< Daniyel 1 >

1 A Shekara ta uku ta mulki Yehohiyakim sarkin Yahuda, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya zo Urushalima ya kuma yi mata ƙawanya.
La troisième année de Jéhojakim Roi de Juda, Nébucadnetsar Roi de Babylone vint [contre] Jérusalem, et l'assiégea.
2 Sai Ubangiji ya bashe Yehohiyakim sarkin Yahuda a hannunsa, tare da waɗansu kayayyakin haikalin Allah. Ya ɗauki waɗannan kayan zuwa cikin haikalin allahnsa a Babilon cikin ma’ajin gidan allahnsa.
Et le Seigneur livra en sa main Jéhojakim Roi de Juda, et une partie des vaisseaux de la maison de Dieu, lesquels [Nébucadnetsar] fit emporter au pays de Sinhar en la maison de son Dieu; et il mit ces vaisseaux en la Trésorerie de son Dieu.
3 Sa’an nan sarkin ya umarci Ashfenaz, shugaban fadarsa yă kawo waɗansu daga cikin Isra’ilawan da suka fito daga gidan sarauta da kuma na fitattun mutane.
Et le Roi dit à Aspenaz, Capitaine de ses Eunuques, qu'il amenât d'entre les enfants d'Israël, et de la race Royale et des principaux Seigneurs,
4 Matasa maza waɗanda ba su da wata naƙasa kuma kyawawa, hazikai ta kowace hanyar koyo, sanannu, masu saurin fahimtar abu, da kuma waɗanda suka cancanci su yi aiki a fadar sarki. Zai koya musu harshen Babiloniyawa da kuma littattafansu.
Quelques jeunes enfants, en qui il n'y eût aucun défaut, beaux de visage, instruits en toute sagesse, connaissant les sciences, qui eussent beaucoup d'intelligence, et en qui il y eût de la force, pour se tenir au palais du Roi; et qu'on leur enseignât les lettres et la langue des Caldéens.
5 Sarki kuma ya sa a ba su abinci da ruwan inabi kowace rana daga cikin abincin sarki. Za a koyar da su har shekaru uku, bayan haka kuma su shiga yin wa sarki hidima.
Et le Roi leur assigna pour provision chaque jour une portion de la viande Royale, et du vin dont il buvait; afin qu'on les nourrît ainsi trois ans, et qu'ensuite [quelques-uns d'entre eux] servissent en la présence du Roi.
6 Daga cikin waɗannan da aka zaɓa akwai waɗansu daga Yahuda, Daniyel, Hananiya, Mishayel da kuma Azariya.
Entre ceux-là il y eut des enfants de Juda, Daniel, Hanania, Misaël et Hazaria.
7 Sai sarkin fada ya raɗa musu sababbin sunaye, ga Daniyel ya raɗa masa Belteshazar; ga Hananiya ya raɗa masa Shadrak; ga Mishayel ya raɗa masa Meshak; ga Azariya kuma ya raɗa masa Abednego.
Mais le Capitaine des Eunuques leur mit d'autres noms; car il donna à Daniel le nom de Beltesatsar; à Hanania, celui de Sadrac; à Misaël, celui de Mésac; et à Hazaria, celui d'Habed-nego.
8 Amma Daniyel ya ƙudura a zuciyarsa ba zai ƙazantar da kansa da abinci da ruwan inabin sarki ba, sai ya tambayi sarkin fada don a ba shi izinin kada yă ƙazantar da kansa ta wannan hanya.
Or Daniel se proposa dans son cœur de ne se point souiller par la portion de la viande du Roi, ni par le vin dont le Roi buvait; c'est pourquoi il supplia le Chef des Eunuques afin qu'il ne l'engageât point à se souiller.
9 Sai Allah ya sa sarkin fada ya nuna masa tagomashi ya kuma ƙaunaci Daniyel,
Et Dieu fit que le Chef des Eunuques eut de la bonté pour Daniel, et qu'il eut pitié de lui.
10 amma sai sarkin fada ya ce wa Daniyel, “Ina jin tsoron ranka yă daɗe, sarkina wanda ya sa a ba ku abinci da ruwan inabi. Me zai sa yă ga kuna ramewa fiye da sauran samari, tsaranku? Sarki zai sa a fille mini kai saboda ku.”
Toutefois le Capitaine des Eunuques dit à Daniel: Je crains le Roi mon maître, qui a ordonné votre manger et votre boire; pourquoi verrait-il vos visages plus défaits que ceux des autres jeunes enfants vos semblables, et rendriez-vous ma tête coupable envers le Roi?
11 Sai Daniyel ya ce wa mai gadi wanda sarkin fada ya sa yă kula da Daniyel, Hananiya, Mishayel da Azariya,
Mais Daniel dit à Meltsar, qui avait été ordonné par le Capitaine des Eunuques sur Daniel, Hanania, Misaël, et Hazaria;
12 “Ina roƙonka ka gwada bayinka kwana goma. Kada ka ba mu kome sai kayan lambu mu ci da kuma baƙin ruwa mu sha.
Eprouve, je te prie, tes serviteurs pendant dix jours, et qu'on nous donne des légumes à manger, et de l'eau à boire.
13 Sa’an nan sai ka dubi fuskokinmu da na sauran samarin da suke ci daga abincin sarki; sa’an nan ka yi da bayinka bisa ga abin da ka gani.”
Et après cela regarde nos visages, et les visages des jeunes enfants qui mangent la portion de la viande Royale; puis tu feras à tes serviteurs selon ce que tu auras vu.
14 Sai ya amince da haka ya kuma gwada su har kwana goma.
Et il leur accorda cela, et les éprouva pendant dix jours.
15 A ƙarshen kwana goma sai aka ga fuskokinsu suna sheƙi, sun kuma yi ƙiba fiye da samarin da suke cin abinci irin na sarki.
Mais au bout des dix jours leurs visages parurent en meilleur état, et ils avaient plus d'embonpoint que tous les jeunes enfants qui mangeaient la portion de la viande Royale.
16 Sai mai gadinsu ya janye abinci da ruwan inabi irin na sarki, ya ci gaba da ba su kayan lambu.
Ainsi Meltsar prenait la portion de leur viande, et le vin qu'ils devaient boire, et leur donnait des légumes.
17 Ga samarin nan guda huɗu Allah ya ba su sani da ganewar dukan irin littattafai da kuma koyarwa. Daniyel kuma ya iya gane wahayi da kowane irin mafarki.
Et Dieu donna à ces quatre jeunes enfants de la science et de l'intelligence dans toutes les lettres, et de la sagesse; et Daniel s'entendait en toute vision, et dans les songes.
18 A ƙarshen lokacin da sarki ya sa da za a kawo su ciki, sai sarkin fada ya gabatar da su ga Nebukadnezzar.
Et au bout des jours que le Roi avait dit qu'on les amenât, le Capitaine des Eunuques les amena devant Nébucadnetsar.
19 Sarki kuwa ya yi magana da su, sai ya gano cewa babu wani kamar Daniyel, Hananiya, Mishayel da kuma Azariya; don haka sai suka shiga yi wa sarki hidima.
Et le Roi s'entretint avec eux; mais entre eux tous il ne s'en trouva point de tels que Daniel, Hanania, Misaël, et Hazaria; et ils se tinrent en la présence du Roi.
20 A dukan al’amuran hikima da na fahimta wanda sarki ya tambaye su, ya tarar sun fi dukan masu sihiri da bokaye waɗanda suke cikin mulkinsa sau goma.
Et dans toute question savante et qui demandait de la pénétration, sur quoi le Roi les interrogeait il trouva dix fois plus de science en eux que dans tous les tireurs d'horoscope et les astrologues qui étaient en tout son Royaume.
21 Daniyel kuwa ya kasance a nan har shekara ta farko ta mulkin sarki Sairus.
Et Daniel [y] fut jusqu'à la première année du Roi Cyrus.

< Daniyel 1 >