< Maimaitawar Shari’a 10 >
1 A lokacin Ubangiji ya ce mini, “Ka sassaƙa alluna biyu na dutse kamar na farko, ka haura wurina a kan dutse. Ka kuma yi akwatin katako.
U to vrijeme Jahve mi reče: 'Iskleši dvije kamene ploče kao i prijašnje pa se popni k meni na brdo; a napravi i drveni kovčeg.
2 Ni kuwa zan yi rubutu a kan allunan nan biyu, kalmomin da suke a alluna na farko, waɗanda ka farfashe. Za a ajiye su a cikin akwatin.”
Na ploče ću napisati riječi koje su bile na prvim pločama što si ih razbio. A onda ih položi u kovčeg.'
3 Sai na yi akwatin da itacen ƙirya, na kuma sassaƙa alluna biyu na dutse kamar na farko, sai na haura dutse da alluna biyun a hannuwana.
Načinih kovčeg od bagremovine, isklesah dvije kamene ploče kao što bijahu prve, pa se, s dvjema pločama u ruci, popeh na brdo.
4 Ubangiji kuwa ya sāke yin rubutu a waɗannan alluna abin da ya rubuta a allunan farko, wato, Dokoki Goma da ya furta a kan dutse a tsakiyar wuta, a ranar da mutane suka taru. Sai Ubangiji ya ba ni su.
I napisa na te ploče, kao i prije, Deset riječi koje vam je Jahve rekao na brdu, isred ognja, na dan zbora. Onda ih Jahve dade meni.
5 Sa’an nan na sauko daga dutsen, na kuma ajiye allunan a cikin akwatin da na yi, yadda Ubangiji ya umarce ni, kuma suna can a yanzu.
Okrenuh se i siđoh s brda. Položih ploče u kovčeg koji bijah napravio. I stadoše ondje, kako mi je Jahve naredio.
6 (Isra’ilawa suka kama hanya daga rijiyoyin Beyerot Bene Ya’akan zuwa Mosera. A can Haruna ya rasu, aka kuma binne shi. Sai Eleyazar ɗansa ya gāje shi a matsayin firist.
Od Beerota sinova Jaakanovih odoše Izraelci u Moseru. Ondje umrije Aron i ondje bi pokopan. Svećenikom mjesto njega postade njegov sin Eleazar.
7 Daga can suka tashi zuwa Gudgoda, daga Gudgoda kuma suka tafi Yotbata, ƙasa mai rafuffukan ruwa.
Odande odoše u Gudgodu; iz Gudgode u Jotbatu, u kraj bogat potocima.
8 A lokacin Ubangiji ya keɓe kabilar Lawi don su riƙa ɗaukar akwatin alkawarin Ubangiji, su tsaya a gaban Ubangiji, su riƙa yin masa hidima, su kuma sa albarka a cikin sunansa, yadda suke yi har wa yau.
U to vrijeme odvoji Jahve pleme Levijevo da nosi Kovčeg saveza Jahvina; da pred Jahvom stoji u njegovoj službi te da u njegovo ime blagoslivlja, kako radi i danas.
9 Shi ya sa Lawiyawa ba su da rabo, ko gādo a cikin’yan’uwansu; Ubangiji ne gādonsu yadda Ubangiji Allahnku ya faɗa musu.)
Stoga Levi nema udjela ni baštine sa svojom braćom: Jahve je njegova baština, kako mu je Jahve, Bog tvoj, i rekao.
10 To, na kasance a kan dutse yini arba’in da dare arba’in kamar yadda dā na yi da farko. Ubangiji kuwa ya saurare ni a wannan lokaci kuma. Ba nufinsa ba ne yă hallaka ku.
Na brdu sam ostao, kao i prvi put, četrdeset dana i četrdeset noći. I usliša me Jahve i taj put; nije htio da te uništi,
11 Ubangiji ya ce mini, “Ka sauka, ka jagoranci mutanen a hanyarsu, domin su shiga, su kuma mallaki ƙasar da na rantse wa kakanninsu, zan ba su.”
nego mi Jahve reče: 'Ustaj! Idi pred ovim narodom da uđu i zaposjednu zemlju za koju sam se zakleo njihovim ocima da ću im je dati.'
12 Yanzu fa, ya Isra’ila, mene ne Ubangiji Allahnku yake so a gare ku, in ba ku ji tsoron Ubangiji Allahnku, ku yi tafiya cikin hanyoyinsa, ku ƙaunace shi, ku bauta wa Ubangiji Allahnku da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku,
Dakle, Izraele, što od tebe traži Jahve, Bog tvoj? Samo to da se bojiš Jahve, Boga svoga; da po svim putovima njegovim hodiš; da ga ljubiš i služiš Jahvi, Bogu svome, svim srcem svojim i svom dušom svojom;
13 ku kuma kiyaye umarnan Ubangiji da kuma ƙa’idodinsa da nake ba ku a yau don amfaninku ba?
da držiš Jahvine zapovijedi i njegove zakone što ti ih danas za tvoje dobro dajem.
14 Sammai, har da sama sammai, da duniya, da kome da yake cikinta na Ubangiji Allahnku ne.
Evo, Jahvi, Bogu tvome, pripada nebo i nebo nad nebesima, zemlja i sve što je na njoj.
15 Duk da haka Ubangiji ya ƙaunaci kakanninku, ya kuma zaɓe ku, ku zuriyarsu, a bisa dukan al’ummai, yadda yake a yau.
Ali Jahvi samo vaši oci omilješe i poslije njih izabrao je vas, potomke njihove, između svih naroda, kako je i danas.
16 Saboda haka sai ku kame zukatanku, kada ku ƙara yin taurinkai.
Srce svoje obrežite; šiju više ne ukrućujte!
17 Gama Ubangiji Allahnku ne Allahn alloli da Ubangijin iyayengiji, Allah mai girma, mai ƙarfi da kuma mai banrazana, wanda ba ya sonkai, ba ya cin hanci.
Jer Jahve, Bog vaš, Bog je nad bogovima, Gospodar nad gospodarima, Bog velik, jak i strašan, koji nije pristran i ne da se podmititi;
18 Yakan tsare marayu da gwauraye, yana ƙaunar baƙon da yake zama a cikinku, yana ba su abinci da tufafi.
daje pravdu siroti i udovici; ljubi pridošlicu, daje mu hranu i odjeću.
19 Sai ku ƙaunaci baƙi, gama dā ku ma baƙi ne a ƙasar Masar.
Ljubite i vi pridošlicu, jer ste i sami bili pridošlice u zemlji egipatskoj.
20 Ku ji tsoron Ubangiji Allahnku, ku kuma bauta masa. Ku manne masa, ku kuma yi rantsuwarku da sunansa.
Boj se Jahve, Boga svojeg; njemu služi; uza nj se priljubi; njegovim imenom priseži.
21 Shi ne abin yabonku; shi ne Allahnku, wanda ya aikata muku waɗancan manya abubuwa banmamaki masu banrazanar da kuka gani da idanunku.
On je tvoja slava, Bog tvoj, koji je radi tebe učinio velika i čudesna djela što su ih vidjele tvoje oči.
22 Kakanninku da suka gangara zuwa Masar, su saba’in ne, yanzu kuwa Ubangiji Allahnku ya sa kuka ƙaru, kuka zama kamar taurari a sama.
Tvojih otaca, kad su se spustili u Egipat, bješe samo sedamdeset, a sad je Jahve, Bog tvoj, učinio te vas ima kao zvijezda na nebu.