< Maimaitawar Shari’a 10 >

1 A lokacin Ubangiji ya ce mini, “Ka sassaƙa alluna biyu na dutse kamar na farko, ka haura wurina a kan dutse. Ka kuma yi akwatin katako.
"En ce temps-là, l’Éternel me dit: "Taille toi-même deux tables de pierre pareilles aux premières, et viens me trouver sur la montagne; fais-toi aussi une arche de bois.
2 Ni kuwa zan yi rubutu a kan allunan nan biyu, kalmomin da suke a alluna na farko, waɗanda ka farfashe. Za a ajiye su a cikin akwatin.”
J’Écrirai sur ces tables les paroles qui étaient sur les premières que tu as brisées, et tu les déposeras dans l’arche."
3 Sai na yi akwatin da itacen ƙirya, na kuma sassaƙa alluna biyu na dutse kamar na farko, sai na haura dutse da alluna biyun a hannuwana.
Je fis une arche en bois de chitîm, je taillai deux tables de pierre, semblables aux précédentes; puis je montai sur la montagne, les deux tables à la main.
4 Ubangiji kuwa ya sāke yin rubutu a waɗannan alluna abin da ya rubuta a allunan farko, wato, Dokoki Goma da ya furta a kan dutse a tsakiyar wuta, a ranar da mutane suka taru. Sai Ubangiji ya ba ni su.
Et l’Éternel grava sur les tables la même inscription, les dix paroles qu’il vous avait fait entendre sur la montagne, du milieu du feu, le jour de la convocation; puis l’Éternel me les remit.
5 Sa’an nan na sauko daga dutsen, na kuma ajiye allunan a cikin akwatin da na yi, yadda Ubangiji ya umarce ni, kuma suna can a yanzu.
Je redescendis de la montagne, je déposai les tables dans l’arche que j’avais faite, et elles y sont restées, ainsi que l’Éternel me l’avait prescrit.
6 (Isra’ilawa suka kama hanya daga rijiyoyin Beyerot Bene Ya’akan zuwa Mosera. A can Haruna ya rasu, aka kuma binne shi. Sai Eleyazar ɗansa ya gāje shi a matsayin firist.
(Or, les enfants d’Israël partirent de Beéroth-Benê-Yaakân pour aller à Mocêra: là est mort Aaron, là il a été enseveli, et son fils Eléazar l’a remplacé dans le sacerdoce.
7 Daga can suka tashi zuwa Gudgoda, daga Gudgoda kuma suka tafi Yotbata, ƙasa mai rafuffukan ruwa.
De là, ils allèrent à Goudgoda, et de Goudgoda à Yotbatha, contrée abondante en cours d’eau.
8 A lokacin Ubangiji ya keɓe kabilar Lawi don su riƙa ɗaukar akwatin alkawarin Ubangiji, su tsaya a gaban Ubangiji, su riƙa yin masa hidima, su kuma sa albarka a cikin sunansa, yadda suke yi har wa yau.
A cette même époque, l’Éternel distingua la tribu de Lévi, en la chargeant de porter l’arche de la divine alliance, de faire en permanence le service du Seigneur et de donner la bénédiction en son nom, comme elle l’a fait jusqu’à ce jour.
9 Shi ya sa Lawiyawa ba su da rabo, ko gādo a cikin’yan’uwansu; Ubangiji ne gādonsu yadda Ubangiji Allahnku ya faɗa musu.)
C’Est pourquoi Lévi n’a reçu part ni héritage avec ses frères: c’est Dieu qui est son héritage, ainsi que l’Éternel, ton Dieu, le lui a déclaré).
10 To, na kasance a kan dutse yini arba’in da dare arba’in kamar yadda dā na yi da farko. Ubangiji kuwa ya saurare ni a wannan lokaci kuma. Ba nufinsa ba ne yă hallaka ku.
J’Étais donc resté sur la montagne, comme la première fois, quarante jours et quarante nuits; et l’Éternel m’exauça cette fois encore, il ne voulut pas t’exterminer,
11 Ubangiji ya ce mini, “Ka sauka, ka jagoranci mutanen a hanyarsu, domin su shiga, su kuma mallaki ƙasar da na rantse wa kakanninsu, zan ba su.”
et il me dit: "Va, dirige la marche de ce peuple, pour qu’il atteigne et conquière le pays que j’ai juré à leurs pères de leur donner."
12 Yanzu fa, ya Isra’ila, mene ne Ubangiji Allahnku yake so a gare ku, in ba ku ji tsoron Ubangiji Allahnku, ku yi tafiya cikin hanyoyinsa, ku ƙaunace shi, ku bauta wa Ubangiji Allahnku da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku,
Et maintenant, ô Israël! Ce que l’Éternel, ton Dieu, te demande uniquement, c’est de révérer l’Éternel, ton Dieu, de suivre en tout ses voies, de l’aimer, de le servir de tout ton cœur et de toute ton âme,
13 ku kuma kiyaye umarnan Ubangiji da kuma ƙa’idodinsa da nake ba ku a yau don amfaninku ba?
en observant les préceptes et les lois du Seigneur, que je t’impose aujourd’hui, pour devenir heureux.
14 Sammai, har da sama sammai, da duniya, da kome da yake cikinta na Ubangiji Allahnku ne.
Vois, l’Éternel, ton Dieu, possède les cieux et les cieux des cieux, la terre et tout ce qu’elle renferme:
15 Duk da haka Ubangiji ya ƙaunaci kakanninku, ya kuma zaɓe ku, ku zuriyarsu, a bisa dukan al’ummai, yadda yake a yau.
et pourtant, ce sont tes pères qu’à préférés l’Éternel, se complaisant en eux; et c’est leur postérité après eux, c’est vous qu’il a adoptés entre tous les peuples, comme vous le voyez aujourd’hui.
16 Saboda haka sai ku kame zukatanku, kada ku ƙara yin taurinkai.
Supprimez donc l’impureté de votre cœur, et cessez de roidir votre cou.
17 Gama Ubangiji Allahnku ne Allahn alloli da Ubangijin iyayengiji, Allah mai girma, mai ƙarfi da kuma mai banrazana, wanda ba ya sonkai, ba ya cin hanci.
Car l’Éternel, votre Dieu, c’est le Dieu des dieux et le maître des maîtres, Dieu souverain, puissant et redoutable, qui ne fait point acception de personnes, qui ne cède point à la corruption;
18 Yakan tsare marayu da gwauraye, yana ƙaunar baƙon da yake zama a cikinku, yana ba su abinci da tufafi.
qui fait droit à l’orphelin et à la veuve; qui témoigne son amour à l’étranger, en lui assurant le pain et le vêtement.
19 Sai ku ƙaunaci baƙi, gama dā ku ma baƙi ne a ƙasar Masar.
Vous aimerez l’étranger, vous qui fûtes étrangers dans le pays d’Egypte!
20 Ku ji tsoron Ubangiji Allahnku, ku kuma bauta masa. Ku manne masa, ku kuma yi rantsuwarku da sunansa.
C’Est l’Éternel, ton Dieu, que tu dois révérer, c’est lui que tu dois servir; attache-toi à lui seul, ne jure que par son nom.
21 Shi ne abin yabonku; shi ne Allahnku, wanda ya aikata muku waɗancan manya abubuwa banmamaki masu banrazanar da kuka gani da idanunku.
Il est ton honneur, il est ton Dieu, celui qui a fait pour toi ces grandes et prodigieuses choses que tes yeux ont vues!
22 Kakanninku da suka gangara zuwa Masar, su saba’in ne, yanzu kuwa Ubangiji Allahnku ya sa kuka ƙaru, kuka zama kamar taurari a sama.
Tes ancêtres étaient soixante-dix âmes quand ils vinrent en Egypte; et maintenant l’Éternel, ton Dieu, t’a multiplié comme les étoiles du ciel."

< Maimaitawar Shari’a 10 >