< Maimaitawar Shari’a 11 >
1 To, sai ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku, kullum ku kuma kiyaye abubuwan da yake bukata, ku kiyaye ƙa’idodinsa, dokokinsa da kuma umarnansu.
Therefore you will love Yahweh your God and always keep his instructions, his statutes, his decrees, and his commandments.
2 Ku tuna a yau, cewa’ya’yanku ba su ne suka gani suka kuma ɗanɗana horon Ubangiji Allahnku ba; ba su suka gani girmansa, hannunsa mai ƙarfi, hannunsa mai iko;
Notice that I am not speaking to your children, who have not known nor have they seen the punishment of Yahweh your God, his greatness, his mighty hand, or his outstretched arm,
3 alamun da ya aikata da abubuwan da ya yi a cikin Masar, ga Fir’auna sarkin Masar da kuma ga dukan ƙasarsa ba;
the signs and deeds that he did in the midst of Egypt to Pharaoh, king of Egypt, and to all his land.
4 ba su suka gani abin da ya yi wa mayaƙan Masar, da dawakansu da keken yaƙinsu, yadda ya sha kansu da ruwan Jan Teku yayinda suke bin ku, da yadda Ubangiji ya hallaka su ƙaƙaf ba.
Neither did they see what he did to the army of Egypt, to their horses, or to their chariots, how he made the water of the Sea of Reeds overwhelm them as they pursued after you, and how Yahweh has destroyed them until today,
5 Ba’ya’yanku ba ne suka gani abin da ya yi dominku a hamada har sai da kuka kai wannan wuri ba,
or what he did for you in the wilderness until you came to this place.
6 ba su ba ne suka gani abin da ya yi ga Datan da Abiram,’ya’yan Eliyab mutumin Ruben, sa’ad da ƙasa ta buɗe bakinta a tsakiyar dukan Isra’ila ta haɗiye su tare da gidajensu, tentunansu da kowane abu mai rai da yake nasu ba.
They had not seen what Yahweh had done to Dathan and Abiram, the sons of Eliab son of Reuben, how the earth opened its mouth and swallowed them up, their households, their tents, and every living thing that followed them, in the middle of all Israel.
7 Amma idanunku ne suka ga dukan waɗannan manyan abubuwan da Ubangiji ya yi.
But your eyes have seen all the great works of Yahweh that he did.
8 Saboda haka sai ku kiyaye dukan umarnan da nake ba ku a yau, don ku sami ƙarfin da za ku shiga, ku kuma karɓi ƙasar da kuke haye Urdun ku mallaka,
Therefore keep all the commandments that I am commanding you today, that you may be strong, and go in and possess the land where you are going over to possess it,
9 domin kuma ku yi tsawon rai a ƙasar da Ubangiji ya rantse wa kakanninku zai ba su da zuriyarsu, ƙasa mai zub da madara da zuma.
and that you may prolong your days in the land that Yahweh swore to your fathers to give to them and to their descendants, a land flowing with milk and honey.
10 Ƙasar da kuke shiga, ku karɓa, ba kamar ƙasar Masar ba ce, inda kuka fito, inda kuka shuka iri, ku yi ta zuwa kuna banruwa kamar lambu.
For the land, where you go in to possess it, is not like the land of Egypt, from where you came, where you sowed your seed and watered it with your foot, like a garden of herbs;
11 Amma ƙasar da kuke haye Urdun ku mallaki, ƙasa ce ta duwatsu da kwaruruka wadda ruwan sama ne yake jiƙe ta.
but the land, where you go over to possess it, is a land of hills and valleys, and drinks water of the rain of the heavens,
12 Ƙasa ce da Ubangiji Allahnku yake lura da ita; idanun Ubangiji Allahnku yana a kai daga farkon shekara har zuwa ƙarshenta.
a land that Yahweh your God cares for; the eyes of Yahweh your God are always upon it, from the beginning of the year to the end of the year.
13 Saboda haka in kun yi biyayya ga umarnan da nake ba ku a yau cikin aminci, kuna ƙaunaci Ubangiji Allahnku, kuna kuma bauta masa da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku,
It will happen, if you will listen diligently to my commandments that I command you today, to love Yahweh your God and to serve him with all your heart and with all your soul,
14 sai in aika da ruwan sama a ƙasarku a lokacinsa, ruwan saman bazara da kuma na kaka, don ku tattara hatsinku, sabon inabinku da kuma manku.
that I will give the rain of your land in its season, the former rain and the latter rain, that you may gather in your grain, your new wine, and your oil.
15 Zan tanadar da ciyawa a filaye don shanunku, za ku ci, ku kuma ƙoshi.
I will give grass in your fields for your cattle, and you will eat and be full.
16 Ku yi hankali, kada a ruɗe ku har ku bauta wa alloli, ku kuma yi musu sujada,
Pay attention to yourselves so that your heart is not deceived, and you turn aside and worship other gods and bow down to them;
17 don kada fushin Ubangiji yă ƙuna a kanku, yă rufe sammai, ku rasa ruwa, ƙasa kuma ta kāsa ba da amfaninta, da haka za ku murmutu nan da nan a kyakkyawar ƙasar da Ubangiji yake ba ku.
so that the anger of Yahweh is not kindled against you; and so that he does not shut up the heavens so that there will be no rain, and the land will not yield its fruit, and so that you perish quickly from off the good land that Yahweh is giving you.
18 Saboda haka, sai ku riƙe waɗannan kalmomina gam a zukatanku da ranku; ku ɗaura su kamar alama a hannuwanku, da goshinku.
Therefore lay up these words of mine in your heart and soul, bind them as a sign on your hand, and let them be as frontlets between your eyes.
19 Ku koyar da su ga’ya’yanku, ku yi ta haddace su, sa’ad da kuke zaune a gida, da sa’ad da kuke tafiya, sa’ad da kuke kwance, da sa’ad da kuka tashi.
You will teach them to your children and talk about them when you sit in your house, when you walk on the road, when you lie down, and when you get up.
20 Ku rubuta su a kan madogaran ƙofofin gidajenku, da a kan ƙofofinku,
You will write them on the doorposts of your house and on your city gates,
21 saboda kwanakinku da kwanakin’ya’yanku su yi tsawo a ƙasar da Ubangiji ya rantse zai ba wa kakanninku, muddin sama tana bisa duniya.
that your days and the days of your children may be multiplied in the land that Yahweh swore to your ancestors to give them for as long as the heavens are above the earth.
22 In kuka lura, kuka kuma kiyaye dukan umarnai da nake ba ku, ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku, ku yi tafiya a hanyoyinsa, ku kuma riƙe shi gam,
For if you diligently keep all these commandments that I am commanding you, so as to do them, to love Yahweh your God, to walk in all his ways, and to cling to him,
23 Ubangiji zai kori dukan waɗannan al’ummai a gabanku, za ku kuma kore al’umman da suka fi ku yawa da ƙarfi.
then Yahweh will drive out all these nations from before you, and you will dispossess nations larger and mightier than yourselves.
24 Duk inda tafin ƙafanku ya taka, zai zama naku; iyakarku zai kama daga hamadan Lebanon da kuma daga Kogin Yuferites zuwa Bahar Rum.
Every place where the sole of your foot will tread will be yours; from the wilderness to Lebanon, from the river, the Euphrates River, to the western sea will be your border.
25 Babu mutumin da zai iya tsayayya da ku. Ubangiji Allahnku, zai sa razana da tsoronku a dukan ƙasar, a duk inda kuka tafi, kamar yadda ya alkawarta muku.
No man will be able to stand before you. Yahweh your God will lay the fear of you and the terror of you upon all the land that you tread on, as he has said to you.
26 Ga shi, a yau, ina sa a gabanku albarka da kuma la’ana,
Look, I set before you today a blessing and a curse:
27 albarka in kun yi biyayya da umarnan Ubangiji Allahnku, da nake ba ku;
the blessing, if you obey the commandments of Yahweh your God that I command you today,
28 la’ana in ba ku yi biyayya da umarnan Ubangiji Allahnku, kuka kuma juya daga hanyar da na umarce ku, ta wurin bin waɗansu alloli, waɗanda ba ku sani ba.
and the curse, if you do not obey the commandments of Yahweh your God, but turn aside from the way that I command you today, to go after other gods that you have not known.
29 Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya kawo ku cikin ƙasar da za ku shiga ku ci gādonta, sai ku yi shelar albarkun nan a dutsen Gerizim, ku kuma yi na la’ana a dutsen Ebal.
It will happen, when Yahweh your God brings you into the land which you go to possess, that you will set the blessing on Mount Gerizim, and the curse on Mount Ebal.
30 Waɗannan duwatsu biyu suna a hayin Urdun, yamma da hanya a ƙasar Kan’aniyawa mazaunan Araba, kusa da Gilgal wajajen manyan itatuwan More.
Are they not beyond the Jordan, west of the western road, in the land of the Canaanites who live in the Arabah, over against Gilgal, beside the oaks of Moreh?
31 Kuna gab da ƙetare Urdun fa, ku shiga, ku kuma mallaki ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku. Sa’ad da kuka karɓe ta, kuka kuma zauna a can,
For you are to cross over the Jordan to go in to possess the land that Yahweh your God is giving you, and you will possess it and live in it.
32 ku tabbata kun yi biyayya da dukan ƙa’idodi, da kuma dokokin da nake sawa a gabanku a yau.
You will keep all the statutes and the decrees that I set before you today.