< Maimaitawar Shari’a 10 >

1 A lokacin Ubangiji ya ce mini, “Ka sassaƙa alluna biyu na dutse kamar na farko, ka haura wurina a kan dutse. Ka kuma yi akwatin katako.
Dans ce même temps l'Éternel me dit: Taille-toi deux Tables de pierre, comme les premières, et monte vers moi sur la montagne et fais-toi une Arche de bois,
2 Ni kuwa zan yi rubutu a kan allunan nan biyu, kalmomin da suke a alluna na farko, waɗanda ka farfashe. Za a ajiye su a cikin akwatin.”
et j'écrirai sur les Tables les Paroles qui se trouvaient sur les premières Tables que tu as brisées, et tu les placeras dans l'Arche.
3 Sai na yi akwatin da itacen ƙirya, na kuma sassaƙa alluna biyu na dutse kamar na farko, sai na haura dutse da alluna biyun a hannuwana.
Je fis donc une Arche de bois d'acacia et taillai deux Tables de pierre pareilles aux premières, et je montai à la montagne ayant les deux Tables dans ma main.
4 Ubangiji kuwa ya sāke yin rubutu a waɗannan alluna abin da ya rubuta a allunan farko, wato, Dokoki Goma da ya furta a kan dutse a tsakiyar wuta, a ranar da mutane suka taru. Sai Ubangiji ya ba ni su.
Alors Il écrivit sur les Tables les mêmes choses qui avaient été écrites sur les premières, les Dix Paroles que l'Éternel vous avait adressées sur la montagne du milieu du feu le jour de l'Assemblée; et l'Éternel me les donna.
5 Sa’an nan na sauko daga dutsen, na kuma ajiye allunan a cikin akwatin da na yi, yadda Ubangiji ya umarce ni, kuma suna can a yanzu.
Et me retournant je descendis de la montagne et je mis les Tables dans l'Arche que j'avais faite, et elles y furent, comme l'Éternel me l'avait commandé.
6 (Isra’ilawa suka kama hanya daga rijiyoyin Beyerot Bene Ya’akan zuwa Mosera. A can Haruna ya rasu, aka kuma binne shi. Sai Eleyazar ɗansa ya gāje shi a matsayin firist.
Et les enfants d'Israël partirent de Beeroth Benei-Jaakan pour Moser. Là mourut Aaron, et il y reçut la sépulture, et Eléazar, son fils, lui succéda dans le sacerdoce.
7 Daga can suka tashi zuwa Gudgoda, daga Gudgoda kuma suka tafi Yotbata, ƙasa mai rafuffukan ruwa.
De là ils se portèrent à Gudgoda, et de Gudgoda à Jotbath, pays de cours d'eaux.
8 A lokacin Ubangiji ya keɓe kabilar Lawi don su riƙa ɗaukar akwatin alkawarin Ubangiji, su tsaya a gaban Ubangiji, su riƙa yin masa hidima, su kuma sa albarka a cikin sunansa, yadda suke yi har wa yau.
C'est dans ce temps-là que l'Éternel mit à part la Tribu de Lévi, pour porter l'Arche de l'Alliance de l'Éternel, et se tenir devant l'Éternel pour le servir, et pour bénir en son nom, jusqu'aujourd'hui.
9 Shi ya sa Lawiyawa ba su da rabo, ko gādo a cikin’yan’uwansu; Ubangiji ne gādonsu yadda Ubangiji Allahnku ya faɗa musu.)
C'est pourquoi Lévi n'eut point de portion ni de lot avec ses frères: l'Éternel est son lot, ainsi que l'Éternel, ton Dieu, le lui a dit.
10 To, na kasance a kan dutse yini arba’in da dare arba’in kamar yadda dā na yi da farko. Ubangiji kuwa ya saurare ni a wannan lokaci kuma. Ba nufinsa ba ne yă hallaka ku.
Or moi je restai sur la montagne, comme dans le séjour précédent, quarante jours et quarante nuits; et l'Éternel m'exauça aussi cette fois: l'Éternel ne voulut plus vous perdre.
11 Ubangiji ya ce mini, “Ka sauka, ka jagoranci mutanen a hanyarsu, domin su shiga, su kuma mallaki ƙasar da na rantse wa kakanninsu, zan ba su.”
Et l'Éternel me dit: Lève-toi, et dans le décampement marche à la tête du peuple, afin qu'ils arrivent et fassent la conquête du pays que j'ai juré à leurs pères de leur donner.
12 Yanzu fa, ya Isra’ila, mene ne Ubangiji Allahnku yake so a gare ku, in ba ku ji tsoron Ubangiji Allahnku, ku yi tafiya cikin hanyoyinsa, ku ƙaunace shi, ku bauta wa Ubangiji Allahnku da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku,
Et maintenant, Israël, qu'est-ce que l'Éternel, ton Dieu, exige de toi, sinon de craindre l'Éternel, ton Dieu, de marcher dans toutes ses voies, et de l'aimer, et de servir l'Éternel, ton Dieu, de tout ton cœur et de toute ton âme,
13 ku kuma kiyaye umarnan Ubangiji da kuma ƙa’idodinsa da nake ba ku a yau don amfaninku ba?
de garder les commandements de l'Éternel et ses statuts que je te prescris aujourd'hui pour ton bien.
14 Sammai, har da sama sammai, da duniya, da kome da yake cikinta na Ubangiji Allahnku ne.
Voici, à l'Éternel, ton Dieu, appartiennent les Cieux et les Cieux des Cieux, la terre et tout ce qu'elle renferme;
15 Duk da haka Ubangiji ya ƙaunaci kakanninku, ya kuma zaɓe ku, ku zuriyarsu, a bisa dukan al’ummai, yadda yake a yau.
cependant c'est à tes pères seuls que l'Éternel s'est attaché pour les aimer, et Il a choisi leur race qui viendrait après eux, vous, entre tous les peuples, comme [il arrive] aujourd'hui.
16 Saboda haka sai ku kame zukatanku, kada ku ƙara yin taurinkai.
En conséquence circoncisez le prépuce de vos cœurs et n'ayez plus le col roide.
17 Gama Ubangiji Allahnku ne Allahn alloli da Ubangijin iyayengiji, Allah mai girma, mai ƙarfi da kuma mai banrazana, wanda ba ya sonkai, ba ya cin hanci.
Car l'Éternel, votre Dieu, est le Dieu des Dieux, et le Seigneur des Seigneurs, le Dieu grand, puissant et redoutable qui ne fait point acception des personnes, et n'accepte point de présents,
18 Yakan tsare marayu da gwauraye, yana ƙaunar baƙon da yake zama a cikinku, yana ba su abinci da tufafi.
qui fait droit à l'orphelin et à la veuve et aime l'étranger et lui donne nourriture et vêtement.
19 Sai ku ƙaunaci baƙi, gama dā ku ma baƙi ne a ƙasar Masar.
Aimez donc les étrangers, car vous fûtes étrangers dans le pays d'Egypte.
20 Ku ji tsoron Ubangiji Allahnku, ku kuma bauta masa. Ku manne masa, ku kuma yi rantsuwarku da sunansa.
Crains l'Éternel, ton Dieu, sers-le, reste lui attaché et jure par son nom.
21 Shi ne abin yabonku; shi ne Allahnku, wanda ya aikata muku waɗancan manya abubuwa banmamaki masu banrazanar da kuka gani da idanunku.
Il est ta gloire, et Il est ton Dieu qui a opéré pour toi ces choses grandes et terribles que tes yeux ont vues.
22 Kakanninku da suka gangara zuwa Masar, su saba’in ne, yanzu kuwa Ubangiji Allahnku ya sa kuka ƙaru, kuka zama kamar taurari a sama.
C'est avec soixante-dix âmes que tes pères descendirent en Egypte, et maintenant l'Éternel, ton Dieu, t'a rendu égal en nombre aux étoiles des Cieux.

< Maimaitawar Shari’a 10 >