< Maimaitawar Shari’a 12 >

1 Waɗannan su ne ƙa’idodi da kuma dokokin da za ku lura, ku kuma kiyaye a ƙasar da Ubangiji, Allahn kakanninku, yake ba ku don ku ci gādonta, muddin kuna zama a ƙasar.
These are the statutes and ordinances, which ye shall observe to do, in the land which the Lord, the God of thy fathers, giveth unto thee to possess it, and all the days that ye live upon the earth.
2 Ku hallaka dukan wuraren da al’umman da kuke kora suke yi wa allolinsu sujada, a kan duwatsu masu tsawo, da a kan tuddai, da kuma ƙarƙashin kowane itace gaba ɗaya.
Ye shall utterly destroy all the places whereon the nations which ye are about to drive out served their gods, upon the high mountains, and upon the hills, and under every green tree;
3 Ku rurrushe bagadansu, ku farfashe keɓaɓɓun duwatsunsu, ku kuma ƙone ginshiƙan Asheransu da wuta; ku yayyanka gumakan allolinsu, ku kuma shafe sunayensu daga waɗannan wurare.
And ye shall overthrow their altars, and break their statues, and their groves shall ye burn with fire; and the graven images of their gods shall ye hew down; and ye shall destroy their name out of the same place.
4 Ba za ku yi wa Ubangiji Allahnku sujada a hanyar da suke yi ba.
Ye shall not do so unto the Lord your God;
5 Amma sai ku nemi wurin da Ubangiji Allahnku zai zaɓa daga cikin dukan kabilanku, inda zai sa Sunansa, yă mai wurin mazauninsa. A wannan wuri ne za ku tafi;
But unto the place which the Lord your God may choose out of all your tribes to put his name there, even unto his habitation shall ye repair, and thither shalt thou come;
6 a can ne kuma za ku kawo hadayun ƙonawa da sadakoki, zakkarku da kyautai na musamman, da abin da kuka yi alkawari za ku bayar, da hadayunku na yardar rai, da kuma’ya’yan farin garkunanku na shanu da na tumaki.
And ye shall bring thither your burnt-offerings, and your sacrifices, and your tithes, and the heave-offering of your hand, and your vows, and your freewill-offerings, and the first-born of your herds and of your flocks;
7 A can, a gaban Ubangiji Allahnku, ku da iyalanku za su ci, su kuma yi farin ciki a kome da kuka sa hannunku a kai, domin Ubangiji Allahnku zai albarkace ku.
And ye shall eat there before the Lord your God, and ye shall rejoice with all the acquisition of your hand, ye and your households, wherewith the Lord thy God may have blessed thee.
8 Kada ku yi kamar yadda muke yi a nan yau, yadda kowa yake yin abin da ya ga dama.
Ye shall not do after all the manner that we do here this day, every one whatsoever is right in his own eyes.
9 Gama ba ku kai wurin hutawa wanda Ubangiji Allahnku zai ba ku gādo ba tukuna.
For ye are not as yet come to the rest and to the inheritance, which the Lord thy God giveth thee.
10 Amma sa’ad da kuka haye Urdun, kuka zauna a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku ita gādo, zai kuwa ba ku hutu daga dukan abokan gābanku da suke kewaye da ku, kuka sami zaman lafiya,
But ye will go over the Jordan, and dwell in the land which the Lord your God causeth you to inherit, and he will give you rest from all your enemies round about, so that ye may dwell in safety.
11 sai ku kai dukan abin da na umarce ku ku kai, wato, hadayu na ƙonawa, da sadakokinku, da zakkarku, da hadayunku na ɗagawa, da hadayunku na alkawarin da kuka yi wa Ubangiji a wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa yă sa sunansa.
And then shall it be, that the place which the Lord your God will choose to cause his name to dwell there, —[even] thither shall ye bring all that I command you: your burnt-offerings, and your sacrifices, your tithes, and the heave-offering of your hand, and all your choice vows which ye may vow unto the Lord;
12 A can kuma za ku yi farin ciki a gaban Ubangiji Allahnku, ku da’ya’yanku maza da mata, da bayinku maza da mata, da kuma Lawiyawa daga biranenku, waɗanda ba a ba su rabo ba, ba su kuma da gādo na kansu.
And ye shall rejoice before the Lord your God, ye, and your sons, and your daughters, and your men-servants, and your maid-servants, and the Levite who is within your gates; because he hath not any portion nor inheritance with you.
13 Ku kula fa kada ku miƙa hadayun ƙonawa a wani wurin da kuka ga dama.
Take heed to thyself that thou offer not thy burnt-offerings in every place which thou mayest see;
14 Ku miƙa su kawai a wurin da Ubangiji zai zaɓa a cikin ɗaya daga kabilanku, a can za ku yi kowane abin da na umarce ku.
But in the place which the Lord will choose in one of thy tribes, there shalt thou offer thy burnt-offerings, and there shalt thou do all that I command thee.
15 Amma kwa iya yanka nama ku ci a garuruwanku, a duk lokacin da ranku yake so, kamar yadda ake yi da gada ko barewa, bisa ga albarkar da Ubangiji Allahnku yake sa muku. Marar tsarki da mai tsarki, duka za ku iya ci.
Notwithstanding, according to all the longing of thy soul, mayest thou kill and eat flesh, according to the blessing of the Lord thy God which he hath given thee, in all thy gates: the unclean and the clean may eat thereof, as of the roebuck, and as of the hart.
16 Amma kada ku ci jini, ku zubar da shi a ƙasa kamar ruwa.
Only the blood shall ye not eat: upon the earth shall ye pour it out as water.
17 Kada ku ci zakkar hatsi, da na sabon inabi, da kuma na mai a biranenku, ko kuwa na’ya’yan fari na garkunanku na shanu da na tumaki, ko kuwa duk wani abin da kuka yi alkawari za ku bayar, ko hadayunku na yardar rai, ko kyautai na musamman.
Thou mayest not eat within thy gates the tithe of thy corn, or of thy wine, or of thy oil, nor the first-born of thy herds or of thy flocks, nor any of thy vows which thou mayest vow, nor thy freewill-offerings, and the heave-offering of thy hand;
18 A maimakon haka, sai ku ci su a gaban Ubangiji Allahnku a wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa, da ku da’ya’yanku maza da mata, da bayinku maza da mata, da kuma Lawiyawa daga biranenku, ku kuwa yi farin ciki a gaban Ubangiji Allahnku a kowane abin da kuka sa hannunku.
But before the Lord thy God must thou eat them in the place which the Lord thy God may choose, thou, and thy son, and thy daughter, and thy man-servant, and thy maid-servant, and the Levite who is within thy gates; and thou shalt rejoice before the Lord thy God with all the acquisition of thy hand.
19 Ku yi hankali, kada ku manta da Lawiyawa, muddin kuna zaune a ƙasarku.
Take heed to thyself that thou forsake not the Levite as long as thou livest upon thy land.
20 Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya fadada iyakarku kamar yadda ya yi muku alkawari, kuka kuma ji marmarin nama, kuka kuma ce, “Muna so mu ci nama,” to, za ku iya cin yadda kuke so.
When the Lord thy God will enlarge thy border, as he hath spoken unto thee, and thou dost say, I wish to eat flesh, because thy soul longeth to eat flesh: then mayest thou, according to all the longing of thy soul, eat flesh.
21 In wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa don yă sa Sunansa yana da nisa sosai daga inda kuke, za ku iya yankan dabbobi daga garkunanku na shanu da na tumakin da Ubangiji ya ba ku, kamar yadda na umarce ku, a cikin biranenku kuma za ku iya ci, yadda kuke so.
If the place which the Lord thy God may choose to put his name there be too far for thee: then mayest thou kill of thy herds and of thy flocks, which the Lord hath given thee, as I have commanded thee; and thou shalt eat in thy gates according to all the longing of thy soul.
22 Ku ci su yadda akan ci barewa ko mariri. Marar tsarki da mai tsarki, za ku iya ci.
But as the roebuck and the hart are eaten, so shalt thou eat the same: the unclean and the clean may eat thereof together.
23 Amma ku tabbata ba ku ci jinin ba, domin jini ne rai, ba kuwa za ku ci rai cikin naman ba.
Only be firm so as not to eat the blood; for the blood is the life; and thou shalt not eat the life with the flesh.
24 Ba za ku ci jini ba, ku zubar da shi a ƙasa kamar ruwa.
Thou shalt not eat it: upon the earth shalt thou pour it out like water.
25 Kada ku ci shi, don ku zauna lafiya, da ku da’ya’yanku bayanku, gama za ku riƙa aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji.
Thou shalt not eat it; in order that it may go well with thee, and with thy children after thee, when thou wilt do what is right in the eyes of the Lord.
26 Amma ku ɗauki abubuwa masu tsarki, da kuma duk abin da kuka yi alkawari za ku bayar, ku tafi inda Ubangiji ya zaɓa.
Nevertheless thy holy things which thou mayest have, and thy vows, shalt thou take, and go unto the place which the Lord may choose:
27 Ku miƙa hadayunku na ƙonawa a bagaden Ubangiji Allahnku, da naman da kuma jinin. Dole a zub da jinin hadayunku a gindin bagaden Ubangiji Allahnku, amma za ku iya cin naman.
And thou shalt offer thy burnt-offerings, the flesh and the blood, upon the altar of the Lord thy God; and the blood of thy sacrifices shall be poured out upon the altar of the Lord thy God, and the flesh shalt thou eat.
28 Ku yi hankali, ku yi biyayya da dukan waɗannan umarnan da nake ba ku, da kuma’ya’yanku, don ku zauna lafiya, da ku da’ya’yanku a bayanku, gama za ku riƙa aikata abin da yake daidai da kuma yake mai kyau a gaban Ubangiji Allahnku.
Observe and hear all these words which I command thee; in order that it may go well with thee, and with thy children after thee for ever, when thou wilt do what is good and right in the eyes of the Lord thy God.
29 Ubangiji Allahnku zai kawar muku da al’umman nan da kuke niyyar shiga cikin ƙasarsu don ku kore su, bayan kuka kore su, kuka kuma zauna a ƙasarsu,
When the Lord thy God will cut off the nations, whither thou goest to drive them out from before thee, and thou succeedest them, and dwellest in their land:
30 to, sai ku lura, kada ku jarrabtu ku kwaikwaye su bayan da an riga an shafe su daga gabanku, kada ku tambayi kome game da allolinsu, kuna cewa, “Yaya waɗannan al’ummai suke bauta wa allolinsu? Mu ma za mu yi kamar yadda suka yi.”
Then take heed to thyself that thou be not snared by following them, after they have been destroyed from before thee; and that thou inquire not after their gods, saying, How did these nations serve their gods? even so will I do likewise.
31 Ba za ku yi wa Ubangiji Allahnku sujada a hanyar da suke yi ba, gama a cikin yin sujada wa allolinsu, sun yi dukan abubuwan banƙyaman da Ubangiji yake ƙi. Har ma sukan ƙone’ya’yansu maza da mata a wuta a matsayin hadayu.
Thou shalt not do so unto the Lord thy God; for every abomination to the Lord, which he hateth, have they done unto their gods; for even their sons and their daughters have they burnt in the fire to their gods.
32 Ku lura, ku aikata dukan abin da na umarce ku; kada ku ƙara, kada ku rage daga cikin.
What thing soever I command you, even that shall ye observe to do: thou shalt not add thereto, and thou shalt not diminish therefrom.

< Maimaitawar Shari’a 12 >