< Maimaitawar Shari’a 11 >

1 To, sai ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku, kullum ku kuma kiyaye abubuwan da yake bukata, ku kiyaye ƙa’idodinsa, dokokinsa da kuma umarnansu.
C’est pourquoi aime le Seigneur ton Dieu, observe ses préceptes et ses cérémonies, ses ordonnances et ses commandements en tout temps.
2 Ku tuna a yau, cewa’ya’yanku ba su ne suka gani suka kuma ɗanɗana horon Ubangiji Allahnku ba; ba su suka gani girmansa, hannunsa mai ƙarfi, hannunsa mai iko;
Reconnaissez aujourd’hui ce que vos fils ignorent, eux qui n’ont pas vu les châtiments du Seigneur votre Dieu, ses merveilles, sa main puissante et son bras étendu;
3 alamun da ya aikata da abubuwan da ya yi a cikin Masar, ga Fir’auna sarkin Masar da kuma ga dukan ƙasarsa ba;
Les signes et les œuvres qu’il a faits au milieu de l’Egypte au roi Pharaon et à toute sa terre;
4 ba su suka gani abin da ya yi wa mayaƙan Masar, da dawakansu da keken yaƙinsu, yadda ya sha kansu da ruwan Jan Teku yayinda suke bin ku, da yadda Ubangiji ya hallaka su ƙaƙaf ba.
À toute l’armée des Egyptiens, à ses chevaux et à ses chariots: de quelle manière les eaux de la mer Rouge les ont couverts, lorsqu’ils vous poursuivaient, et comment le Seigneur les a détruits jusqu’au présent jour;
5 Ba’ya’yanku ba ne suka gani abin da ya yi dominku a hamada har sai da kuka kai wannan wuri ba,
Ce qu’il vous a fait à vous-mêmes dans le désert, jusqu’à ce que vous soyez venus en ce lieu;
6 ba su ba ne suka gani abin da ya yi ga Datan da Abiram,’ya’yan Eliyab mutumin Ruben, sa’ad da ƙasa ta buɗe bakinta a tsakiyar dukan Isra’ila ta haɗiye su tare da gidajensu, tentunansu da kowane abu mai rai da yake nasu ba.
Et à Dathan et à Abiron, fils d’Eliab, qui fut fils de Ruben, que la terre, ayant ouvert sa bouche, engloutit avec leurs maisons, leurs tentes et tout leur bien qu’ils avaient au milieu d’Israël.
7 Amma idanunku ne suka ga dukan waɗannan manyan abubuwan da Ubangiji ya yi.
Vos yeux ont vu toutes les œuvres grandes que le Seigneur a faites,
8 Saboda haka sai ku kiyaye dukan umarnan da nake ba ku a yau, don ku sami ƙarfin da za ku shiga, ku kuma karɓi ƙasar da kuke haye Urdun ku mallaka,
Afin que vous gardiez tous ses commandements, que moi je vous prescris aujourd’hui, que vous puissiez entrer et posséder la terre vers laquelle vous marchez,
9 domin kuma ku yi tsawon rai a ƙasar da Ubangiji ya rantse wa kakanninku zai ba su da zuriyarsu, ƙasa mai zub da madara da zuma.
Et que vous viviez longtemps en cette terre, que le Seigneur a promise avec serment à vos pères, et à leur postérité, et où coulent du lait et du miel
10 Ƙasar da kuke shiga, ku karɓa, ba kamar ƙasar Masar ba ce, inda kuka fito, inda kuka shuka iri, ku yi ta zuwa kuna banruwa kamar lambu.
Car la terre dans laquelle tu entreras pour la posséder, n’est pas comme la terre d’Egypte dont tu es sorti, où, la semence jetée, on conduit comme dans les jardins, des eaux qui servent à arroser;
11 Amma ƙasar da kuke haye Urdun ku mallaki, ƙasa ce ta duwatsu da kwaruruka wadda ruwan sama ne yake jiƙe ta.
Mais c’est une terre de montagnes et de plaines, qui attend du ciel de la pluie;
12 Ƙasa ce da Ubangiji Allahnku yake lura da ita; idanun Ubangiji Allahnku yana a kai daga farkon shekara har zuwa ƙarshenta.
Que le Seigneur ton Dieu regarde toujours; et ses yeux sont sur elle depuis le commencement de l’année jusqu’à sa fin.
13 Saboda haka in kun yi biyayya ga umarnan da nake ba ku a yau cikin aminci, kuna ƙaunaci Ubangiji Allahnku, kuna kuma bauta masa da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku,
Si donc vous obéissez à mes commandements, que moi, je vous prescris aujourd’hui, d’aimer le Seigneur votre Dieu, et de le servir en tout votre cœur et en toute votre âme,
14 sai in aika da ruwan sama a ƙasarku a lokacinsa, ruwan saman bazara da kuma na kaka, don ku tattara hatsinku, sabon inabinku da kuma manku.
Il donnera à votre terre les premières et les dernières pluies, afin que vous recueilliez le blé, le vin et l’huile,
15 Zan tanadar da ciyawa a filaye don shanunku, za ku ci, ku kuma ƙoshi.
Et du foin des champs pour nourrir vos bestiaux, et pour que vous-mêmes, vous mangiez et soyez rassasiés.
16 Ku yi hankali, kada a ruɗe ku har ku bauta wa alloli, ku kuma yi musu sujada,
Prenez garde que votre cœur ne soit séduit, que vous ne vous éloigniez du Seigneur, que vous ne serviez des dieux étrangers, et que vous ne les adoriez:
17 don kada fushin Ubangiji yă ƙuna a kanku, yă rufe sammai, ku rasa ruwa, ƙasa kuma ta kāsa ba da amfaninta, da haka za ku murmutu nan da nan a kyakkyawar ƙasar da Ubangiji yake ba ku.
Et, qu’irrité, le Seigneur ne ferme le ciel, que les pluies ne descendent pas, que la terre ne donne pas sa végétation, que vous ne soyez exterminés en peu de temps de la terre excellente que le Seigneur va vous donner.
18 Saboda haka, sai ku riƙe waɗannan kalmomina gam a zukatanku da ranku; ku ɗaura su kamar alama a hannuwanku, da goshinku.
Déposez ces paroles que je dis dans vos cœurs et dans vos esprits, et suspendez-les comme un signe à vos mains, et placez-les entre vos yeux,
19 Ku koyar da su ga’ya’yanku, ku yi ta haddace su, sa’ad da kuke zaune a gida, da sa’ad da kuke tafiya, sa’ad da kuke kwance, da sa’ad da kuka tashi.
Apprenez-les à vos enfants, pour qu’ils les méditent; lorsque tu seras assis en ta maison, lorsque tu marcheras dans la voie, que tu te coucheras et que tu te lèveras,
20 Ku rubuta su a kan madogaran ƙofofin gidajenku, da a kan ƙofofinku,
Tu les écriras sur les poteaux et sur les portes de ta maison;
21 saboda kwanakinku da kwanakin’ya’yanku su yi tsawo a ƙasar da Ubangiji ya rantse zai ba wa kakanninku, muddin sama tana bisa duniya.
Afin que se multiplient tes jours et ceux de tes enfants dans la terre que le Seigneur a juré à tes pères de leur donner, tant que le ciel sera suspendu au-dessus de la terre.
22 In kuka lura, kuka kuma kiyaye dukan umarnai da nake ba ku, ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku, ku yi tafiya a hanyoyinsa, ku kuma riƙe shi gam,
Car si vous gardez et si vous pratiquez les commandements que moi, je vous prescris, d’aimer le Seigneur votre Dieu, et de marcher dans toutes ses voies, vous attachant à lui,
23 Ubangiji zai kori dukan waɗannan al’ummai a gabanku, za ku kuma kore al’umman da suka fi ku yawa da ƙarfi.
Le Seigneur détruira toutes ces nations devant votre face et vous les posséderez, ces nations qui sont plus grandes et plus fortes que vous.
24 Duk inda tafin ƙafanku ya taka, zai zama naku; iyakarku zai kama daga hamadan Lebanon da kuma daga Kogin Yuferites zuwa Bahar Rum.
Tout lieu que foulera votre pied sera à vous. Depuis le désert et depuis le Liban, depuis le grand fleuve d’Euphrate jusqu’à la mer occidentale, ce seront vos limites.
25 Babu mutumin da zai iya tsayayya da ku. Ubangiji Allahnku, zai sa razana da tsoronku a dukan ƙasar, a duk inda kuka tafi, kamar yadda ya alkawarta muku.
Nul ne tiendra contre vous: le Seigneur votre Dieu jettera la terreur et l’effroi sur toute la terre que vous devez fouler, comme il vous a dit.
26 Ga shi, a yau, ina sa a gabanku albarka da kuma la’ana,
Voici que je mets aujourd’hui en votre présence la bénédiction et la malédiction:
27 albarka in kun yi biyayya da umarnan Ubangiji Allahnku, da nake ba ku;
La bénédiction, si vous obéissez aux commandements du Seigneur votre Dieu, que moi, je vous prescris aujourd’hui:
28 la’ana in ba ku yi biyayya da umarnan Ubangiji Allahnku, kuka kuma juya daga hanyar da na umarce ku, ta wurin bin waɗansu alloli, waɗanda ba ku sani ba.
La malédiction, si vous n’obéissez pas aux commandements du Seigneur votre Dieu, mais si vous vous écartez de la voie que moi, je vous montre maintenant, et que vous marchiez après des dieux étrangers que vous ne connaissez pas.
29 Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya kawo ku cikin ƙasar da za ku shiga ku ci gādonta, sai ku yi shelar albarkun nan a dutsen Gerizim, ku kuma yi na la’ana a dutsen Ebal.
Mais lorsque le Seigneur ton Dieu t’aura introduit dans la terre vers laquelle tu chemines pour l’habiter, tu mettras la bénédiction sur la montagne de Garizim, et la malédiction sur la montagne d’Hébal,
30 Waɗannan duwatsu biyu suna a hayin Urdun, yamma da hanya a ƙasar Kan’aniyawa mazaunan Araba, kusa da Gilgal wajajen manyan itatuwan More.
Qui sont au-delà du Jourdain, derrière la voie qui tourne à l’occident, dans la terre du Chananéen, qui habite dans les plaines contre Galgala, qui est près d’une vallée qui s’étend et s’avance au loin.
31 Kuna gab da ƙetare Urdun fa, ku shiga, ku kuma mallaki ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku. Sa’ad da kuka karɓe ta, kuka kuma zauna a can,
Car vous, vous passerez le Jourdain, pour posséder la terre que le Seigneur votre Dieu doit vous donner, afin que vous l’ayez et que vous la possédiez.
32 ku tabbata kun yi biyayya da dukan ƙa’idodi, da kuma dokokin da nake sawa a gabanku a yau.
Voyez donc à ce que vous accomplissiez les cérémonies et les ordonnances que moi, je mettrai en votre présence aujourd’hui.

< Maimaitawar Shari’a 11 >