< Maimaitawar Shari’a 10 >
1 A lokacin Ubangiji ya ce mini, “Ka sassaƙa alluna biyu na dutse kamar na farko, ka haura wurina a kan dutse. Ka kuma yi akwatin katako.
En ce temps-là le Seigneur me dit: Taille-toi deux tables de pierre, comme les premières étaient, et monte vers moi sur la montagne, et tu feras une arche de bois,
2 Ni kuwa zan yi rubutu a kan allunan nan biyu, kalmomin da suke a alluna na farko, waɗanda ka farfashe. Za a ajiye su a cikin akwatin.”
Et j’écrirai sur ces tables les paroles qui étaient sur celles que tu as déjà brisées, et tu les placeras dans l’arche.
3 Sai na yi akwatin da itacen ƙirya, na kuma sassaƙa alluna biyu na dutse kamar na farko, sai na haura dutse da alluna biyun a hannuwana.
Je fis donc une arche de bois de sétim. Et lorsque j’eus taillé deux tables de pierre comme les premières, je montai sur la montagne, les ayant en mes mains.
4 Ubangiji kuwa ya sāke yin rubutu a waɗannan alluna abin da ya rubuta a allunan farko, wato, Dokoki Goma da ya furta a kan dutse a tsakiyar wuta, a ranar da mutane suka taru. Sai Ubangiji ya ba ni su.
Et le Seigneur écrivit sur ces tables, selon ce qu’il avait d’abord écrit, les dix paroles qu’il vous adressa sur la montagne, du milieu du feu, quand le peuple était assemblé, et il me les donna.
5 Sa’an nan na sauko daga dutsen, na kuma ajiye allunan a cikin akwatin da na yi, yadda Ubangiji ya umarce ni, kuma suna can a yanzu.
Et revenu de la montagne, je descendis, et je plaçai les tables dans l’arche que j’avais faite; et elles y sont demeurées jusqu’ici, comme le Seigneur m’a commandé.
6 (Isra’ilawa suka kama hanya daga rijiyoyin Beyerot Bene Ya’akan zuwa Mosera. A can Haruna ya rasu, aka kuma binne shi. Sai Eleyazar ɗansa ya gāje shi a matsayin firist.
Or les enfants d’Israël transportèrent leur camp de Béroth des enfants de Jacan à Moséra, où mourut et fut enseveli Aaron, à la place duquel Eléazar, son fils, exerça les fonctions du sacerdoce.
7 Daga can suka tashi zuwa Gudgoda, daga Gudgoda kuma suka tafi Yotbata, ƙasa mai rafuffukan ruwa.
De là ils vinrent à Gadgad, et partis de ce lieu, ils campèrent à Jétébatha, terre d’eaux et de torrents.
8 A lokacin Ubangiji ya keɓe kabilar Lawi don su riƙa ɗaukar akwatin alkawarin Ubangiji, su tsaya a gaban Ubangiji, su riƙa yin masa hidima, su kuma sa albarka a cikin sunansa, yadda suke yi har wa yau.
En ce temps-là, le Seigneur sépara la tribu de Lévi, afin qu’elle portât l’arche d’alliance du Seigneur, qu’elle se tînt devant lui pour son ministère, et qu’elle bénît en son nom, comme elle a fait jusqu’au présent jour.
9 Shi ya sa Lawiyawa ba su da rabo, ko gādo a cikin’yan’uwansu; Ubangiji ne gādonsu yadda Ubangiji Allahnku ya faɗa musu.)
À cause de cela Lévi n’a pas eu de part, ni de possession avec ses frères, parce que le Seigneur lui-même est sa possession, comme lui a promis le Seigneur ton Dieu.
10 To, na kasance a kan dutse yini arba’in da dare arba’in kamar yadda dā na yi da farko. Ubangiji kuwa ya saurare ni a wannan lokaci kuma. Ba nufinsa ba ne yă hallaka ku.
Pour moi, je me tins sur la montagne comme auparavant, quarante jours et quarante nuits; et le Seigneur m’exauça encore cette fois, et il ne voulut pas te perdre.
11 Ubangiji ya ce mini, “Ka sauka, ka jagoranci mutanen a hanyarsu, domin su shiga, su kuma mallaki ƙasar da na rantse wa kakanninsu, zan ba su.”
Il me dit ensuite: Va, et précède le peuple, afin qu’il entre, et qu’il possède la terre que j’ai juré à ses pères de leur donner.
12 Yanzu fa, ya Isra’ila, mene ne Ubangiji Allahnku yake so a gare ku, in ba ku ji tsoron Ubangiji Allahnku, ku yi tafiya cikin hanyoyinsa, ku ƙaunace shi, ku bauta wa Ubangiji Allahnku da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku,
Et maintenant, Israël, qu’est-ce que le Seigneur ton Dieu demande de toi, si ce n’est que tu craignes le Seigneur ton Dieu, que tu marches dans ses voies, que tu l’aimes, que tu serves le Seigneur ton Dieu en tout ton cœur et en toute ton âme;
13 ku kuma kiyaye umarnan Ubangiji da kuma ƙa’idodinsa da nake ba ku a yau don amfaninku ba?
Et que tu gardes les commandements du Seigneur et ses cérémonies, que moi, je te prescris aujourd’hui, afin que bien t’arrive?
14 Sammai, har da sama sammai, da duniya, da kome da yake cikinta na Ubangiji Allahnku ne.
Voici, au Seigneur ton Dieu est le ciel, et le ciel du ciel, et la terre et tout ce qui est sur elle.
15 Duk da haka Ubangiji ya ƙaunaci kakanninku, ya kuma zaɓe ku, ku zuriyarsu, a bisa dukan al’ummai, yadda yake a yau.
Et cependant le Seigneur s’est uni étroitement à tes pères, il les a aimés, et il a choisi leur postérité après eux, c’est-à-dire, vous, d’entre toutes les nations, comme il est entièrement prouvé aujourd’hui.
16 Saboda haka sai ku kame zukatanku, kada ku ƙara yin taurinkai.
Opérez donc la circoncision de votre cœur, et ne rendez plus votre cou inflexible,
17 Gama Ubangiji Allahnku ne Allahn alloli da Ubangijin iyayengiji, Allah mai girma, mai ƙarfi da kuma mai banrazana, wanda ba ya sonkai, ba ya cin hanci.
Parce que le Seigneur votre Dieu est lui-même le Dieu des dieux et le Seigneur des seigneurs, le Dieu grand, puissant et terrible, qui n’a point égard à la personne, ni aux présents.
18 Yakan tsare marayu da gwauraye, yana ƙaunar baƙon da yake zama a cikinku, yana ba su abinci da tufafi.
Il fait justice à l’orphelin et à la veuve, il aime l’étranger, et il lui donne la nourriture et le vêtement.
19 Sai ku ƙaunaci baƙi, gama dā ku ma baƙi ne a ƙasar Masar.
Vous donc aussi, aimez les étrangers, parce que vous-mêmes aussi, vous avez été étrangers dans la terre d’Egypte.
20 Ku ji tsoron Ubangiji Allahnku, ku kuma bauta masa. Ku manne masa, ku kuma yi rantsuwarku da sunansa.
Tu craindras le Seigneur ton Dieu, et tu le serviras lui seul; tu t’attacheras à lui, et tu jureras par son nom.
21 Shi ne abin yabonku; shi ne Allahnku, wanda ya aikata muku waɗancan manya abubuwa banmamaki masu banrazanar da kuka gani da idanunku.
C’est lui-même qui est ta gloire et ton Dieu; lui qui a fait pour toi ces merveilles grandes et terribles qu’ont vues tes yeux.
22 Kakanninku da suka gangara zuwa Masar, su saba’in ne, yanzu kuwa Ubangiji Allahnku ya sa kuka ƙaru, kuka zama kamar taurari a sama.
C’est au nombre de soixante dix âmes que tes pères sont descendus en Egypte, et voilà que maintenant le Seigneur ton Dieu t’a multiplié comme les astres du ciel.