< Maimaitawar Shari’a 10 >

1 A lokacin Ubangiji ya ce mini, “Ka sassaƙa alluna biyu na dutse kamar na farko, ka haura wurina a kan dutse. Ka kuma yi akwatin katako.
Ob tistem času mi je Gospod rekel: ›Izsekaj si dve kamniti plošči, podobni prvima in pridi gor k meni na goro in si naredi skrinjo iz lesa.
2 Ni kuwa zan yi rubutu a kan allunan nan biyu, kalmomin da suke a alluna na farko, waɗanda ka farfashe. Za a ajiye su a cikin akwatin.”
Na tabli bom zapisal besede, ki so bile na prvih tablah, ki si ju razbil in položil ju boš v skrinjo.‹
3 Sai na yi akwatin da itacen ƙirya, na kuma sassaƙa alluna biyu na dutse kamar na farko, sai na haura dutse da alluna biyun a hannuwana.
In naredil sem skrinjo iz akacijevega lesa in izsekal dve kamniti plošči, podobni prvima in odšel gor na goro in v svoji roki sem imel dve tabli.
4 Ubangiji kuwa ya sāke yin rubutu a waɗannan alluna abin da ya rubuta a allunan farko, wato, Dokoki Goma da ya furta a kan dutse a tsakiyar wuta, a ranar da mutane suka taru. Sai Ubangiji ya ba ni su.
Na tabli je zapisal deset zapovedi, glede na prvo pisanje, ki vam jih je Gospod govoril na gori iz srede ognja na dan zbora. In Gospod mi ju je dal.
5 Sa’an nan na sauko daga dutsen, na kuma ajiye allunan a cikin akwatin da na yi, yadda Ubangiji ya umarce ni, kuma suna can a yanzu.
Obrnil sem se in prišel dol z gore in tabli položil v skrinjo, ki sem jo naredil, in tam sta, kakor mi je Gospod zapovedal.
6 (Isra’ilawa suka kama hanya daga rijiyoyin Beyerot Bene Ya’akan zuwa Mosera. A can Haruna ya rasu, aka kuma binne shi. Sai Eleyazar ɗansa ya gāje shi a matsayin firist.
Izraelovi otroci so odšli na svoje potovanje od Beeróta Jaakánovih otrok v Mosêro. Tam je Aron umrl in tam je bil pokopan in namesto njega je v duhovniški službi služil njegov sin Eleazar.
7 Daga can suka tashi zuwa Gudgoda, daga Gudgoda kuma suka tafi Yotbata, ƙasa mai rafuffukan ruwa.
Od tam so odpotovali v Gidgád in iz Gidgáda v Jotbáto, deželo rek vodá.
8 A lokacin Ubangiji ya keɓe kabilar Lawi don su riƙa ɗaukar akwatin alkawarin Ubangiji, su tsaya a gaban Ubangiji, su riƙa yin masa hidima, su kuma sa albarka a cikin sunansa, yadda suke yi har wa yau.
Ob tistem času je Gospod ločil Lévijev rod, da nosi skrinjo Gospodove zaveze, da stojijo pred Gospodom, da mu služijo in da blagoslavljajo v njegovem imenu, do današnjega dne.
9 Shi ya sa Lawiyawa ba su da rabo, ko gādo a cikin’yan’uwansu; Ubangiji ne gādonsu yadda Ubangiji Allahnku ya faɗa musu.)
Zato Levi nima deleža niti dediščine s svojimi brati; Gospod je njegova dediščina, kakor mu je obljubil Gospod, tvoj Bog.
10 To, na kasance a kan dutse yini arba’in da dare arba’in kamar yadda dā na yi da farko. Ubangiji kuwa ya saurare ni a wannan lokaci kuma. Ba nufinsa ba ne yă hallaka ku.
In ostal sem na gori, kakor prvič, štirideset dni in štirideset noči in Gospod mi je prisluhnil tudi ob tistem času in Gospod te ni hotel uničiti.
11 Ubangiji ya ce mini, “Ka sauka, ka jagoranci mutanen a hanyarsu, domin su shiga, su kuma mallaki ƙasar da na rantse wa kakanninsu, zan ba su.”
Gospod mi je rekel: ›Vstani, odpravi se na svoje potovanje pred ljudstvom, da lahko vstopijo in vzamejo v last deželo, ki sem jo prisegel njihovim očetom, da jim jo dam.‹
12 Yanzu fa, ya Isra’ila, mene ne Ubangiji Allahnku yake so a gare ku, in ba ku ji tsoron Ubangiji Allahnku, ku yi tafiya cikin hanyoyinsa, ku ƙaunace shi, ku bauta wa Ubangiji Allahnku da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku,
In sedaj, Izrael, kaj Gospod, tvoj Bog, zahteva od tebe, razen, da se bojiš Gospoda, svojega Boga, da hodiš po vseh njegovih poteh, da ga ljubiš, da služiš Gospodu, svojemu Bogu, z vsem svojim srcem in z vso svojo dušo.
13 ku kuma kiyaye umarnan Ubangiji da kuma ƙa’idodinsa da nake ba ku a yau don amfaninku ba?
Da varuješ Gospodove zapovedi in njegove zakone, ki ti jih ta dan zapovedujem v tvoje dobro?
14 Sammai, har da sama sammai, da duniya, da kome da yake cikinta na Ubangiji Allahnku ne.
Glej, nebo in nebesa nebes so od Gospoda, tvojega Boga, tudi zemlja z vsem, kar je na njej.
15 Duk da haka Ubangiji ya ƙaunaci kakanninku, ya kuma zaɓe ku, ku zuriyarsu, a bisa dukan al’ummai, yadda yake a yau.
Samo Gospod je imel zadovoljstvo v tvojih očetih, da jih vzljubi in izbral je njihovo seme za njimi, torej vas, izmed vseh ljudstev, kakor je to ta dan.
16 Saboda haka sai ku kame zukatanku, kada ku ƙara yin taurinkai.
Obrežite torej prednjo kožico svojega srca in ne bodite več trdovratni.
17 Gama Ubangiji Allahnku ne Allahn alloli da Ubangijin iyayengiji, Allah mai girma, mai ƙarfi da kuma mai banrazana, wanda ba ya sonkai, ba ya cin hanci.
Kajti Gospod, vaš Bog, je Bog bogov in Gospod gospodov in véliki Bog, mogočen in strašen, ki se ne ozira na osebe niti ne sprejema nagrade.
18 Yakan tsare marayu da gwauraye, yana ƙaunar baƙon da yake zama a cikinku, yana ba su abinci da tufafi.
Izvaja sodbo sirote in vdove in ljubi tujca v tem, da mu daje hrano in oblačilo.
19 Sai ku ƙaunaci baƙi, gama dā ku ma baƙi ne a ƙasar Masar.
Ljubite torej tujca, kajti tujci ste bili v egiptovski deželi.
20 Ku ji tsoron Ubangiji Allahnku, ku kuma bauta masa. Ku manne masa, ku kuma yi rantsuwarku da sunansa.
Bal se boš Gospoda, svojega Boga. Njemu boš služil in k njemu se boš trdno pridružil in prisegal pri njegovem imenu.
21 Shi ne abin yabonku; shi ne Allahnku, wanda ya aikata muku waɗancan manya abubuwa banmamaki masu banrazanar da kuka gani da idanunku.
On je tvoja hvala in on je tvoj Bog, ki je zate storil te velike in strašne stvari, ki so jih videle tvoje oči.
22 Kakanninku da suka gangara zuwa Masar, su saba’in ne, yanzu kuwa Ubangiji Allahnku ya sa kuka ƙaru, kuka zama kamar taurari a sama.
Tvoji očetje so odšli dol v Egipt s sedemdesetimi osebami in sedaj te je Gospod, tvoj Bog, naredil kakor zvezd neba zaradi množice.

< Maimaitawar Shari’a 10 >