< Maimaitawar Shari’a 10 >
1 A lokacin Ubangiji ya ce mini, “Ka sassaƙa alluna biyu na dutse kamar na farko, ka haura wurina a kan dutse. Ka kuma yi akwatin katako.
'At that time hath Jehovah said unto me, Grave for thee two tables of stone, like the first, and come up unto Me, into the mount, and thou hast made for thee an ark of wood,
2 Ni kuwa zan yi rubutu a kan allunan nan biyu, kalmomin da suke a alluna na farko, waɗanda ka farfashe. Za a ajiye su a cikin akwatin.”
and I write on the tables the words which were on the first tables, which thou hast broken, and thou hast placed them in the ark;
3 Sai na yi akwatin da itacen ƙirya, na kuma sassaƙa alluna biyu na dutse kamar na farko, sai na haura dutse da alluna biyun a hannuwana.
and I make an ark of shittim wood, and grave two tables of stone like the first, and go up to the mount, and the two tables in my hand.
4 Ubangiji kuwa ya sāke yin rubutu a waɗannan alluna abin da ya rubuta a allunan farko, wato, Dokoki Goma da ya furta a kan dutse a tsakiyar wuta, a ranar da mutane suka taru. Sai Ubangiji ya ba ni su.
'And He writeth on the tables, according to the first writing, the Ten Matters, which Jehovah hath spoken unto you in the mount, out of the midst of the fire, in the day of the assembly, and Jehovah giveth them unto me,
5 Sa’an nan na sauko daga dutsen, na kuma ajiye allunan a cikin akwatin da na yi, yadda Ubangiji ya umarce ni, kuma suna can a yanzu.
and I turn and come down from the mount, and put the tables in the ark which I had made, and they are there, as Jehovah commanded me.
6 (Isra’ilawa suka kama hanya daga rijiyoyin Beyerot Bene Ya’akan zuwa Mosera. A can Haruna ya rasu, aka kuma binne shi. Sai Eleyazar ɗansa ya gāje shi a matsayin firist.
'And the sons of Israel have journeyed from Beeroth of the sons of Jaakan to Mosera, there Aaron died, and he is buried there, and Eleazar his son doth act as priest in his stead;
7 Daga can suka tashi zuwa Gudgoda, daga Gudgoda kuma suka tafi Yotbata, ƙasa mai rafuffukan ruwa.
thence they journeyed to Gudgodah, and from Gudgodah to Jotbathah, a land of brooks of water.
8 A lokacin Ubangiji ya keɓe kabilar Lawi don su riƙa ɗaukar akwatin alkawarin Ubangiji, su tsaya a gaban Ubangiji, su riƙa yin masa hidima, su kuma sa albarka a cikin sunansa, yadda suke yi har wa yau.
'At that time hath Jehovah separated the tribe of Levi, to bear the ark of the covenant of Jehovah, to stand before Jehovah, to serve Him, and to bless in His name, unto this day,
9 Shi ya sa Lawiyawa ba su da rabo, ko gādo a cikin’yan’uwansu; Ubangiji ne gādonsu yadda Ubangiji Allahnku ya faɗa musu.)
therefore there hath not been to Levi a portion and inheritance with his brethren; Jehovah Himself [is] his inheritance, as Jehovah thy God hath spoken to him.
10 To, na kasance a kan dutse yini arba’in da dare arba’in kamar yadda dā na yi da farko. Ubangiji kuwa ya saurare ni a wannan lokaci kuma. Ba nufinsa ba ne yă hallaka ku.
'And I — I have stood in the mount, as the former days, forty days and forty nights, and Jehovah hearkeneth unto me also at that time; Jehovah hath not willed to destroy thee.
11 Ubangiji ya ce mini, “Ka sauka, ka jagoranci mutanen a hanyarsu, domin su shiga, su kuma mallaki ƙasar da na rantse wa kakanninsu, zan ba su.”
'And Jehovah saith unto me, Rise, go to journey before the people, and they go in and possess the land which I have sworn to their fathers to give to them.
12 Yanzu fa, ya Isra’ila, mene ne Ubangiji Allahnku yake so a gare ku, in ba ku ji tsoron Ubangiji Allahnku, ku yi tafiya cikin hanyoyinsa, ku ƙaunace shi, ku bauta wa Ubangiji Allahnku da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku,
'And now, Israel, what is Jehovah thy God asking from thee, except to fear Jehovah thy God, to walk in all His ways, and to love Him, and to serve Jehovah thy God with all thy heart, and with all thy soul,
13 ku kuma kiyaye umarnan Ubangiji da kuma ƙa’idodinsa da nake ba ku a yau don amfaninku ba?
to keep the commands of Jehovah, and His statutes which I am commanding thee to-day, for good to thee?
14 Sammai, har da sama sammai, da duniya, da kome da yake cikinta na Ubangiji Allahnku ne.
'Lo, to Jehovah thy God [are] the heavens and the heavens of the heavens, the earth and all that [is] in it;
15 Duk da haka Ubangiji ya ƙaunaci kakanninku, ya kuma zaɓe ku, ku zuriyarsu, a bisa dukan al’ummai, yadda yake a yau.
only in thy fathers hath Jehovah delighted — to love them, and He doth fix on their seed after them — on you, out of all the peoples as [at] this day;
16 Saboda haka sai ku kame zukatanku, kada ku ƙara yin taurinkai.
and ye have circumcised the foreskin of your heart, and your neck ye do not harden any more;
17 Gama Ubangiji Allahnku ne Allahn alloli da Ubangijin iyayengiji, Allah mai girma, mai ƙarfi da kuma mai banrazana, wanda ba ya sonkai, ba ya cin hanci.
for Jehovah your God — He [is] God of the gods, and Lord of the lords; God, the great, the mighty, and the fearful; who accepteth not persons, nor taketh a bribe;
18 Yakan tsare marayu da gwauraye, yana ƙaunar baƙon da yake zama a cikinku, yana ba su abinci da tufafi.
He is doing the judgment of fatherless and widow, and loving the sojourner, to give to him bread and raiment.
19 Sai ku ƙaunaci baƙi, gama dā ku ma baƙi ne a ƙasar Masar.
'And ye have loved the sojourner, for sojourners ye were in the land of Egypt.
20 Ku ji tsoron Ubangiji Allahnku, ku kuma bauta masa. Ku manne masa, ku kuma yi rantsuwarku da sunansa.
'Jehovah thy God thou dost fear, Him thou dost serve, and to Him thou dost cleave, and by His name thou dost swear.
21 Shi ne abin yabonku; shi ne Allahnku, wanda ya aikata muku waɗancan manya abubuwa banmamaki masu banrazanar da kuka gani da idanunku.
He [is] thy praise, and He [is] thy God, who hath done with thee these great and fearful [things] which thine eyes have seen:
22 Kakanninku da suka gangara zuwa Masar, su saba’in ne, yanzu kuwa Ubangiji Allahnku ya sa kuka ƙaru, kuka zama kamar taurari a sama.
with seventy persons did thy fathers go down to Egypt, and now hath Jehovah thy God made thee as stars of the heavens for multitude.