< Maimaitawar Shari’a 11 >
1 To, sai ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku, kullum ku kuma kiyaye abubuwan da yake bukata, ku kiyaye ƙa’idodinsa, dokokinsa da kuma umarnansu.
Therfor loue thi Lord God, and kepe thou hise comaundementis and cerymonyes, domes and heestis, in al tyme.
2 Ku tuna a yau, cewa’ya’yanku ba su ne suka gani suka kuma ɗanɗana horon Ubangiji Allahnku ba; ba su suka gani girmansa, hannunsa mai ƙarfi, hannunsa mai iko;
Knowe ye to day tho thingis whiche youre sones knowen not, `whiche sones sien not the doctryn of youre Lord God, hise grete dedis, and strong hond, and `arm holdun forth,
3 alamun da ya aikata da abubuwan da ya yi a cikin Masar, ga Fir’auna sarkin Masar da kuma ga dukan ƙasarsa ba;
myraclis and werkis, whiche he dide `in the myddis of Egipt to Farao, kyng, and to al `the lond of hym, and to al the oost of Egipcians,
4 ba su suka gani abin da ya yi wa mayaƙan Masar, da dawakansu da keken yaƙinsu, yadda ya sha kansu da ruwan Jan Teku yayinda suke bin ku, da yadda Ubangiji ya hallaka su ƙaƙaf ba.
and to horsis, and carris; hou the watris of the reed see hiliden hem, whanne thei pursueden you, and the Lord `dide awei hem `til in to `present dai;
5 Ba’ya’yanku ba ne suka gani abin da ya yi dominku a hamada har sai da kuka kai wannan wuri ba,
and whiche thingis the Lord dide to you in wildernesse, til ye camen to this place;
6 ba su ba ne suka gani abin da ya yi ga Datan da Abiram,’ya’yan Eliyab mutumin Ruben, sa’ad da ƙasa ta buɗe bakinta a tsakiyar dukan Isra’ila ta haɗiye su tare da gidajensu, tentunansu da kowane abu mai rai da yake nasu ba.
and to Dathan and Abiron, `the sones of Heliab, that was `the sone of Ruben, whiche the erthe swolewide, whanne his mouth was openyd, with `the housis and tabernaclis, and al the catel `of hem which thei hadden, in the myddis of Israel.
7 Amma idanunku ne suka ga dukan waɗannan manyan abubuwan da Ubangiji ya yi.
Youre iyen sien alle the grete werkis of the Lord,
8 Saboda haka sai ku kiyaye dukan umarnan da nake ba ku a yau, don ku sami ƙarfin da za ku shiga, ku kuma karɓi ƙasar da kuke haye Urdun ku mallaka,
whiche he dide, that ye kepe alle hise heestis whiche Y comaunde to dai to you, and that ye moun entre, and welde the lond,
9 domin kuma ku yi tsawon rai a ƙasar da Ubangiji ya rantse wa kakanninku zai ba su da zuriyarsu, ƙasa mai zub da madara da zuma.
to which ye schulen entre, and ye lyue therynne in myche time; which lond, flowynge with mylk and hony, the Lord bihiyte vndur an ooth to youre fadris and to `the seed of hem.
10 Ƙasar da kuke shiga, ku karɓa, ba kamar ƙasar Masar ba ce, inda kuka fito, inda kuka shuka iri, ku yi ta zuwa kuna banruwa kamar lambu.
For the lond, to which thou schalt entre to welde, is not as the lond of Egipt, `out of which thou yedist, where whanne the seed is cast in the maner of gardyns, moist waters ben led;
11 Amma ƙasar da kuke haye Urdun ku mallaki, ƙasa ce ta duwatsu da kwaruruka wadda ruwan sama ne yake jiƙe ta.
but it is hilli, and feldi, and abidith reynes fro heuene,
12 Ƙasa ce da Ubangiji Allahnku yake lura da ita; idanun Ubangiji Allahnku yana a kai daga farkon shekara har zuwa ƙarshenta.
which lond thi Lord God biholdith, and hise iyen ben therynne, fro the bigynnyng of the yeer `til to the ende therof.
13 Saboda haka in kun yi biyayya ga umarnan da nake ba ku a yau cikin aminci, kuna ƙaunaci Ubangiji Allahnku, kuna kuma bauta masa da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku,
Therfor if ye schulen obeie to myn heestis whiche Y comaunde to dai to you, that ye loue youre Lord God, and serue hym in al youre herte, and in al youre soule;
14 sai in aika da ruwan sama a ƙasarku a lokacinsa, ruwan saman bazara da kuma na kaka, don ku tattara hatsinku, sabon inabinku da kuma manku.
he schal yyue to youre lond reyn tymeful and late, that ye gadere wheete, and wyn, and oile,
15 Zan tanadar da ciyawa a filaye don shanunku, za ku ci, ku kuma ƙoshi.
hey of the feeldis to feede beestis, that ye bothe ete and be fillid.
16 Ku yi hankali, kada a ruɗe ku har ku bauta wa alloli, ku kuma yi musu sujada,
Be ye war, lest perauenture youre herte be disseyued, and ye go awei fro the Lord, and serue alien goddis, and worschipe hem;
17 don kada fushin Ubangiji yă ƙuna a kanku, yă rufe sammai, ku rasa ruwa, ƙasa kuma ta kāsa ba da amfaninta, da haka za ku murmutu nan da nan a kyakkyawar ƙasar da Ubangiji yake ba ku.
and the Lord be wrooth, and close heuene, and reynes come not doun, nether the erthe yyue his fruyt, and ye perische swiftli fro the beste lond which the Lord schal yyue to you.
18 Saboda haka, sai ku riƙe waɗannan kalmomina gam a zukatanku da ranku; ku ɗaura su kamar alama a hannuwanku, da goshinku.
Putte ye thes wordis in youre hertes and soules, and honge ye `tho wordis for a signe in the hondis, and sette ye bitwixe youre iyen.
19 Ku koyar da su ga’ya’yanku, ku yi ta haddace su, sa’ad da kuke zaune a gida, da sa’ad da kuke tafiya, sa’ad da kuke kwance, da sa’ad da kuka tashi.
Teche youre sones, that thei thenke on tho wordis, whanne thou sittist in thin hows, and goist in the weie, and lyggist doun, and risist.
20 Ku rubuta su a kan madogaran ƙofofin gidajenku, da a kan ƙofofinku,
Thou schalt write tho wordis on the postis, and yatis of thin hous,
21 saboda kwanakinku da kwanakin’ya’yanku su yi tsawo a ƙasar da Ubangiji ya rantse zai ba wa kakanninku, muddin sama tana bisa duniya.
that the daies of thee and of thi sones be multiplied in the lond which the Lord swoor to thi fadris, that he schulde yyue to hem, as long as heuene is aboue erthe.
22 In kuka lura, kuka kuma kiyaye dukan umarnai da nake ba ku, ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku, ku yi tafiya a hanyoyinsa, ku kuma riƙe shi gam,
For if ye kepen the heestis whiche Y comaunde to you, and ye do tho, that ye loue youre Lord God, and go in alle hise weies,
23 Ubangiji zai kori dukan waɗannan al’ummai a gabanku, za ku kuma kore al’umman da suka fi ku yawa da ƙarfi.
and cleue to hym, the Lord schal destrie alle these hethen men bifor youre face, and ye schulen welde tho folkis that ben grettere and strongere than ye.
24 Duk inda tafin ƙafanku ya taka, zai zama naku; iyakarku zai kama daga hamadan Lebanon da kuma daga Kogin Yuferites zuwa Bahar Rum.
Ech place which youre foot schal trede, schal be youre; fro the deseert, and fro the Liban, and fro the greet flood Eufrates `til to the west see, schulen be youre termes.
25 Babu mutumin da zai iya tsayayya da ku. Ubangiji Allahnku, zai sa razana da tsoronku a dukan ƙasar, a duk inda kuka tafi, kamar yadda ya alkawarta muku.
Noon schal stonde ayens you; youre Lord God schal yiue youre outward drede and inward drede on ech lond which ye schulen trede, as he spak to you.
26 Ga shi, a yau, ina sa a gabanku albarka da kuma la’ana,
Lo! Y sette forth in youre siyt to day blissyng and cursyng;
27 albarka in kun yi biyayya da umarnan Ubangiji Allahnku, da nake ba ku;
blessyng, if ye obeien to the heestis of youre Lord God, whiche Y comaunde to you to dai;
28 la’ana in ba ku yi biyayya da umarnan Ubangiji Allahnku, kuka kuma juya daga hanyar da na umarce ku, ta wurin bin waɗansu alloli, waɗanda ba ku sani ba.
cursyng, if ye heren not the heestis of youre Lord God, but goen awei fro the weie which Y schewe now to you, and goen after alien goddis whiche ye knowen not.
29 Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya kawo ku cikin ƙasar da za ku shiga ku ci gādonta, sai ku yi shelar albarkun nan a dutsen Gerizim, ku kuma yi na la’ana a dutsen Ebal.
Sotheli whanne thi Lord God hath brouyt thee in to the lond, to which to enhabite thou goist, thou schalt sette blessyng on the hil Garisym, cursyng on the hil Hebal, whiche hillis ben biyende Jordan,
30 Waɗannan duwatsu biyu suna a hayin Urdun, yamma da hanya a ƙasar Kan’aniyawa mazaunan Araba, kusa da Gilgal wajajen manyan itatuwan More.
aftir the weie that goith to the goyng doun of the sunne, in the lond of Cananey, that dwellith in the feeldi places ayens Galgala, which is bisidis the valey goynge and entrynge fer.
31 Kuna gab da ƙetare Urdun fa, ku shiga, ku kuma mallaki ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku. Sa’ad da kuka karɓe ta, kuka kuma zauna a can,
For ye schulen passe Jordan, that ye welde the lond which youre Lord God schal yyue to you, and that ye haue and welde that lond.
32 ku tabbata kun yi biyayya da dukan ƙa’idodi, da kuma dokokin da nake sawa a gabanku a yau.
Therfor se ye, `that ye fille the cerymonyes and domes, whiche I schal sette to dai in youre siyt.