< Daniyel 9 >
1 A shekara ta fari da mulkin Dariyus ɗan Zerzes (wanda yake Bamediye), wanda aka mai da shi sarki a masarautar Babiloniyawa
Прве године Дарија, сина Асвировог од племена мидског, који се зацари над царством халдејским,
2 a shekara ta farko ta mulkinsa, ni, Daniyel na gane daga cikin littattafai, bisa ga maganar Ubangiji da aka faɗa wa annabi Irmiya, cewa zaman Urushalima kango zai kai shekara saba’in.
Прве године његовог царовања ја Данило разумех из књига број година, које беше рекао Господ Јеремији пророку да ће се навршити развалинама јерусалимским, седамдесет година.
3 Sai na juya wurin Ubangiji Allah na roƙe shi ta wurin addu’a da koke-koke, cikin azumi, ina saye da tsummoki, na kuma zauna a cikin toka.
И окретох лице своје ка Господу Богу тражећи Га молитвом и молбама с постом и с кострети и пепелом.
4 Na yi addu’a ga Ubangiji Allahna na furta laifina. “Ya Ubangiji, mai alfarma da kuma Allah mai banrazana, wanda yake cika alkawarinsa na ƙauna ga duk wanda ya ƙaunace shi ya kuma kiyaye dokokinsa,
И помолих се Господу Богу свом и исповедајући се рекох: О Господе, Боже велики и страшни, који држиш завет и милост онима који Те љубе и држе заповести Твоје;
5 mun yi zunubi muka kuma yi ba daidai ba. Mu mugaye ne da kuma’yan tawaye; mun juya wa umarninka da shari’unka baya.
Згрешисмо и зло чинисмо и бисмо безбожни, и одметнусмо се и одступисмо од заповести Твојих и од закона Твојих.
6 Ba mu saurari bayinka annabawa ba, waɗanda suka yi magana a sunanka ga sarakunanmu da masu mulkinmu da iyayenmu, da kuma dukan mutanen ƙasa.
И не слушасмо слуга Твојих пророка, који говораху у Твоје име царевима нашим, кнезовима нашим и очевима нашим и свему народу земаљском.
7 “Ubangiji, kai mai adalci ne, amma a yau kunya ta rufe mu, mutanen Yahuda da mutanen Urushalima da na dukan Isra’ila, waɗanda suke kusa da kuma nesa, a dukan ƙasashen da ka warwatsa mu saboda rashin amincinmu a gare ka.
У Тебе је, Господе, правда, а у нас срам на лицу, како је данас, у Јудејаца и у Јерусалимљана и у свих Израиљаца, који су близу и који су далеко по свим земљама куда си их разагнао за грехе њихове, којима Ти грешише.
8 Ya Ubangiji, mu da sarakunanmu, da masu mulkinmu da iyayenmu kunya ta rufe mu saboda mun yi maka zunubi.
Господе, у нас је срам на лицу, у царева наших, у кнезова наших и у отаца наших, јер Ти згрешисмо.
9 Ubangiji Allahnmu mai jinƙai ne, mai gafartawa ne kuma, ko da yake mun yi masa tawaye;
У Господа је Бога нашег милост и праштање, јер се одметнусмо од Њега,
10 ba mu yi biyayya ga Ubangiji Allahnmu ba, ba mu kuma kiyaye shari’unsa da ya ba mu ta wuri bayinsa annabawa ba.
И не слушасмо глас Господа Бога свог да ходимо по законима Његовим, које нам је дао преко слуга својих пророка.
11 Dukan Isra’ila sun karya dokokinka suka kuma juya maka baya, sun ƙi yi maka biyayya. “Saboda haka la’anoni da rantsuwar hukunce-hukuncen da suke a rubuce a cikin Dokar Musa, bawan Allah, sun kama mu domin mun yi maka zunubi.
И сав Израиљ преступи закон Твој, и одступи да не слуша глас Твој; зато се изли на нас проклетство и заклетва написана у закону Мојсија, слуге Божијег, јер Му згрешисмо.
12 Ka cika kalmomin da ka yi a kanmu da kuma a kan masu mulkinmu ta wurin kawo mana babban bala’i. A duniya duka ba a taɓa yin wani abu kamar yadda aka yi wa Urushalima ba.
И Он потврди речи своје које је говорио за нас и за судије наше, које су нам судиле, пустивши на нас зло велико, да тако не би под свим небом како би у Јерусалиму.
13 Kamar yadda yake a rubuce cikin Dokar Musa, dukan wannan bala’i ya sauko a kanmu, duk da haka ba mu nemi tagomashin Ubangiji Allahnmu ta wurin barin aikatawa zunubanmu, mu kuma mai da hankali a kan gaskiyarka ba.
Како је писано у закону Мојсијевом, све то зло дође на нас, и опет се не молисмо Господу Богу свом да бисмо се вратили од безакоња свог и пазили на истину Твоју.
14 Ubangiji bai yi wata-wata wajen kawo mana bala’i ba, domin Ubangiji Allahnmu mai adalci ne a cikin dukan abin da yake yi; duk da haka ba mu yi masa biyayya ba.
И Господ наста око зла и наведе га на нас; јер је праведан Господ Бог наш у свим делима својим која чини, јер не слушасмо глас Његов.
15 “Yanzu, ya Ubangiji Allahnmu, wanda ya fito da mutanensa daga Masar ta hannu mai ƙarfi wanda kuma ya yi wa kansa sunan da ya dawwama har yă zuwa yau, mun yi zunubi, mun yi abin da ba daidai ba.
Али сада, Господе Боже наш, који си извео народ свој из земље мисирске руком крепком, и стекао си себи име, како је данас, згрешисмо, безбожни бисмо.
16 Ya Ubangiji, ta wurin kiyaye dukan ayyukanka na adalci, ka huce daga fushinka da hukuncinka da ka yi a kan Urushalima, birninka, tudunka mai tsarki. Zunubinmu da laifofin iyayenmu sun mai da Urushalima da kuma mutanenka abin ba’a ga dukan waɗanda suke kewaye da mu.
Господе, по свој правди Твојој нека се одврати гнев Твој и јарост Твоја од града Твог Јерусалима, свете горе Твоје; јер са греха наших и с безакоња отаца наших Јерусалим и Твој народ поста руг у свих који су око нас.
17 “Yanzu, ya Allahnmu, ka ji addu’o’i da koke-koken bayinka. Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka duba da rahama wurinka mai tsarki da ya zama kango.
Сада дакле послушај, Боже наш, молитву слуге свог и молбе његове, и обасјај лицем својим опустелу светињу своју, Господа ради.
18 Ka kasa kunne, ya Allah, ka kuma ji; ka buɗe idanunka ka kuma ga yadda birninka ya zama kango, birnin da yake ɗauke da Sunanka. Ba cewa muna roƙonka saboda mu masu adalci ba ne, amma saboda girman jinƙanka.
Боже мој, пригни ухо своје, и чуј; отвори очи своје, и види пустош нашу и град, на који је призвано име Твоје, јер не ради своје правде него ради милости Твоје падамо пред Тобом молећи се.
19 Ya Ubangiji, ka saurara! Ya Ubangiji ka gafarta! Ya Ubangiji, ka ji ka kuma yi wani abu! Saboda sunanka, ya Allahna, kada ka yi jinkiri, domin da sunanka ake kiran birninka da jama’arka.”
Господе услиши, Господе опрости, Господе пази и учини, не часи себе ради Боже мој, јер је Твоје име призвано на овај град и на Твој народ.
20 Yayinda da nake magana da addu’a, ina furta zunubina da zunubin mutanena Isra’ila ina miƙa koke-kokena ga Ubangiji Allahna saboda tudunsa mai tsarki,
А док ја још говорах и мољах се и исповедах грех свој и грех народа свог Израиља, и падах молећи се пред Господом Богом својим за свету гору Бога свог,
21 yayinda nake cikin addu’a, sai Jibra’ilu, mutumin nan da na gani a wahayin da ya wuce, ya zo wurina gaggauce wajen lokacin yin hadaya ta yamma.
Док још говорах молећи се, онај човек Гаврило, ког видех пре у утвари, долете брзо и дотаче ме се о вечерњој жртви.
22 Ya umarce ni ya kuma ce mini, “Daniyel, yanzu na zo domin in ba ka hikima da ganewa.
И научи ме и говори са мном и рече: Данило, сада изиђох да те уразумим.
23 Da zarar ka fara addu’a, an amsa, wadda na zo in faɗa maka, gama ana ƙaunar ka sosai. Saboda haka, ka yi lura da saƙon ka kuma fahimci wahayin.
У почетку молитве твоје изиђе реч, и ја дођох да ти кажем, јер си мио; зато слушај реч, и разуми утвару.
24 “An ƙayyade wa jama’arka da tsattsarkan birninka shekara ɗari huɗu da tasa’in domin a kawo ƙarshen laifi da zunubi, domin a yi kafarar laifi, sa’an nan a shigo da adalci madawwami, a rufe wahayi da annabci, a tsarkake haikali.
Седамдесет је недеља одређено твом народу и твом граду светом да се сврши преступ и да нестане греха и да се очисти безакоње и да се доведе вечна правда, и да се запечати утвара и пророштво, и да се помаже Свети над светима.
25 “Sai ka sani ka kuma fahimci wannan; Tun daga sa’ad da aka kafa doka don a maido a kuma sāke gina Urushalima har sai Shafaffen nan, mai mulki, ya zo, za a yi shekara arba’in da tara, da shekara ɗari huɗu da talatin da huɗu. Za a sāke gina ta a yi mata tituna da mafaka.
Зато знај и разуми: Откада изиђе реч да се Јерусалим опет сазида до помазаника војводе биће седам недеља, и шездесет и две недеље да се опет пограде улице и зидови, и то у тешко време.
26 Bayan shekara ɗari huɗu da talatin da huɗu, za a datse Shafaffen nan zai kuma kasance ba shi da kome. Mutanen mai mulkin za su zo su hallaka birnin da kuma wuri mai tsarki. Ƙarshen zai zo kamar rigyawa. Yaƙi zai ci gaba har ƙarshe, a kuma hallakar kamar yadda aka ƙaddara.
А после те шездесет и две недеље погубљен ће бити помазаник и ништа му неће остати; народ ће војводин доћи и разорити град и светињу; и крај ће му бити с потопом, и одређено ће пустошење бити до свршетка рата.
27 Zai tabbatar da alkawari da mutane masu yawa har na shekara bakwai. A tsakiyar bakwai ɗin nan ɗaya zai kawo ƙarshen duk wata hadaya da baiko. Kuma a kusurwar haikali zai sa abin ƙyama mai kawo hallaka, har sai ƙarshen da aka ƙaddara ya auko wa wanda ya sa abin ƙyama.”
И утврдиће завет с многима за недељу дана, а у половину недеље укинуће жртву и принос; и крилима мрским, која пустоше, до свршетка одређеног излиће се на пустош.