< Maimaitawar Shari’a 11 >

1 To, sai ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku, kullum ku kuma kiyaye abubuwan da yake bukata, ku kiyaye ƙa’idodinsa, dokokinsa da kuma umarnansu.
Saa elsk da HERREN din Gud og hold hans Forskrifter, hans Anordninger, Lovbud og Bud alle Dage:
2 Ku tuna a yau, cewa’ya’yanku ba su ne suka gani suka kuma ɗanɗana horon Ubangiji Allahnku ba; ba su suka gani girmansa, hannunsa mai ƙarfi, hannunsa mai iko;
jeg taler ikke til eders Børn, der ikke har oplevet det og set det; betænk derfor i Dag HERREN eders Guds Optugtelse, hans Storhed, hans stærke Haand og udstrakte Arm,
3 alamun da ya aikata da abubuwan da ya yi a cikin Masar, ga Fir’auna sarkin Masar da kuma ga dukan ƙasarsa ba;
hans Tegn og Gerninger, som han gjorde midt i Ægypten mod Farao, Ægypterkongen, og hele hans Land,
4 ba su suka gani abin da ya yi wa mayaƙan Masar, da dawakansu da keken yaƙinsu, yadda ya sha kansu da ruwan Jan Teku yayinda suke bin ku, da yadda Ubangiji ya hallaka su ƙaƙaf ba.
og hvad han gjorde ved Ægypternes Hærmagt, deres Heste og Vogne, som han, da de forfulgte eder, lod det røde Havs Vande skylle hen over og tilintetgjorde for stedse,
5 Ba’ya’yanku ba ne suka gani abin da ya yi dominku a hamada har sai da kuka kai wannan wuri ba,
og hvad han gjorde for eder i Ørkenen, lige til I kom til Stedet her,
6 ba su ba ne suka gani abin da ya yi ga Datan da Abiram,’ya’yan Eliyab mutumin Ruben, sa’ad da ƙasa ta buɗe bakinta a tsakiyar dukan Isra’ila ta haɗiye su tare da gidajensu, tentunansu da kowane abu mai rai da yake nasu ba.
og hvad han gjorde ved Datan og Abiram, Rubens Søn Eliabs Sønner, hvorledes Jorden aabnede sin Mund og slugte dem tillige med deres Huse og Telte og alt, hvad der var i Ledtog med dem, midt iblandt hele Israel!
7 Amma idanunku ne suka ga dukan waɗannan manyan abubuwan da Ubangiji ya yi.
Thi med egne Øjne har I set al den Stordaad, HERREN har øvet!
8 Saboda haka sai ku kiyaye dukan umarnan da nake ba ku a yau, don ku sami ƙarfin da za ku shiga, ku kuma karɓi ƙasar da kuke haye Urdun ku mallaka,
Saa hold da alle de Bud, jeg i Dag paalægger dig, for at I kan vinde Styrke og komme og tage det Land i Besiddelse, som I skal over og tage i Besiddelse,
9 domin kuma ku yi tsawon rai a ƙasar da Ubangiji ya rantse wa kakanninku zai ba su da zuriyarsu, ƙasa mai zub da madara da zuma.
og for at I kan faa et langt Liv paa den Jord, HERREN tilsvor eders Fædre at ville give dem og deres Afkom, et Land, der flyder med Mælk og Honning.
10 Ƙasar da kuke shiga, ku karɓa, ba kamar ƙasar Masar ba ce, inda kuka fito, inda kuka shuka iri, ku yi ta zuwa kuna banruwa kamar lambu.
Thi det Land, du skal ind og tage i Besiddelse, er ikke som Ægypten, hvorfra I drog ud! Naar du der havde saaet din Sæd, maatte du vande Landet med din Fod, som en Urtehave;
11 Amma ƙasar da kuke haye Urdun ku mallaki, ƙasa ce ta duwatsu da kwaruruka wadda ruwan sama ne yake jiƙe ta.
nej, det Land, I skal over og tage i Besiddelse, er et Land med Bjerge og Dale, der drikker Vand, naar Regnen falder fra Himmelen,
12 Ƙasa ce da Ubangiji Allahnku yake lura da ita; idanun Ubangiji Allahnku yana a kai daga farkon shekara har zuwa ƙarshenta.
et Land, som HERREN din Gud har Omhu for, og som HERREN din Guds Øjne stadig hviler paa, fra Aarets Begyndelse og til dets Slutning.
13 Saboda haka in kun yi biyayya ga umarnan da nake ba ku a yau cikin aminci, kuna ƙaunaci Ubangiji Allahnku, kuna kuma bauta masa da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku,
Og hvis I nu lyder mine Bud, som jeg i Dag paalægger eder, saa I elsker HERREN eders Gud og tjener ham af hele eders Hjerte og hele eders Sjæl,
14 sai in aika da ruwan sama a ƙasarku a lokacinsa, ruwan saman bazara da kuma na kaka, don ku tattara hatsinku, sabon inabinku da kuma manku.
saa vil jeg give eders Land dets Regn i rette Tid, baade Tidligregn og Sildigregn, saa du kan høste dit Korn, din Most og din Olie;
15 Zan tanadar da ciyawa a filaye don shanunku, za ku ci, ku kuma ƙoshi.
og jeg vil give Græs paa din Mark til dit Kvæg; og du skal spise dig mæt.
16 Ku yi hankali, kada a ruɗe ku har ku bauta wa alloli, ku kuma yi musu sujada,
Men vogt eder, at ikke eders Hjerte daares, saa I falder fra og dyrker andre Guder og tilbeder dem;
17 don kada fushin Ubangiji yă ƙuna a kanku, yă rufe sammai, ku rasa ruwa, ƙasa kuma ta kāsa ba da amfaninta, da haka za ku murmutu nan da nan a kyakkyawar ƙasar da Ubangiji yake ba ku.
thi da vil HERRENS Vrede blusse op imod eder, og han vil lukke Himmelen, saa der ikke falder Regn, og Jorden ikke giver Grøde, og I skal hurtigt udryddes af det herlige Land, HERREN vil give eder.
18 Saboda haka, sai ku riƙe waɗannan kalmomina gam a zukatanku da ranku; ku ɗaura su kamar alama a hannuwanku, da goshinku.
I skal lægge eder disse mine Ord paa Hjerte og Sinde, binde dem som et Tegn om eders Haand og lade dem være et Erindringsmærke paa eders Pande,
19 Ku koyar da su ga’ya’yanku, ku yi ta haddace su, sa’ad da kuke zaune a gida, da sa’ad da kuke tafiya, sa’ad da kuke kwance, da sa’ad da kuka tashi.
og I skal lære eders Børn dem, idet I taler om dem, baade naar du sidder i dit Hus, og naar du vandrer paa Vejen, baade naar du lægger dig, og naar du staar op.
20 Ku rubuta su a kan madogaran ƙofofin gidajenku, da a kan ƙofofinku,
Og du skal skrive dem paa Dørstolperne af dit Hus og paa dine Porte,
21 saboda kwanakinku da kwanakin’ya’yanku su yi tsawo a ƙasar da Ubangiji ya rantse zai ba wa kakanninku, muddin sama tana bisa duniya.
for at I og eders Børn maa leve i det Land, HERREN tilsvor eders Fædre at ville give dem, saa længe Himmelen er over Jorden.
22 In kuka lura, kuka kuma kiyaye dukan umarnai da nake ba ku, ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku, ku yi tafiya a hanyoyinsa, ku kuma riƙe shi gam,
Thi hvis I vogter vel paa alle disse Bud, som jeg i Dag paalægger eder at holde, saa I elsker HERREN eders Gud og vandrer paa alle hans Veje og hænger fast ved ham,
23 Ubangiji zai kori dukan waɗannan al’ummai a gabanku, za ku kuma kore al’umman da suka fi ku yawa da ƙarfi.
saa skal HERREN drive alle disse Folk bort foran eder, og I skal underlægge eder Folk, der er større og mægtigere end I.
24 Duk inda tafin ƙafanku ya taka, zai zama naku; iyakarku zai kama daga hamadan Lebanon da kuma daga Kogin Yuferites zuwa Bahar Rum.
Hver Plet, eders Fodsaal betræder, skal tilhøre eder; fra Ørkenen til Libanon og fra den store Flod, Eufratfloden, til Havet i Vest skal eders Landemærker strække sig.
25 Babu mutumin da zai iya tsayayya da ku. Ubangiji Allahnku, zai sa razana da tsoronku a dukan ƙasar, a duk inda kuka tafi, kamar yadda ya alkawarta muku.
Ingen skal kunne holde Stand for eder; Skræk og Rædsel for eder skal HERREN eders Gud lade komme over hele det Land, I betræder, saaledes som han lovede eder.
26 Ga shi, a yau, ina sa a gabanku albarka da kuma la’ana,
Se, jeg forelægger eder i Dag Velsignelse og Forbandelse,
27 albarka in kun yi biyayya da umarnan Ubangiji Allahnku, da nake ba ku;
Velsignelsen, hvis I lyder HERREN eders Guds Bud, som jeg i Dag paalægger eder,
28 la’ana in ba ku yi biyayya da umarnan Ubangiji Allahnku, kuka kuma juya daga hanyar da na umarce ku, ta wurin bin waɗansu alloli, waɗanda ba ku sani ba.
og Forbandelsen, hvis I ikke lyder HERREN eders Guds Bud, men viger bort fra den Vej, jeg i Dag foreskriver eder, for at holde eder til andre Guder, I ikke før kendte til.
29 Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya kawo ku cikin ƙasar da za ku shiga ku ci gādonta, sai ku yi shelar albarkun nan a dutsen Gerizim, ku kuma yi na la’ana a dutsen Ebal.
Og naar HERREN din Gud fører dig ind i det Land, du skal ind og tage i Besiddelse, saa skal du lægge Velsignelsen paa Garizims Bjerg og Forbandelsen paa Ebals Bjerg.
30 Waɗannan duwatsu biyu suna a hayin Urdun, yamma da hanya a ƙasar Kan’aniyawa mazaunan Araba, kusa da Gilgal wajajen manyan itatuwan More.
De ligger jo hinsides Jordan, bag ved den, mod Vest, i de Kana'anæeres Land, der bor i Arabalavningen, lige over for Gilgal ved Sandsigerens Træ.
31 Kuna gab da ƙetare Urdun fa, ku shiga, ku kuma mallaki ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku. Sa’ad da kuka karɓe ta, kuka kuma zauna a can,
Thi I staar jo nu i Begreb med at overskride Jordan for at gaa ind og tage det Land i Besiddelse, som HERREN eders Gud vil give eder. Naar I da har taget det i Besiddelse og bosat eder der,
32 ku tabbata kun yi biyayya da dukan ƙa’idodi, da kuma dokokin da nake sawa a gabanku a yau.
skal I omhyggeligt handle efter alle de Anordninger og Lovbud, jeg i Dag forelægger eder!

< Maimaitawar Shari’a 11 >