< Maimaitawar Shari’a 10 >
1 A lokacin Ubangiji ya ce mini, “Ka sassaƙa alluna biyu na dutse kamar na farko, ka haura wurina a kan dutse. Ka kuma yi akwatin katako.
Te vaeng tue ah BOEIPA loh kai taengah, “Lungto te lamhma kah lungpael rhoi bangla namah loh saek lamtah tlang ah kai taengla ha yoeng. Te phoeiah thing thingkawng khaw namah loh saii bal.
2 Ni kuwa zan yi rubutu a kan allunan nan biyu, kalmomin da suke a alluna na farko, waɗanda ka farfashe. Za a ajiye su a cikin akwatin.”
Lamhma kah vik na dae lungpael rhoi dongkah aka om olka te tahae kah lungpael rhoi dongah koep ka daek saeh lamtah thingkawng khuiah khueh,” a ti.
3 Sai na yi akwatin da itacen ƙirya, na kuma sassaƙa alluna biyu na dutse kamar na farko, sai na haura dutse da alluna biyun a hannuwana.
Te dongah rhining thing te thingkawng la ka saii tih lungto panit te lamhma kah cabael bangla ka saek. Te phoeiah kut dongkah cabael rhoi neh tlang la ka luei.
4 Ubangiji kuwa ya sāke yin rubutu a waɗannan alluna abin da ya rubuta a allunan farko, wato, Dokoki Goma da ya furta a kan dutse a tsakiyar wuta, a ranar da mutane suka taru. Sai Ubangiji ya ba ni su.
Te daengah ni hlangping hnin kah tlang ah BOEIPA loh nangmih ham hmai khui lamkah a thui olka lungrha te lungpael dongah lamhma kah cadaek bangla a daek tih BOEIPA amah loh kai m'paek pueng.
5 Sa’an nan na sauko daga dutsen, na kuma ajiye allunan a cikin akwatin da na yi, yadda Ubangiji ya umarce ni, kuma suna can a yanzu.
Te dongah tlang lamkah ka mael tih ka suntlak vaengah lungpael rhoi te BOEIPA loh kai n'uen vanbangla ka saii thingkawng khuiah ka khueh tih om van.
6 (Isra’ilawa suka kama hanya daga rijiyoyin Beyerot Bene Ya’akan zuwa Mosera. A can Haruna ya rasu, aka kuma binne shi. Sai Eleyazar ɗansa ya gāje shi a matsayin firist.
Israel ca rhoek loh Beeroth-Bene-jaakan lamkah Moserah la a caeh uh vaengah Aaron duek tih pahoi a up uh. Te phoeiah a capa Eleazar te anih yueng la khosoih.
7 Daga can suka tashi zuwa Gudgoda, daga Gudgoda kuma suka tafi Yotbata, ƙasa mai rafuffukan ruwa.
Te lamkah te Gudgodah la cet uh tih Gudgodah lamloh Jobathah kho kah soklong tui la cetuh.
8 A lokacin Ubangiji ya keɓe kabilar Lawi don su riƙa ɗaukar akwatin alkawarin Ubangiji, su tsaya a gaban Ubangiji, su riƙa yin masa hidima, su kuma sa albarka a cikin sunansa, yadda suke yi har wa yau.
Te vaeng hnin ah Levi koca rhoek tah, BOEIPA kah paipi thingkawng aka kawt ham, a bibi la BOEIPA mikhmuh ah aka pai ham tihnin duela a ming neh yoethen paek ham khaw BOEIPA loh a hoep.
9 Shi ya sa Lawiyawa ba su da rabo, ko gādo a cikin’yan’uwansu; Ubangiji ne gādonsu yadda Ubangiji Allahnku ya faɗa musu.)
Te dongah Levi kah khoyo neh a manuca rhoek taengkah rho he rhawp om pawh. BOEIPA na Pathen kah a thui bangla BOEIPA amah ni anih kah rho la aka om coeng.
10 To, na kasance a kan dutse yini arba’in da dare arba’in kamar yadda dā na yi da farko. Ubangiji kuwa ya saurare ni a wannan lokaci kuma. Ba nufinsa ba ne yă hallaka ku.
Kai ngawn tah hnuk vaengkah bangla tlang ah khohnin likip khoyin khothaih sut ka om. Tekah khohnin ah khaw BOEIPA loh ka ol a hnatun bal dongah ni nang phae ham te BOEIPA loh a huem pawh.
11 Ubangiji ya ce mini, “Ka sauka, ka jagoranci mutanen a hanyarsu, domin su shiga, su kuma mallaki ƙasar da na rantse wa kakanninsu, zan ba su.”
Te dongah BOEIPA loh kai taengah, “Thoo, longpueng ah khaw pilnam kah a hmai la na caeh pah daengah ni amih taengah paek hamla, a napa rhoek taengah ka caeng khohmuen te kun uh vetih a pang uh eh,” a ti.
12 Yanzu fa, ya Isra’ila, mene ne Ubangiji Allahnku yake so a gare ku, in ba ku ji tsoron Ubangiji Allahnku, ku yi tafiya cikin hanyoyinsa, ku ƙaunace shi, ku bauta wa Ubangiji Allahnku da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku,
Tahae ah Israel nang, BOEIPA na Pathen loh nang taeng lamkah balae ham bih? Tedae BOEIPA na Pathen te rhih ham neh, a longpuei boeih dongah pongpa ham, amah lungnah ham neh BOEIPA na Pathen te na thinko boeih, na hinglu boeih neh thothueng ham,
13 ku kuma kiyaye umarnan Ubangiji da kuma ƙa’idodinsa da nake ba ku a yau don amfaninku ba?
BOEIPA kah olpaek neh a khosing tah ngaithuen ham ah om. Te te namah kah a then ham ni tihnin ah kai loh nang kang uen.
14 Sammai, har da sama sammai, da duniya, da kome da yake cikinta na Ubangiji Allahnku ne.
Vaan neh vaan kah vaan boeih khaw, diklai neh a khuiah aka om boeih khaw, BOEIPA na Pathen ham ni ke.
15 Duk da haka Ubangiji ya ƙaunaci kakanninku, ya kuma zaɓe ku, ku zuriyarsu, a bisa dukan al’ummai, yadda yake a yau.
Na pa rhoek te BOEIPA loh a ven tih, a lungnah dongah ni amih hnukkah a tiingan la, nangmih te pilnam cungkuem soah tihnin kah bangla n'coelh.
16 Saboda haka sai ku kame zukatanku, kada ku ƙara yin taurinkai.
Te dongah na thinko yahhmui te rhet uh lamtah na rhawn khaw mangkhak sak uh voel boeh.
17 Gama Ubangiji Allahnku ne Allahn alloli da Ubangijin iyayengiji, Allah mai girma, mai ƙarfi da kuma mai banrazana, wanda ba ya sonkai, ba ya cin hanci.
BOEIPA na Pathen tah pathen boeih kah Pathen, boei boeih kah Boeipa, hlangrhalh Pathen puei la om tih a rhih a om dongah hlang maelhmai khaw dan pawt tih kapbaih khaw doe bal pawh.
18 Yakan tsare marayu da gwauraye, yana ƙaunar baƙon da yake zama a cikinku, yana ba su abinci da tufafi.
Cadah nuhmai kah laitloeknah te a rhuun tih yinlai te buh neh himbai paek ham a lungnah.
19 Sai ku ƙaunaci baƙi, gama dā ku ma baƙi ne a ƙasar Masar.
Egypt kho ah yinlai la na om uh dongah yinlai te lungnah uh van.
20 Ku ji tsoron Ubangiji Allahnku, ku kuma bauta masa. Ku manne masa, ku kuma yi rantsuwarku da sunansa.
BOEIPA na Pathen amah te rhih lamtah thothueng lah. Amah taengah pangnal lamtah a ming neh toemngam lah.
21 Shi ne abin yabonku; shi ne Allahnku, wanda ya aikata muku waɗancan manya abubuwa banmamaki masu banrazanar da kuka gani da idanunku.
Anih tah na koehnah neh na Pathen la om. Amah loh nang ham hno len a saii dongah a rhih om la na mik loh a hmuh.
22 Kakanninku da suka gangara zuwa Masar, su saba’in ne, yanzu kuwa Ubangiji Allahnku ya sa kuka ƙaru, kuka zama kamar taurari a sama.
Na pa rhoek te hinglu sawmrhih ni Egypt la aka suntla. Tedae tahae ah BOEIPA na Pathen loh vaan aisi yet la nang n'khueh.