ku ci jinin ba, domin jini ne rai, ba kuwa za ku ci rai cikin naman ba.
Only be strong to not to eat the blood for the blood it [is] the life and not you must eat the life with the meat.
24 Ba za ku ci jini ba, ku zubar da shi a ƙasa kamar ruwa.
Not you must eat it on the ground you will pour out it like water.
25 Kada ku ci shi, don ku zauna lafiya, da ku da’ya’yanku bayanku, gama za ku riƙa aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji.
Not you must eat it so that it may go well for you and for children your after you for you will do the right in [the] eyes of Yahweh.
26 Amma ku ɗauki abubuwa masu tsarki, da kuma duk abin da kuka yi alkawari za ku bayar, ku tafi inda Ubangiji ya zaɓa.
Only holy things your which they will belong to you and votive offerings your you will take and you will go to the place which he will choose Yahweh.
27 Ku miƙa hadayunku na ƙonawa a bagaden Ubangiji Allahnku, da naman da kuma jinin. Dole a zub da jinin hadayunku a gindin bagaden Ubangiji Allahnku, amma za ku iya cin naman.
And you will make burnt offerings your the flesh and the blood on [the] altar of Yahweh God your and [the] blood of sacrifices your it will be poured out on [the] altar of Yahweh God your and the flesh you will eat.
28 Ku yi hankali, ku yi biyayya da dukan waɗannan umarnan da nake ba ku, da kuma’ya’yanku, don ku zauna lafiya, da ku da’ya’yanku a bayanku, gama za ku riƙa aikata abin da yake daidai da kuma yake mai kyau a gaban Ubangiji Allahnku.
Take care and you will hear all the words these which I [am] commanding you so that it may go well for you and for children your after you until perpetuity for you will do the good [thing] and the right in [the] eyes of Yahweh God your.
29 Ubangiji Allahnku zai kawar muku da al’umman nan da kuke niyyar shiga cikin ƙasarsu don ku kore su, bayan kuka kore su, kuka kuma zauna a ƙasarsu,
If he will cut off Yahweh God your the nations where you [are] about to go there towards by dispossessing them from before you and you will dispossess them and you will dwell in land their.
30 to, sai ku lura, kada ku jarrabtu ku kwaikwaye su bayan da an riga an shafe su daga gabanku, kada ku tambayi kome game da allolinsu, kuna cewa, “Yaya waɗannan al’ummai suke bauta wa allolinsu? Mu ma za mu yi kamar yadda suka yi.”
Take heed to yourself lest you should be ensnared after them after have been destroyed they from before you and lest you should enquire of gods their saying how? do they serve the nations these gods their so I may do thus also I.
31 Ba za ku yi wa Ubangiji Allahnku sujada a hanyar da suke yi ba, gama a cikin yin sujada wa allolinsu, sun yi dukan abubuwan banƙyaman da Ubangiji yake ƙi. Har ma sukan ƙone’ya’yansu maza da mata a wuta a matsayin hadayu.
Not you will do thus to Yahweh God your for every abomination of Yahweh which he hates they have done to gods their for also sons their and daughters their they burn with fire to gods their.
32 Ku lura, ku aikata dukan abin da na umarce ku; kada ku ƙara, kada ku rage daga cikin.
Every word which I [am] commanding you it you will take care to do not you must add to it and not you must diminish from it.

< Maimaitawar Shari’a 12 >