< Daniyel 9 >

1 A shekara ta fari da mulkin Dariyus ɗan Zerzes (wanda yake Bamediye), wanda aka mai da shi sarki a masarautar Babiloniyawa
In the first year of Darius, the son of Ahasuerus, of the race of the Medes, who became king over the realm of the Chaldaeans,
2 a shekara ta farko ta mulkinsa, ni, Daniyel na gane daga cikin littattafai, bisa ga maganar Ubangiji da aka faɗa wa annabi Irmiya, cewa zaman Urushalima kango zai kai shekara saba’in.
in the first year of his reign, I Daniel attentively considered in the Books the number of the years, concerning which the word of Jehovah came to Jeremiah the prophet, that Jerusalem should remain in ruins till they were accomplished, namely, seventy years.
3 Sai na juya wurin Ubangiji Allah na roƙe shi ta wurin addu’a da koke-koke, cikin azumi, ina saye da tsummoki, na kuma zauna a cikin toka.
And I set my face toward God, the Lord, and made prayers and supplications, with fasting and sackcloth and ashes.
4 Na yi addu’a ga Ubangiji Allahna na furta laifina. “Ya Ubangiji, mai alfarma da kuma Allah mai banrazana, wanda yake cika alkawarinsa na ƙauna ga duk wanda ya ƙaunace shi ya kuma kiyaye dokokinsa,
And I prayed to Jehovah, my God, and made my confession, and said, O Lord, the great and terrible God, who keepeth the covenant and mercy to them that love him and keep his commandments!
5 mun yi zunubi muka kuma yi ba daidai ba. Mu mugaye ne da kuma’yan tawaye; mun juya wa umarninka da shari’unka baya.
We have sinned, and have committed iniquity, and have done wickedly, and have rebelled, even by departing from thy precepts and thy statutes.
6 Ba mu saurari bayinka annabawa ba, waɗanda suka yi magana a sunanka ga sarakunanmu da masu mulkinmu da iyayenmu, da kuma dukan mutanen ƙasa.
Neither have we hearkened to thy servants, the prophets, who spake in thy name to our kings, our princes, and our fathers, and to all the people of the land.
7 “Ubangiji, kai mai adalci ne, amma a yau kunya ta rufe mu, mutanen Yahuda da mutanen Urushalima da na dukan Isra’ila, waɗanda suke kusa da kuma nesa, a dukan ƙasashen da ka warwatsa mu saboda rashin amincinmu a gare ka.
To thee, O Lord, belongeth righteousness, but to us confusion of face, as at this day; to the men of Judah, and to the inhabitants of Jerusalem, and to all Israel, to those that are near and to those that are far off through all the countries whither thou hast driven them because of their trespass which they have trespassed against thee.
8 Ya Ubangiji, mu da sarakunanmu, da masu mulkinmu da iyayenmu kunya ta rufe mu saboda mun yi maka zunubi.
O Lord, to us belongeth confusion of face, to our kings, to our princes, and to our fathers, because we have sinned against thee.
9 Ubangiji Allahnmu mai jinƙai ne, mai gafartawa ne kuma, ko da yake mun yi masa tawaye;
Yet with the Lord our God is mercy and forgiveness. For we have rebelled against him,
10 ba mu yi biyayya ga Ubangiji Allahnmu ba, ba mu kuma kiyaye shari’unsa da ya ba mu ta wuri bayinsa annabawa ba.
and have not obeyed the voice of Jehovah our God, to walk in his laws, which he set before us by his servants, the prophets.
11 Dukan Isra’ila sun karya dokokinka suka kuma juya maka baya, sun ƙi yi maka biyayya. “Saboda haka la’anoni da rantsuwar hukunce-hukuncen da suke a rubuce a cikin Dokar Musa, bawan Allah, sun kama mu domin mun yi maka zunubi.
Yea, all Israel have transgressed thy law, and turned away, so as not to obey thy voice; therefore the curse is poured out upon us, and the oath that is written in the law of Moses, the servant of God, because we have sinned against him.
12 Ka cika kalmomin da ka yi a kanmu da kuma a kan masu mulkinmu ta wurin kawo mana babban bala’i. A duniya duka ba a taɓa yin wani abu kamar yadda aka yi wa Urushalima ba.
And he hath fulfilled his word which he spake against us, and against our judges who judged us, by bringing great calamity upon us; for under the whole heaven hath it not been done as hath been done to Jerusalem.
13 Kamar yadda yake a rubuce cikin Dokar Musa, dukan wannan bala’i ya sauko a kanmu, duk da haka ba mu nemi tagomashin Ubangiji Allahnmu ta wurin barin aikatawa zunubanmu, mu kuma mai da hankali a kan gaskiyarka ba.
As it is written in the law of Moses, all this evil came upon us. For we made not our prayer to Jehovah our God, that we might turn from our iniquities, and give heed to thy truth.
14 Ubangiji bai yi wata-wata wajen kawo mana bala’i ba, domin Ubangiji Allahnmu mai adalci ne a cikin dukan abin da yake yi; duk da haka ba mu yi masa biyayya ba.
Therefore hath Jehovah our God kept his mind upon the evil, and brought it upon us; for Jehovah our God is righteous in all his works which he doeth; for we obeyed not his voice.
15 “Yanzu, ya Ubangiji Allahnmu, wanda ya fito da mutanensa daga Masar ta hannu mai ƙarfi wanda kuma ya yi wa kansa sunan da ya dawwama har yă zuwa yau, mun yi zunubi, mun yi abin da ba daidai ba.
And now, O Lord our God, that broughtest thy people forth from the land of Egypt with a mighty hand, and madest thee a name such as it is at this day, we have sinned, we have done wickedly.
16 Ya Ubangiji, ta wurin kiyaye dukan ayyukanka na adalci, ka huce daga fushinka da hukuncinka da ka yi a kan Urushalima, birninka, tudunka mai tsarki. Zunubinmu da laifofin iyayenmu sun mai da Urushalima da kuma mutanenka abin ba’a ga dukan waɗanda suke kewaye da mu.
O Lord, according to all thy goodness, let thine anger and thy fury, I beseech thee, be turned away from thy city Jerusalem, thy holy mountain! for because of our iniquities, and the iniquities of our fathers, Jerusalem and thy people are become a reproach to all that are about us.
17 “Yanzu, ya Allahnmu, ka ji addu’o’i da koke-koken bayinka. Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka duba da rahama wurinka mai tsarki da ya zama kango.
Now, therefore, O our God, hear the prayer of thy servant, and his supplications, and cause thy face to shine upon thy sanctuary that is desolate, for the Lord's sake!
18 Ka kasa kunne, ya Allah, ka kuma ji; ka buɗe idanunka ka kuma ga yadda birninka ya zama kango, birnin da yake ɗauke da Sunanka. Ba cewa muna roƙonka saboda mu masu adalci ba ne, amma saboda girman jinƙanka.
O my God, incline thine ear, and hear! open thine eyes, and behold our desolations, and the city which is called by thy name! for we do not present our supplications before thee on account of our righteousness, but on account of thy great mercy.
19 Ya Ubangiji, ka saurara! Ya Ubangiji ka gafarta! Ya Ubangiji, ka ji ka kuma yi wani abu! Saboda sunanka, ya Allahna, kada ka yi jinkiri, domin da sunanka ake kiran birninka da jama’arka.”
O Lord, hear! O Lord, forgive! O Lord, hearken and do! Defer not, for thine own sake, O my God! For thy city and thy people are called by thy name.
20 Yayinda da nake magana da addu’a, ina furta zunubina da zunubin mutanena Isra’ila ina miƙa koke-kokena ga Ubangiji Allahna saboda tudunsa mai tsarki,
And while I was speaking, and praying, and confessing my sin, and the sin of my people Israel, and presenting my supplication before Jehovah my God, for the holy mountain of my God,
21 yayinda nake cikin addu’a, sai Jibra’ilu, mutumin nan da na gani a wahayin da ya wuce, ya zo wurina gaggauce wajen lokacin yin hadaya ta yamma.
yea, while I was speaking in prayer, the man Gabriel, whom I had seen in the former vision, came, weary with running, and reached me about the time of the evening oblation.
22 Ya umarce ni ya kuma ce mini, “Daniyel, yanzu na zo domin in ba ka hikima da ganewa.
And he instructed me, and talked with me, and said: Daniel, I am now come forth to give thee understanding.
23 Da zarar ka fara addu’a, an amsa, wadda na zo in faɗa maka, gama ana ƙaunar ka sosai. Saboda haka, ka yi lura da saƙon ka kuma fahimci wahayin.
At the beginning of thy supplication a word went forth, and I am come to show it thee; for thou art greatly beloved; therefore give heed to the word, and consider the vision.
24 “An ƙayyade wa jama’arka da tsattsarkan birninka shekara ɗari huɗu da tasa’in domin a kawo ƙarshen laifi da zunubi, domin a yi kafarar laifi, sa’an nan a shigo da adalci madawwami, a rufe wahayi da annabci, a tsarkake haikali.
Seventy weeks are appointed for thy people, and for thy holy city, to complete the iniquity, and to fill up the measure of the sins, and to expiate the guilt, and to bring in everlasting righteousness, and to seal vision and prophet, and to anoint a holy of holies.
25 “Sai ka sani ka kuma fahimci wannan; Tun daga sa’ad da aka kafa doka don a maido a kuma sāke gina Urushalima har sai Shafaffen nan, mai mulki, ya zo, za a yi shekara arba’in da tara, da shekara ɗari huɗu da talatin da huɗu. Za a sāke gina ta a yi mata tituna da mafaka.
Know, therefore, and understand! From the going forth of the word that Jerusalem should be restored and built till an anointed one, a prince, are seven weeks; and during sixty-two weeks it shall be restored and built with streets and moats, yet in troublous times.
26 Bayan shekara ɗari huɗu da talatin da huɗu, za a datse Shafaffen nan zai kuma kasance ba shi da kome. Mutanen mai mulkin za su zo su hallaka birnin da kuma wuri mai tsarki. Ƙarshen zai zo kamar rigyawa. Yaƙi zai ci gaba har ƙarshe, a kuma hallakar kamar yadda aka ƙaddara.
And after the sixty-two weeks shall an anointed one be cut off, and there shall not be to him [[a successor]]; and the city and the sanctuary shall be destroyed by the people of a prince that shall come, whose end will be as in a flood; and to the end shall be war, decreed desolations.
27 Zai tabbatar da alkawari da mutane masu yawa har na shekara bakwai. A tsakiyar bakwai ɗin nan ɗaya zai kawo ƙarshen duk wata hadaya da baiko. Kuma a kusurwar haikali zai sa abin ƙyama mai kawo hallaka, har sai ƙarshen da aka ƙaddara ya auko wa wanda ya sa abin ƙyama.”
And he will establish a covenant with many for one week, and during half a week he will cause sacrifice and oblation to cease, and upon the wing of abominations shall come the destroyer, until decreed destruction be poured out on the destroyer.

< Daniyel 9 >