< Daniyel 8 >
1 A shekara ta uku ta mulkin sarki Belshazar, ni, Daniyel, na ga wahayi, bayan wancan da na riga gani.
Ngomnyaka wesithathu wokubusa kwenkosi uBelishazari kwabonakala umbono kimi, mina Daniyeli, emva kwalowo owabonakala kimi kuqala.
2 A cikin wahayin, na ga kaina a mafakar Shusha a yankin Elam; a wahayin na ga ina a bakin Kogin Ulai.
Ngabona-ke embonweni; kwasekusithi, sengibonile, ngiseShushani isigodlo, esisesabelweni seElamu; ngasengibona embonweni, mina ngangingasemfuleni iUlayi.
3 Na ɗaga ido, a gabana kuwa sai ga rago mai ƙahoni biyu, yana tsaye a gefen mashigin kogin, ƙahonin kuma suna da tsawo. Ɗaya daga cikin ƙahonin ya fi ɗayan tsawo. Wanda ya fi tsawon shi ne ya tsiro daga baya.
Ngasengiphakamisa amehlo ami, ngabona, khangela-ke, kwema phambi komfula inqama elempondo ezimbili. Impondo zombili zaziphakeme, kodwa olunye lwaluphakeme okwedlula olunye, njalo oluphakemeyo lwenyuka muva.
4 Na lura da ragon sa’ad da ya kai karo wajen yamma da arewa da kudu. Babu wata dabbar da ta iya ƙarawa da shi, babu kuma wanda ya iya kuɓuta daga ikonsa. Ya yi yadda ya ga dama, ya kuma zama mai girma.
Ngabona inqama ihlaba ikhangele ngentshonalanga langenyakatho langeningizimu; ukuze kungabi lezinyamazana ezingema phambi kwayo, njalo kungekho ongophula esandleni sayo; kodwa yenza njengentando yayo, yazikhulisa.
5 Yayinda nake tunani game da wannan, farat ɗaya sai ga bunsurun da yake da sanannen ƙaho tsakanin idanunsa ya ɓullo daga wajen yamma, yana ratsa dukan duniya ba ya ko taɓa ƙasa.
Kwathi mina ngisacabanga, khangela-ke, kweza impongo yembuzi ivela ngentshonalanga phezu kobuso bomhlaba wonke, njalo kayiwuthintanga umhlabathi. Njalo limpongo yayilophondo olunanzelelekayo phakathi laphakathi kwamehlo ayo.
6 Ya zo wajen rago mai ƙahoni biyu ɗin nan da na riga na gani tsaye a gefen mashigin kogin nan ya tasar masa da fushi mai zafi.
Yasisiza enqameni eyayilempondo ezimbili, engangiyibone imi phambi komfula, yagijimela kuyo ngolaka lwamandla ayo.
7 Na ga ya zo kusa da ragon, ya husata da shi ƙwarai, ya kai wa ragon hari. Ya kakkarya ƙahoninsa nan biyu. Ƙarfin ragon ya kāsa, bai iya kāre kansa daga bunsurun ba. Bunsurun ya buge shi ƙasa ya tattake shi. Ba wanda ya iya ceton ragon daga bunsurun.
Ngasengiyibona isondela ngasenqameni, yathukuthela kakhulu imelene layo, yayitshaya inqama, yephula impondo zayo zombili. Kwakungaselamandla enqameni okuma phambi kwayo; kodwa impongo yayiwisela emhlabathini, yayinyathelela phansi; njalo kwakungekho owayengayophula inqama esandleni sayo.
8 Bunsurun kuwa ya ƙasaita, amma a ƙwanƙolin ikonsa sai aka karye babban ƙahonsa, kuma a wurin da ƙahon nan ya kasance waɗansu sanannun ƙahoni huɗu suka tsiro suna fuskantar kusurwoyin nan huɗu.
Ngakho impongo yembuzi yazikhulisa kakhulukazi; yathi isilamandla, uphondo olukhulu lwephuka; njalo endaweni yalo kwenyuka ezine ezinanzelelekayo ngasemimoyeni emine yamazulu.
9 Daga cikin ɗayansu kuma wani ƙaramin ƙaho ya fito, ya yi girma ya ƙasaita ƙwarai zuwa kudu da kuma gabas da wajen Kyakkyawar Ƙasa.
Njalo kolunye lwazo kwaphuma uphondo oluncinyane, olwakhula kakhulukazi, ngaseningizimu langasempumalanga langaselizweni elihle.
10 Ya yi girma sai da ya kai rundunar sammai, ya kuma fid da waɗansu rundunar taurari zuwa ƙasa ya kuma tattake su.
Lwaselukhula kwaze kwaba sebuthweni lamazulu; lwaseluwisela emhlabathini okwebutho lokwezinkanyezi, lwakunyathelela phansi.
11 Sai ya ɗora kansa ya zama mai girma kamar Sarkin runduna; sai aka ɗauke hadaya ta kullayaumi daga gare shi, aka kuma saukar da wurin masujadarsa ƙasa.
Yebo, lwazikhulisa kwaze kwaba sesiphathamandleni sebutho, langalo umhlatshelo oqhubekayo wasuswa, lendawo yendlu yaso engcwele yadilizelwa phansi.
12 Saboda tawaye, sai aka ba da rundunar tsarkaka da kuma hadayar ƙonawa ta kowace rana ga ƙahon. Sai ya yi watsi da gaskiya, ya yi abin da ya ga dama, ya kuwa yi nasara.
Kwasekunikelwa ibutho limelene lomhlatshelo oqhubekayo ngenxa yesiphambeko, laphosela emhlabathini iqiniso, lenza, laphumelela.
13 Sa’an nan na ji mai tsarkin nan yana magana, wani mai tsarki kuma ya ce da wancan, “Har yaushe wannan wahayi zai tabbata, wahayi game da hadaya ta kullayaumi, da tawayen da yake kawo lalacewa, da kuma miƙa wuri mai tsarki da kuma na rundunar da za a tattake a ƙarƙashin sawu?”
Ngasengisizwa ongcwele oyedwa ekhuluma, njalo omunye ongcwele wathi kulowo othile owakhulumayo: Koze kube nini uzakuba khona lumbono mayelana lomhlatshelo oqhubekayo, lesiphambeko sencithakalo, ukunikela indawo engcwele kanye lebutho ukuthi kunyathelelwe phansi?
14 Sai ya ce mini, “Zai ɗauki safiya da yamma 2,300; sa’an nan za a sāke tsarkake wuri mai tsarki.”
Wasesithi kimi: Kuze kube zintambama lekuseni okuzinkulungwane ezimbili lamakhulu amathathu; kube sekuhlanjululwa indawo engcwele.
15 Yayinda ni, Daniyel, nake duban wahayi ina ƙoƙari in fahimce shi, sai ga wani a gabana wanda ya yi kama da mutum.
Kwasekusithi mina Daniyeli sengiwubonile umbono ngadinga ukuqedisisa, khangela-ke, kwema phambi kwami okunjengesimo somuntu.
16 Sai na ji muryar wani mutum daga Ulai tana cewa, “Jibra’ilu, faɗa wa wannan mutum ma’anar wahayin.”
Ngasengisizwa ilizwi lomuntu phakathi kwezinkumbizeUlayi, elamemeza lathi: Gabriyeli, yenza lo aqedisise umbono.
17 Da ya zo kusa da inda nake tsaye, na firgita na kuma fāɗi rubda ciki. Ya ce da ni “Ɗan mutum, ka gane da cewa wannan wahayi yana magana ne a kan kwanakin ƙarshe.”
Wasesiza eceleni kwalapho engangimi khona. Esefikile, ngethuka, ngathi mbo ngobuso bami. Kodwa wathi kimi: Qedisisa, ndodana yomuntu, ngoba umbono ungowesikhathi sokucina.
18 Yayinda yake magana da ni, barci mai nauyi ya kwashe ni, da nake kwance rubda ciki. Sai ya taɓa ni ya kuma tashe ni tsaye.
Kwathi esakhuluma lami, ngangilele ubuthongo obukhulu ngobuso bami emhlabathini; kodwa wangithinta, wangimisa endaweni yami yokuma.
19 Sai ya ce, “Zan faɗa maka abin da zai faru a lokacin fushi, saboda wahayin yana magana ne a kan lokacin da aka ƙayyade na ƙarshe.
Wasesithi: Khangela, ngizakwenza wazi okuzakuba sekupheleni kwentukuthelo, ngoba ukucina kuzakuba ngesikhathi esimisiweyo.
20 Rago mai ƙahoni biyu da ka gani, yana a madadin sarakunan Medes da Farisa ne.
Inqama oyibonileyo elempondo ezimbili ngamakhosi eMede lePerisiya.
21 Bunsurun kuwa sarkin Girka ne, kuma babban ƙahon da yake tsakanin idanunsa, sarki na farko ne.
Njalo impongo eyisiyephu iyinkosi yeGirisi, lophondo olukhulu oluphakathi laphakathi kwamehlo ayo luyinkosi yokuqala.
22 Ƙahoni huɗu da suka maya wannan da ya karye yana a madadin masarautu huɗu da za su tashi daga cikin al’ummarsa amma ba za su sami irin ikonsa ba.
Ngolwephukayo, njengoba kwema ezine endaweni yalo, kuzakuma imibuso emine kuso isizwe, kodwa hatshi ngamandla alo.
23 “Can wajen ƙarshe mulkinsu, sa’ad da muguntarsu ta kai intaha, wani mugun sarki mai rashin hankali, uban makirci, zai fito.
Njalo ekucineni kwemibuso yazo, lapho abaphambeki sebephelele, izakuma inkosi elukhuni ngobuso, eqedisisa imizekeliso.
24 Zai yi ƙarfi ƙwarai da gaske, amma ba da ikonsa ba. Zai jawo mummunar hallakarwa kuma zai yi nasara a duk abin da ya sa gaba. Zai hallakar da majiya ƙarfi da kuma tsarkaka.
Lamandla ayo azaqina, kodwa hatshi ngamandla ayo. Njalo izachitha ngokumangalisayo, iphumelele, yenze, ichithe abalamandla lesizwe sabangcwele.
25 Zai sa yaudara ta ƙara yin yawa, zai ɗaukaka kansa. Sa’ad da suke ji sun sami mafaka, zai hallaka mutane da yawa sa’an nan kuma yă fara gāba da Sarkin sarakuna. Duk da haka za a hallaka shi, amma ba da ikon mutum ba.
Langobuqili bayo izaphumelelisa inkohliso esandleni sayo, izikhulise enhliziyweni yayo, ichithe abanengi ngokuthula, futhi izamelana leNkosana yamakhosana, kodwa izakwephulwa kungelasandla.
26 “Wahayin nan na safiya da yamma da aka nuna maka gaskiya ne, amma ka ɓoye wahayin, gama ya shafi nan gaba mai tsawo ne.”
Njalo umbono wantambama lowekuseni olandisiweyo uliqiniso; wena-ke valela umbono, ngoba ungowensuku ezinengi.
27 Ni, Daniyel, na gaji matuƙa na kuma yi rashin lafiya na kwanaki masu yawa. Sa’an nan sai na tashi na ci gaba da hidimar sarki. Wahayin ya shige mini duhu, ya fi ƙarfin fahimtata.
Mina-ke Daniyeli, ngaphela amandla ngagula okwensuku ezithile; emva kwalokho ngasukuma, ngenza umsebenzi wenkosi; njalo ngamangala kakhulu ngombono, kodwa kakho owaqedisisayo.