< Maimaitawar Shari’a 11 >

1 To, sai ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku, kullum ku kuma kiyaye abubuwan da yake bukata, ku kiyaye ƙa’idodinsa, dokokinsa da kuma umarnansu.
Aime donc l'Eternel ton Dieu, et garde toujours ce qu'il veut que tu gardes, ses statuts, ses lois, et ses commandements.
2 Ku tuna a yau, cewa’ya’yanku ba su ne suka gani suka kuma ɗanɗana horon Ubangiji Allahnku ba; ba su suka gani girmansa, hannunsa mai ƙarfi, hannunsa mai iko;
Et connaissez aujourd'hui que ce ne sont pas vos enfants qui ont connu, et qui ont vu le châtiment de l'Eternel votre Dieu, sa grandeur, sa main forte, et son bras étendu;
3 alamun da ya aikata da abubuwan da ya yi a cikin Masar, ga Fir’auna sarkin Masar da kuma ga dukan ƙasarsa ba;
Et ses signes, et les œuvres qu'il a faites au milieu de l'Egypte, contre Pharaon Roi d'Egypte, et contre tout son pays;
4 ba su suka gani abin da ya yi wa mayaƙan Masar, da dawakansu da keken yaƙinsu, yadda ya sha kansu da ruwan Jan Teku yayinda suke bin ku, da yadda Ubangiji ya hallaka su ƙaƙaf ba.
Et ce qu'il a fait à l'armée d'Egypte, à ses chevaux et à ses chariots, quand il a fait que les eaux de la mer Rouge les ont couverts, lorsqu'ils vous poursuivaient; car l'Eternel les a détruits jusqu'à ce jour;
5 Ba’ya’yanku ba ne suka gani abin da ya yi dominku a hamada har sai da kuka kai wannan wuri ba,
Et ce qu'il a fait pour vous dans ce désert, jusqu'à ce que vous êtes arrivés en ce lieu-ci;
6 ba su ba ne suka gani abin da ya yi ga Datan da Abiram,’ya’yan Eliyab mutumin Ruben, sa’ad da ƙasa ta buɗe bakinta a tsakiyar dukan Isra’ila ta haɗiye su tare da gidajensu, tentunansu da kowane abu mai rai da yake nasu ba.
Et ce qu'il a fait à Dathan, et à Abiram, enfants d'Eliab, fils de Ruben, [et] comment la terre ouvrit sa bouche, et les engloutit avec leurs familles et leurs tentes, et tout ce qui était en leur puissance, au milieu de tout Israël;
7 Amma idanunku ne suka ga dukan waɗannan manyan abubuwan da Ubangiji ya yi.
Mais ce sont vos yeux qui ont vu toutes les grandes œuvres que l'Eternel a faites.
8 Saboda haka sai ku kiyaye dukan umarnan da nake ba ku a yau, don ku sami ƙarfin da za ku shiga, ku kuma karɓi ƙasar da kuke haye Urdun ku mallaka,
Vous garderez donc tous les commandements que je vous prescris aujourd'hui, afin que vous soyez fortifiés, et que vous entriez en possession du pays, dans lequel vous allez passer pour le posséder.
9 domin kuma ku yi tsawon rai a ƙasar da Ubangiji ya rantse wa kakanninku zai ba su da zuriyarsu, ƙasa mai zub da madara da zuma.
Et afin que vous prolongiez vos jours sur la terre que l'Eternel a juré à vos pères de leur donner, et à leur postérité, terre où coulent le lait et le miel.
10 Ƙasar da kuke shiga, ku karɓa, ba kamar ƙasar Masar ba ce, inda kuka fito, inda kuka shuka iri, ku yi ta zuwa kuna banruwa kamar lambu.
Car le pays où tu vas entrer pour le posséder n'[est] pas comme le pays d'Egypte, duquel vous êtes sortis, où tu semais ta semence, et l'arrosais avec ton pied, comme un jardin à herbes.
11 Amma ƙasar da kuke haye Urdun ku mallaki, ƙasa ce ta duwatsu da kwaruruka wadda ruwan sama ne yake jiƙe ta.
Mais le pays dans lequel vous allez passer pour le posséder, est un pays de montagnes et de campagnes, et il est abreuvé d'eau selon qu'il pleut des cieux.
12 Ƙasa ce da Ubangiji Allahnku yake lura da ita; idanun Ubangiji Allahnku yana a kai daga farkon shekara har zuwa ƙarshenta.
C'est un pays dont l'Eternel ton Dieu a soin, sur lequel l'Eternel ton Dieu a continuellement ses yeux, depuis le commencement de l'année jusqu'à la fin.
13 Saboda haka in kun yi biyayya ga umarnan da nake ba ku a yau cikin aminci, kuna ƙaunaci Ubangiji Allahnku, kuna kuma bauta masa da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku,
Il arrivera donc que si vous obéissez exactement à mes commandements, lesquels je vous prescris aujourd'hui, que vous aimiez l'Eternel votre Dieu, et que vous le serviez de tout votre cœur et de toute votre âme,
14 sai in aika da ruwan sama a ƙasarku a lokacinsa, ruwan saman bazara da kuma na kaka, don ku tattara hatsinku, sabon inabinku da kuma manku.
Alors je donnerai la pluie telle qu'il faut à votre pays en sa saison, la pluie de la première et de la dernière saison, et tu recueilleras ton froment, ton vin excellent, et ton huile.
15 Zan tanadar da ciyawa a filaye don shanunku, za ku ci, ku kuma ƙoshi.
Je ferai croître aussi dans ton champ de l'herbe pour ton bétail; tu mangeras et tu seras rassasié.
16 Ku yi hankali, kada a ruɗe ku har ku bauta wa alloli, ku kuma yi musu sujada,
Prenez garde à vous, de peur que votre cœur ne soit séduit, et que vous ne vous détourniez, et serviez d'autres dieux, et vous prosterniez devant eux;
17 don kada fushin Ubangiji yă ƙuna a kanku, yă rufe sammai, ku rasa ruwa, ƙasa kuma ta kāsa ba da amfaninta, da haka za ku murmutu nan da nan a kyakkyawar ƙasar da Ubangiji yake ba ku.
Et que la colère de l'Eternel ne s'enflamme contre vous, et qu'il ne ferme les cieux, tellement qu'il n'y ait point de pluie; et que la terre ne donne point son fruit; et que vous ne périssiez aussitôt sur ce bon pays que l'Eternel vous donne.
18 Saboda haka, sai ku riƙe waɗannan kalmomina gam a zukatanku da ranku; ku ɗaura su kamar alama a hannuwanku, da goshinku.
Mettez donc dans votre cœur et dans votre entendement ces paroles que je vous dis, et liez-les pour signe sur vos mains, et qu'elles soient pour fronteaux entre vos yeux,
19 Ku koyar da su ga’ya’yanku, ku yi ta haddace su, sa’ad da kuke zaune a gida, da sa’ad da kuke tafiya, sa’ad da kuke kwance, da sa’ad da kuka tashi.
Et enseignez-les à vos enfants, en vous en entretenant, soit que tu te tiennes dans ta maison, soit que tu voyages, soit que tu te couches, soit que tu te lèves.
20 Ku rubuta su a kan madogaran ƙofofin gidajenku, da a kan ƙofofinku,
Tu les écriras aussi sur les poteaux de ta maison, et sur tes portes.
21 saboda kwanakinku da kwanakin’ya’yanku su yi tsawo a ƙasar da Ubangiji ya rantse zai ba wa kakanninku, muddin sama tana bisa duniya.
Afin que vos jours et les jours de vos enfants soient multipliés sur la terre que l'Eternel a juré à vos pères de leur donner, [qu'ils soient, dis-je, multipliés] comme les jours des cieux sur la terre.
22 In kuka lura, kuka kuma kiyaye dukan umarnai da nake ba ku, ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku, ku yi tafiya a hanyoyinsa, ku kuma riƙe shi gam,
Car si vous gardez soigneusement tous ces commandements que je vous ordonne de faire, aimant l'Eternel votre Dieu, marchant dans toutes ses voies, et vous attachant à lui;
23 Ubangiji zai kori dukan waɗannan al’ummai a gabanku, za ku kuma kore al’umman da suka fi ku yawa da ƙarfi.
Alors l'Eternel chassera toutes ces nations-là de devant vous et vous posséderez le pays des nations qui sont plus grandes et plus puissantes que vous.
24 Duk inda tafin ƙafanku ya taka, zai zama naku; iyakarku zai kama daga hamadan Lebanon da kuma daga Kogin Yuferites zuwa Bahar Rum.
Tout lieu où vous aurez mis la plante de votre pied sera à vous; vos frontières seront du désert au Liban; [et] depuis le fleuve, qui est le fleuve d'Euphrate, jusqu'à la mer d'Occident.
25 Babu mutumin da zai iya tsayayya da ku. Ubangiji Allahnku, zai sa razana da tsoronku a dukan ƙasar, a duk inda kuka tafi, kamar yadda ya alkawarta muku.
Nul ne pourra se soutenir devant vous; l'Eternel votre Dieu mettra la frayeur et la terreur qu'on aura de vous, par toute la terre sur laquelle vous marcherez, ainsi qu'il vous en a parlé.
26 Ga shi, a yau, ina sa a gabanku albarka da kuma la’ana,
Regardez, je vous propose aujourd'hui la bénédiction et la malédiction;
27 albarka in kun yi biyayya da umarnan Ubangiji Allahnku, da nake ba ku;
La bénédiction, si vous obéissez aux commandements de l'Eternel votre Dieu, lesquels je vous prescris aujourd'hui;
28 la’ana in ba ku yi biyayya da umarnan Ubangiji Allahnku, kuka kuma juya daga hanyar da na umarce ku, ta wurin bin waɗansu alloli, waɗanda ba ku sani ba.
La malédiction, si vous n'obéissez point aux commandements de l'Eternel votre Dieu, et si vous vous détournez de la voie que je vous prescris aujourd'hui, pour marcher après d'autres dieux que vous n'avez point connus.
29 Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya kawo ku cikin ƙasar da za ku shiga ku ci gādonta, sai ku yi shelar albarkun nan a dutsen Gerizim, ku kuma yi na la’ana a dutsen Ebal.
Et quand l'Eternel ton Dieu t'aura fait entrer au pays où tu vas pour le posséder, tu prononceras alors les bénédictions, étant sur la montagne de Guérizim, et les malédictions, étant sur la montagne de Hébal.
30 Waɗannan duwatsu biyu suna a hayin Urdun, yamma da hanya a ƙasar Kan’aniyawa mazaunan Araba, kusa da Gilgal wajajen manyan itatuwan More.
[Ces montagnes] ne sont-elles pas au delà du Jourdain, sur le chemin qui tire vers le soleil couchant, au pays des Cananéens qui demeurent en la campagne, vis-à-vis de Guilgal, près des plaines de Moré?
31 Kuna gab da ƙetare Urdun fa, ku shiga, ku kuma mallaki ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku. Sa’ad da kuka karɓe ta, kuka kuma zauna a can,
Car vous allez passer le Jourdain, pour entrer au pays que l'Eternel votre Dieu vous donne pour le posséder; vous le posséderez, et vous y habiterez.
32 ku tabbata kun yi biyayya da dukan ƙa’idodi, da kuma dokokin da nake sawa a gabanku a yau.
Vous prendrez donc garde de faire tous les statuts et les droits que je vous propose aujourd'hui.

< Maimaitawar Shari’a 11 >