< Daniyel 9 >

1 A shekara ta fari da mulkin Dariyus ɗan Zerzes (wanda yake Bamediye), wanda aka mai da shi sarki a masarautar Babiloniyawa
Ngomnyaka wokuqala kaDariyusi indodana kaAhasuwerusi, owenzalo yamaMede, owenziwa waba yinkosi phezu kombuso wamaKhaladiya,
2 a shekara ta farko ta mulkinsa, ni, Daniyel na gane daga cikin littattafai, bisa ga maganar Ubangiji da aka faɗa wa annabi Irmiya, cewa zaman Urushalima kango zai kai shekara saba’in.
ngomnyaka wokuqala wokubusa kwakhe, mina Daniyeli ngaqedisisa ngezincwadi inani leminyaka, ilizwi leNkosi eleza ngayo kuJeremiya umprofethi, ukugcwalisa iminyaka engamatshumi ayisikhombisa encithakalweni zeJerusalema.
3 Sai na juya wurin Ubangiji Allah na roƙe shi ta wurin addu’a da koke-koke, cikin azumi, ina saye da tsummoki, na kuma zauna a cikin toka.
Ngasengikhangelisa ubuso bami kuyo iNkosi uNkulunkulu, ukudinga ngomkhuleko, lokuncenga, ngokuzila ukudla, lesaka, lomlotha.
4 Na yi addu’a ga Ubangiji Allahna na furta laifina. “Ya Ubangiji, mai alfarma da kuma Allah mai banrazana, wanda yake cika alkawarinsa na ƙauna ga duk wanda ya ƙaunace shi ya kuma kiyaye dokokinsa,
Ngasengikhuleka eNkosini uNkulunkulu wami, ngenza uvumo, ngathi: Hawu Nkosi, uNkulunkulu omkhulu lowesabekayo, ogcina isivumelwano lomusa kwabamthandayo lakulabo abagcina imilayo yakhe.
5 mun yi zunubi muka kuma yi ba daidai ba. Mu mugaye ne da kuma’yan tawaye; mun juya wa umarninka da shari’unka baya.
Sonile, senza okubi, senza ngenkohlakalo, senza umvukela, ngokuphambuka emilayweni yakho lezahlulelweni zakho.
6 Ba mu saurari bayinka annabawa ba, waɗanda suka yi magana a sunanka ga sarakunanmu da masu mulkinmu da iyayenmu, da kuma dukan mutanen ƙasa.
Futhi kasilalelanga izinceku zakho abaprofethi, ezikhulume ebizweni lakho emakhosini ethu, iziphathamandla zethu, labobaba, lakibo bonke abantu belizwe.
7 “Ubangiji, kai mai adalci ne, amma a yau kunya ta rufe mu, mutanen Yahuda da mutanen Urushalima da na dukan Isra’ila, waɗanda suke kusa da kuma nesa, a dukan ƙasashen da ka warwatsa mu saboda rashin amincinmu a gare ka.
Nkosi, kukhona ukulunga kuwe, kodwa kithi ukusanganiseka kobuso, njengalolusuku; ebantwini bakoJuda, lakubahlali beJerusalema, lakuIsrayeli wonke, abaseduze labakhatshana, kuwo wonke amazwe lapho obaxotshele khona, ngenxa yesiphambeko abaphambeka ngaso bemelene lawe.
8 Ya Ubangiji, mu da sarakunanmu, da masu mulkinmu da iyayenmu kunya ta rufe mu saboda mun yi maka zunubi.
Nkosi, kukhona kithi ukusanganiseka kobuso, emakhosini ethu, eziphathamandleni zethu, lakubobaba, ngoba sonile simelene lawe.
9 Ubangiji Allahnmu mai jinƙai ne, mai gafartawa ne kuma, ko da yake mun yi masa tawaye;
ENkosini uNkulunkulu wethu kukhona izisa lezintethelelo; lanxa siyivukele.
10 ba mu yi biyayya ga Ubangiji Allahnmu ba, ba mu kuma kiyaye shari’unsa da ya ba mu ta wuri bayinsa annabawa ba.
Futhi kasilalelanga ilizwi leNkosi uNkulunkulu wethu, ukuthi sihambe emilayweni yakhe, ayibeka phambi kwethu ngesandla sezinceku zakhe abaprofethi.
11 Dukan Isra’ila sun karya dokokinka suka kuma juya maka baya, sun ƙi yi maka biyayya. “Saboda haka la’anoni da rantsuwar hukunce-hukuncen da suke a rubuce a cikin Dokar Musa, bawan Allah, sun kama mu domin mun yi maka zunubi.
Yebo, uIsrayeli wonke weqile umlayo wakho, ngokuphambuka, ukuze bangalaleli ilizwi lakho; ngakho isiqalekiso sithululelwe phezu kwethu, lesifungo esibhalwe emlayweni kaMozisi inceku kaNkulunkulu, ngoba sonile kuye.
12 Ka cika kalmomin da ka yi a kanmu da kuma a kan masu mulkinmu ta wurin kawo mana babban bala’i. A duniya duka ba a taɓa yin wani abu kamar yadda aka yi wa Urushalima ba.
Futhi uwaqinisile amazwi akhe, awakhuluma emelene lathi, njalo emelene labehluleli bethu abasehlulelayo, ngokusehlisela ububi obukhulu, ngoba ngaphansi kwamazulu wonke kakuzanga kwenziwe okunjengokwenziwe eJerusalema.
13 Kamar yadda yake a rubuce cikin Dokar Musa, dukan wannan bala’i ya sauko a kanmu, duk da haka ba mu nemi tagomashin Ubangiji Allahnmu ta wurin barin aikatawa zunubanmu, mu kuma mai da hankali a kan gaskiyarka ba.
Njengoba kubhaliwe emlayweni kaMozisi, bonke lobububi busehlele. Kanti kasincenganga ubuso beNkosi uNkulunkulu wethu, ukuze siphenduke eziphambekweni zethu, siqedisise iqiniso lakho.
14 Ubangiji bai yi wata-wata wajen kawo mana bala’i ba, domin Ubangiji Allahnmu mai adalci ne a cikin dukan abin da yake yi; duk da haka ba mu yi masa biyayya ba.
Ngakho iNkosi yalinda phezu kobubi, yabehlisela phezu kwethu; ngoba iNkosi uNkulunkulu wethu ilungile emisebenzini yayo yonke eyenzayo, ngoba singalalelanga ilizwi layo.
15 “Yanzu, ya Ubangiji Allahnmu, wanda ya fito da mutanensa daga Masar ta hannu mai ƙarfi wanda kuma ya yi wa kansa sunan da ya dawwama har yă zuwa yau, mun yi zunubi, mun yi abin da ba daidai ba.
Khathesi-ke, Nkosi Nkulunkulu wethu, owakhupha abantu bakho elizweni leGibhithe ngesandla esilamandla, wazenzela ibizo, njengalamuhla; sonile, senze okubi.
16 Ya Ubangiji, ta wurin kiyaye dukan ayyukanka na adalci, ka huce daga fushinka da hukuncinka da ka yi a kan Urushalima, birninka, tudunka mai tsarki. Zunubinmu da laifofin iyayenmu sun mai da Urushalima da kuma mutanenka abin ba’a ga dukan waɗanda suke kewaye da mu.
Nkosi, njengakho konke ukulunga kwakho, ngiyakuncenga, kakuthi ulaka lwakho lentukuthelo yakho kuphendulwe emzini wakho iJerusalema, intaba yakho engcwele. Ngoba ngenxa yezono zethu, langeziphambeko zabobaba, iJerusalema labantu bakho sebelihlazo kubo bonke abasihanqileyo.
17 “Yanzu, ya Allahnmu, ka ji addu’o’i da koke-koken bayinka. Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka duba da rahama wurinka mai tsarki da ya zama kango.
Khathesi-ke, Nkulunkulu wethu, zwana umkhuleko wenceku yakho, lokuncenga kwayo, wenze ubuso bakho bukhanye endaweni yakho engcwele esilunxiwa, ngenxa yeNkosi.
18 Ka kasa kunne, ya Allah, ka kuma ji; ka buɗe idanunka ka kuma ga yadda birninka ya zama kango, birnin da yake ɗauke da Sunanka. Ba cewa muna roƙonka saboda mu masu adalci ba ne, amma saboda girman jinƙanka.
Nkulunkulu wami, beka indlebe yakho, uzwe; vula amehlo akho, ubone ukuchitheka kwethu, lomuzi obizwa ngebizo lakho; ngoba kasiwisi ukuncenga kwethu phambi kwakho ngenxa yokulunga kwethu, kodwa ngenxa yezihawu zakho ezinkulu.
19 Ya Ubangiji, ka saurara! Ya Ubangiji ka gafarta! Ya Ubangiji, ka ji ka kuma yi wani abu! Saboda sunanka, ya Allahna, kada ka yi jinkiri, domin da sunanka ake kiran birninka da jama’arka.”
Nkosi, zwana! Nkosi, thethelela! Nkosi, lalela wenze, ungalibali; ngenxa yakho, Nkulunkulu wami; ngoba umuzi wakho labantu bakho kubizwa ngebizo lakho.
20 Yayinda da nake magana da addu’a, ina furta zunubina da zunubin mutanena Isra’ila ina miƙa koke-kokena ga Ubangiji Allahna saboda tudunsa mai tsarki,
Kwathi ngisakhuluma, ngikhuleka, ngivuma isono sami lesono sabantu bakithi uIsrayeli, ngiwisa ukuncenga kwami phambi kweNkosi uNkulunkulu wami ngenxa yentaba engcwele kaNkulunkulu wami;
21 yayinda nake cikin addu’a, sai Jibra’ilu, mutumin nan da na gani a wahayin da ya wuce, ya zo wurina gaggauce wajen lokacin yin hadaya ta yamma.
yebo, ngisakhuluma ngomkhuleko, ngitsho lowomuntu uGabriyeli, engangimbone embonweni ekuqaleni, esenziwe waphapha masinyane, wangithinta ngesikhathi somnikelo wakusihlwa.
22 Ya umarce ni ya kuma ce mini, “Daniyel, yanzu na zo domin in ba ka hikima da ganewa.
Wangazisa, wakhuluma lami, wathi: Daniyeli, khathesi ngiphumele ukuzakupha inhlakanipho lokuqedisisa.
23 Da zarar ka fara addu’a, an amsa, wadda na zo in faɗa maka, gama ana ƙaunar ka sosai. Saboda haka, ka yi lura da saƙon ka kuma fahimci wahayin.
Ekuqaliseni kokuncenga kwakho ilizwi laphuma, mina-ke ngize ukukutshela lona; ngoba uthandiwe kakhulu. Ngakho qedisisa loludaba, unakane ngalumbono.
24 “An ƙayyade wa jama’arka da tsattsarkan birninka shekara ɗari huɗu da tasa’in domin a kawo ƙarshen laifi da zunubi, domin a yi kafarar laifi, sa’an nan a shigo da adalci madawwami, a rufe wahayi da annabci, a tsarkake haikali.
Amaviki angamatshumi ayisikhombisa amiswe phezu kwabantu bakho laphezu komuzi wakho ongcwele, ukuqeda isiphambeko, lokuphelelisa izono, lokwenzela isiphambeko inhlawulo yokuthula, lokungenisa ukulunga okulaphakade, lokuphawula umbono lesiprofetho, lokugcoba ingcwele yezingcwele.
25 “Sai ka sani ka kuma fahimci wannan; Tun daga sa’ad da aka kafa doka don a maido a kuma sāke gina Urushalima har sai Shafaffen nan, mai mulki, ya zo, za a yi shekara arba’in da tara, da shekara ɗari huɗu da talatin da huɗu. Za a sāke gina ta a yi mata tituna da mafaka.
Yazi-ke uqedisise: Kusukela ekuphumeni kwelizwi lokubuyisela lokwakha iJerusalema kuze kube kuMesiya iNkosana, kungamaviki ayisikhombisa, lamaviki angamatshumi ayisithupha lambili. Kuzabuya kwakhiwe izitalada lemifolo, kodwa ngokuhlupheka kwezikhathi.
26 Bayan shekara ɗari huɗu da talatin da huɗu, za a datse Shafaffen nan zai kuma kasance ba shi da kome. Mutanen mai mulkin za su zo su hallaka birnin da kuma wuri mai tsarki. Ƙarshen zai zo kamar rigyawa. Yaƙi zai ci gaba har ƙarshe, a kuma hallakar kamar yadda aka ƙaddara.
Langemva kwamaviki angamatshumi ayisithupha lambili uMesiya uzaqunywa, kodwa kungenzelwa yena; lesizwe sesiphathamandla esizakuza sizachitha umuzi lendawo engcwele; lokuphela kwawo kuzakuba ngozamcolo; njalo kuze kube sekupheleni kuzakuba khona impi, kumiswe izincithakalo.
27 Zai tabbatar da alkawari da mutane masu yawa har na shekara bakwai. A tsakiyar bakwai ɗin nan ɗaya zai kawo ƙarshen duk wata hadaya da baiko. Kuma a kusurwar haikali zai sa abin ƙyama mai kawo hallaka, har sai ƙarshen da aka ƙaddara ya auko wa wanda ya sa abin ƙyama.”
Njalo uzaqinisa isivumelwano labanengi okweviki eyodwa; laphakathi kweviki uzakwenza kukhawule umhlatshelo lomnikelo; laphezu kophiko lwezinengiso kuzakuba lomchithi, ngitsho kuze kube sekupheleni, lokumisiweyo kuzathululelwa phezu konxiwa.

< Daniyel 9 >