< Maimaitawar Shari’a 11 >

1 To, sai ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku, kullum ku kuma kiyaye abubuwan da yake bukata, ku kiyaye ƙa’idodinsa, dokokinsa da kuma umarnansu.
Therefore shalt thou love Yahweh thy God and keep his observance and his statutes and his regulations and his commandments all the days.
2 Ku tuna a yau, cewa’ya’yanku ba su ne suka gani suka kuma ɗanɗana horon Ubangiji Allahnku ba; ba su suka gani girmansa, hannunsa mai ƙarfi, hannunsa mai iko;
And ye must know to-day, (for not with your sons [do I speak] who know not, neither have they seen) the discipline of Yahweh your God, —his greatness, his firm hand, and his stretched-out arm;
3 alamun da ya aikata da abubuwan da ya yi a cikin Masar, ga Fir’auna sarkin Masar da kuma ga dukan ƙasarsa ba;
and his signs and his doings, which he did in the midst of Egypt, —unto Pharaoh king of Egypt and unto all his land;
4 ba su suka gani abin da ya yi wa mayaƙan Masar, da dawakansu da keken yaƙinsu, yadda ya sha kansu da ruwan Jan Teku yayinda suke bin ku, da yadda Ubangiji ya hallaka su ƙaƙaf ba.
and what he did unto the forces of Egypt—unto his horses and unto his chariots in that he caused the waters of the Red Sea to flow over their faces, when they were pursuing after you, —and so Yahweh destroyed them (unto this day);
5 Ba’ya’yanku ba ne suka gani abin da ya yi dominku a hamada har sai da kuka kai wannan wuri ba,
and what he did unto you, in the desert, —until ye came in as far as this place;
6 ba su ba ne suka gani abin da ya yi ga Datan da Abiram,’ya’yan Eliyab mutumin Ruben, sa’ad da ƙasa ta buɗe bakinta a tsakiyar dukan Isra’ila ta haɗiye su tare da gidajensu, tentunansu da kowane abu mai rai da yake nasu ba.
and what he did to Dathan and to Abiram, sons of Eliab, son of Reuben, in that the earth opened wide her mouth, and swallowed-up them and their households and their tents, —and all the living things that attended them, in the midst of all Israel.
7 Amma idanunku ne suka ga dukan waɗannan manyan abubuwan da Ubangiji ya yi.
For yours, are the eyes that have seen every great deed of Yahweh, —which he hath done.
8 Saboda haka sai ku kiyaye dukan umarnan da nake ba ku a yau, don ku sami ƙarfin da za ku shiga, ku kuma karɓi ƙasar da kuke haye Urdun ku mallaka,
Therefore shall ye keep all the commandment which I am commanding thee, today, —that ye may be strong, and so enter and possess the land, whither ye are passing over to possess it;
9 domin kuma ku yi tsawon rai a ƙasar da Ubangiji ya rantse wa kakanninku zai ba su da zuriyarsu, ƙasa mai zub da madara da zuma.
and that ye may prolong your days upon the soil which Yahweh sware unto your fathers, to give unto them and unto their seed, —a land flowing with milk and honey.
10 Ƙasar da kuke shiga, ku karɓa, ba kamar ƙasar Masar ba ce, inda kuka fito, inda kuka shuka iri, ku yi ta zuwa kuna banruwa kamar lambu.
For the land which thou art entering to, possess, not like the land of Egypt, it is, from whence ye came out, —where thou didst sow thy seed, and then water it with thy foot, like a garden of herbs;
11 Amma ƙasar da kuke haye Urdun ku mallaki, ƙasa ce ta duwatsu da kwaruruka wadda ruwan sama ne yake jiƙe ta.
but the land whereinto ye are passing over to, possess it, is a land of hills, and valleys, —which of the rain of the heavens, doth drink water:
12 Ƙasa ce da Ubangiji Allahnku yake lura da ita; idanun Ubangiji Allahnku yana a kai daga farkon shekara har zuwa ƙarshenta.
a land which Yahweh thy God careth for, —continually are the eyes of Yahweh thy God upon it, from the beginning of the year, even unto the end of the year.
13 Saboda haka in kun yi biyayya ga umarnan da nake ba ku a yau cikin aminci, kuna ƙaunaci Ubangiji Allahnku, kuna kuma bauta masa da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku,
And it shall come to pass, if ye will hearken, unto my commandments, which, I am commanding you to-day, —to love Yahweh your God, and to serve him, with, all your heart, and with all your soul,
14 sai in aika da ruwan sama a ƙasarku a lokacinsa, ruwan saman bazara da kuma na kaka, don ku tattara hatsinku, sabon inabinku da kuma manku.
then [saith he] I will give the rain of your land in its season, the early rain and the latter rain; so shalt thou gather in thy corn, and thy new wine and thine oil;
15 Zan tanadar da ciyawa a filaye don shanunku, za ku ci, ku kuma ƙoshi.
and I will give grass in thy field for thy cattle, —and thou shalt eat and be satisfied.
16 Ku yi hankali, kada a ruɗe ku har ku bauta wa alloli, ku kuma yi musu sujada,
Take heed to yourselves, lest your heart be befooled, —and ye turn aside and serve other gods, and bow down to them.
17 don kada fushin Ubangiji yă ƙuna a kanku, yă rufe sammai, ku rasa ruwa, ƙasa kuma ta kāsa ba da amfaninta, da haka za ku murmutu nan da nan a kyakkyawar ƙasar da Ubangiji yake ba ku.
So would the anger of Yahweh kindle upon you and he would shut up the heavens, that there should be no rain, and the ground, would not yield her increase, —so should ye perish speedily, from off the good land, which Yahweh is giving unto you.
18 Saboda haka, sai ku riƙe waɗannan kalmomina gam a zukatanku da ranku; ku ɗaura su kamar alama a hannuwanku, da goshinku.
Therefore shall ye lay these my words upon your heart, and upon your soul, —and bind them for a sign upon your hand, and they shall serve as bands between your eyes;
19 Ku koyar da su ga’ya’yanku, ku yi ta haddace su, sa’ad da kuke zaune a gida, da sa’ad da kuke tafiya, sa’ad da kuke kwance, da sa’ad da kuka tashi.
and ye shall teach them unto your children by speaking of them, —when thou sittest in thy house, and when thou walkest by the way, and when thou liest down and when thou risest up;
20 Ku rubuta su a kan madogaran ƙofofin gidajenku, da a kan ƙofofinku,
and thou shalt write them upon the door-posts of thy house and within thy gates:
21 saboda kwanakinku da kwanakin’ya’yanku su yi tsawo a ƙasar da Ubangiji ya rantse zai ba wa kakanninku, muddin sama tana bisa duniya.
that your days may multiply, and the days of your children, upon the soil which Yahweh sware unto your fathers, to give unto them, —like the days of the heavens upon the earth.
22 In kuka lura, kuka kuma kiyaye dukan umarnai da nake ba ku, ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku, ku yi tafiya a hanyoyinsa, ku kuma riƙe shi gam,
For if ye do, indeed keep, all this commandment which I am commanding you to do it, —to love Yahweh your God, to Walk in all his ways, and to cleave unto him,
23 Ubangiji zai kori dukan waɗannan al’ummai a gabanku, za ku kuma kore al’umman da suka fi ku yawa da ƙarfi.
then will Yahweh dispossess all these nations, from before you, —and ye shall dispossess nations greater and stronger than ye:
24 Duk inda tafin ƙafanku ya taka, zai zama naku; iyakarku zai kama daga hamadan Lebanon da kuma daga Kogin Yuferites zuwa Bahar Rum.
every place whereon the sole of your foot shall tread yours, shall it be, —from the desert and the Lebanon from the river—the river Euphrates, even unto the hinder sea, shall be your boundary.
25 Babu mutumin da zai iya tsayayya da ku. Ubangiji Allahnku, zai sa razana da tsoronku a dukan ƙasar, a duk inda kuka tafi, kamar yadda ya alkawarta muku.
No man shall stand before you, —the dread of you and the fear of you, will Yahweh your God put forth over the face of all the land whereon ye shall tread, as he spake unto you.
26 Ga shi, a yau, ina sa a gabanku albarka da kuma la’ana,
See! I am setting before you to-day, —a blessing, and a curse:
27 albarka in kun yi biyayya da umarnan Ubangiji Allahnku, da nake ba ku;
the blessing, when ye shall hearken unto the commandments of Yahweh your God, which I am commanding you to-day;
28 la’ana in ba ku yi biyayya da umarnan Ubangiji Allahnku, kuka kuma juya daga hanyar da na umarce ku, ta wurin bin waɗansu alloli, waɗanda ba ku sani ba.
and the curse if ye, shall not hearken unto the commandments of Yahweh your God, but shall turn aside out of the way which I am commanding you to-day, —to go after other gods which ye know not.
29 Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya kawo ku cikin ƙasar da za ku shiga ku ci gādonta, sai ku yi shelar albarkun nan a dutsen Gerizim, ku kuma yi na la’ana a dutsen Ebal.
And it shall come to pass when Yahweh thy God shall bring thee into the land which thou art entering to possess, then shalt thou put the blessing, upon Mount Gerizim, and the curse, upon Mount Ebal.
30 Waɗannan duwatsu biyu suna a hayin Urdun, yamma da hanya a ƙasar Kan’aniyawa mazaunan Araba, kusa da Gilgal wajajen manyan itatuwan More.
Are, they, not over the Jordan on the way towards the entering in of the sun, in the land of the Canaanite who dwelleth in the plain over against Gilgal beside the Teacher’s Terebinths?
31 Kuna gab da ƙetare Urdun fa, ku shiga, ku kuma mallaki ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku. Sa’ad da kuka karɓe ta, kuka kuma zauna a can,
For ye are passing over the Jordan, to enter to possess the land which Yahweh your God, is giving unto you, —so shall ye possess it and dwell therein.
32 ku tabbata kun yi biyayya da dukan ƙa’idodi, da kuma dokokin da nake sawa a gabanku a yau.
Therefore shall ye observe to do all the statutes and the regulations, —which I am setting before you to-day.

< Maimaitawar Shari’a 11 >