< Daniyel 8 >
1 A shekara ta uku ta mulkin sarki Belshazar, ni, Daniyel, na ga wahayi, bayan wancan da na riga gani.
I Kong Belsazars Regerings tredje Aar viste der sig for mig, Daniel, et Syn, efter det, som havde vist sig for mig i Begyndelsen.
2 A cikin wahayin, na ga kaina a mafakar Shusha a yankin Elam; a wahayin na ga ina a bakin Kogin Ulai.
Og jeg saa i Synet, og det skete, idet jeg saa, at jeg var i Borgen Susan, i Landskabet Elam, og jeg saa i Synet, og jeg var ved Floden Ulaj.
3 Na ɗaga ido, a gabana kuwa sai ga rago mai ƙahoni biyu, yana tsaye a gefen mashigin kogin, ƙahonin kuma suna da tsawo. Ɗaya daga cikin ƙahonin ya fi ɗayan tsawo. Wanda ya fi tsawon shi ne ya tsiro daga baya.
Og jeg opløftede mine Øjne og saa, og se, en Væder stod lige for Floden, og den havde to Horn; og Hornene vare høje, og det ene højere end det andet, og det højeste voksede op sidst.
4 Na lura da ragon sa’ad da ya kai karo wajen yamma da arewa da kudu. Babu wata dabbar da ta iya ƙarawa da shi, babu kuma wanda ya iya kuɓuta daga ikonsa. Ya yi yadda ya ga dama, ya kuma zama mai girma.
Jeg saa, at Væderen stangede imod Vesten og Norden og Sønden, og der kunde intet Dyr staa for dens Ansigt, der var ej heller nogen, som kunde redde af dens Vold, og den gjorde efter sin Villie og blev mægtig.
5 Yayinda nake tunani game da wannan, farat ɗaya sai ga bunsurun da yake da sanannen ƙaho tsakanin idanunsa ya ɓullo daga wajen yamma, yana ratsa dukan duniya ba ya ko taɓa ƙasa.
Og jeg gav Agt, og se, en Gedebuk kom fra Vesten hen over al Jorden, og den rørte ikke ved Jorden; og Gedebukken havde et anseligt Horn imellem sine Øjne.
6 Ya zo wajen rago mai ƙahoni biyu ɗin nan da na riga na gani tsaye a gefen mashigin kogin nan ya tasar masa da fushi mai zafi.
Og den kom til Væderen, som havde de to Horn, og som jeg havde set staa lige for Floden, og den løb imod deri i sin Krafts Hidsighed.
7 Na ga ya zo kusa da ragon, ya husata da shi ƙwarai, ya kai wa ragon hari. Ya kakkarya ƙahoninsa nan biyu. Ƙarfin ragon ya kāsa, bai iya kāre kansa daga bunsurun ba. Bunsurun ya buge shi ƙasa ya tattake shi. Ba wanda ya iya ceton ragon daga bunsurun.
Og jeg saa den, at den kom nær hen til Væderen og blev forbitret paa den og slog Væderen og sønderbrød dens to Horn, og der var ingen Kraft i Væderen til at staa for dens Ansigt; og den kastede den til Jorden og nedtraadte den, og der var ingen, som kunde redde Væderen af dens Vold.
8 Bunsurun kuwa ya ƙasaita, amma a ƙwanƙolin ikonsa sai aka karye babban ƙahonsa, kuma a wurin da ƙahon nan ya kasance waɗansu sanannun ƙahoni huɗu suka tsiro suna fuskantar kusurwoyin nan huɗu.
Og Gedebukken blev saare mægtig; men som den stod i sin Styrke, blev det store Horn sønderbrudt, og i Stedet derfor opvoksede fire anselige Horn imod Himmelens fire Vejr;
9 Daga cikin ɗayansu kuma wani ƙaramin ƙaho ya fito, ya yi girma ya ƙasaita ƙwarai zuwa kudu da kuma gabas da wajen Kyakkyawar Ƙasa.
og fra det ene af dem fremskød eet Horn, i Førstningen lidet, men det blev overmaade stort imod Sønden og imod Østen og imod det herlige Land.
10 Ya yi girma sai da ya kai rundunar sammai, ya kuma fid da waɗansu rundunar taurari zuwa ƙasa ya kuma tattake su.
Og det blev stort, indtil Himmelens Hær, og det kastede nogle af Hæren og af Stjernerne til Jorden og nedtraadte dem.
11 Sai ya ɗora kansa ya zama mai girma kamar Sarkin runduna; sai aka ɗauke hadaya ta kullayaumi daga gare shi, aka kuma saukar da wurin masujadarsa ƙasa.
Ja, indtil Hærens Fyrste udstrakte det sin Magt og borttog fra ham den stadige Tjeneste, og hans Helligdoms Bolig blev nedkastet.
12 Saboda tawaye, sai aka ba da rundunar tsarkaka da kuma hadayar ƙonawa ta kowace rana ga ƙahon. Sai ya yi watsi da gaskiya, ya yi abin da ya ga dama, ya kuwa yi nasara.
Og en Hær skal hengives tillige med den stadige Tjeneste for Overtrædelsens Skyld; og det skal kaste Sandheden til Jorden og udføre det og have Lykke.
13 Sa’an nan na ji mai tsarkin nan yana magana, wani mai tsarki kuma ya ce da wancan, “Har yaushe wannan wahayi zai tabbata, wahayi game da hadaya ta kullayaumi, da tawayen da yake kawo lalacewa, da kuma miƙa wuri mai tsarki da kuma na rundunar da za a tattake a ƙarƙashin sawu?”
Derefter hørte jeg en hellig, som talte, og en anden hellig sagde til den, der talte: Paa hvor lang Tid gaar Synet om den stadige Tjeneste og Overtrædelsen, der bringer Ødelæggelse, at baade Helligdommen og Hæren skulle hengives til at nedtrædes?
14 Sai ya ce mini, “Zai ɗauki safiya da yamma 2,300; sa’an nan za a sāke tsarkake wuri mai tsarki.”
Og han sagde til mig: Indtil to Tusinde og tre Hundrede Aftener og Morgener, saa skal Helligdommen faa sin Ret igen.
15 Yayinda ni, Daniyel, nake duban wahayi ina ƙoƙari in fahimce shi, sai ga wani a gabana wanda ya yi kama da mutum.
Og det skete, der jeg, Daniel, saa Synet, at jeg søgte Forklaring, og se, der stod een for mig af Udseende som en Mand.
16 Sai na ji muryar wani mutum daga Ulai tana cewa, “Jibra’ilu, faɗa wa wannan mutum ma’anar wahayin.”
Og jeg hørte en Menneskerøst imellem Ulaj, og han raabte og sagde: Gabriel! forklar denne Synet!
17 Da ya zo kusa da inda nake tsaye, na firgita na kuma fāɗi rubda ciki. Ya ce da ni “Ɗan mutum, ka gane da cewa wannan wahayi yana magana ne a kan kwanakin ƙarshe.”
Og han kom hen, hvor jeg stod, og der han kom, blev jeg forfærdet og faldt paa mit Ansigt; og han sagde til mig: Giv Agt, du Menneskesøn! thi Synet gaar paa Endens Tid.
18 Yayinda yake magana da ni, barci mai nauyi ya kwashe ni, da nake kwance rubda ciki. Sai ya taɓa ni ya kuma tashe ni tsaye.
Og der han talte med mig, faldt jeg bedøvet paa mit Ansigt til Jorden; men han rørte ved mig og rejste mig op, hvor jeg stod.
19 Sai ya ce, “Zan faɗa maka abin da zai faru a lokacin fushi, saboda wahayin yana magana ne a kan lokacin da aka ƙayyade na ƙarshe.
Og han sagde: Se, jeg vil kundgøre dig, hvad der skal ske i Vredens sidste Tid; thi det gaar paa Endens bestemte Tid.
20 Rago mai ƙahoni biyu da ka gani, yana a madadin sarakunan Medes da Farisa ne.
Den Væder, som du saa, der havde de to Horn, er Kongerne af Medien og Persien.
21 Bunsurun kuwa sarkin Girka ne, kuma babban ƙahon da yake tsakanin idanunsa, sarki na farko ne.
Og den laadne Buk er Kongen af Grækenland; og det store Horn, som var imellem dens Øjne, er den første Konge.
22 Ƙahoni huɗu da suka maya wannan da ya karye yana a madadin masarautu huɗu da za su tashi daga cikin al’ummarsa amma ba za su sami irin ikonsa ba.
Og at det blev sønderbrudt, og at fire stode frem i Stedet for det, betyder, at fire Kongeriger skulle opstaa af Folket, men ikke med hans Kraft.
23 “Can wajen ƙarshe mulkinsu, sa’ad da muguntarsu ta kai intaha, wani mugun sarki mai rashin hankali, uban makirci, zai fito.
Og i deres Herredømmes sidste Tid, naar Overtræderne have gjort Maalet luldt, skal der opstaa en Konge, fræk af Ansigt og kyndig i Rænker.
24 Zai yi ƙarfi ƙwarai da gaske, amma ba da ikonsa ba. Zai jawo mummunar hallakarwa kuma zai yi nasara a duk abin da ya sa gaba. Zai hallakar da majiya ƙarfi da kuma tsarkaka.
Og hans Magt skal blive stærk, dog ikke ved hans Kraft, han skal anrette uhørte Ødelæggelser og have Lykke og udføre det; og han skal ødelægge dte stærke og de helliges Folk.
25 Zai sa yaudara ta ƙara yin yawa, zai ɗaukaka kansa. Sa’ad da suke ji sun sami mafaka, zai hallaka mutane da yawa sa’an nan kuma yă fara gāba da Sarkin sarakuna. Duk da haka za a hallaka shi, amma ba da ikon mutum ba.
Og formedelst hans Klogskab skal Svig lykkes i hans Haand, og han skal storlig ophøje sig i sit Hjerte og ødelægge mange i deres Tryghed; og han skal staa op imod Fyrsternes Fyrste, men uden Menneskehaand skal han knuses.
26 “Wahayin nan na safiya da yamma da aka nuna maka gaskiya ne, amma ka ɓoye wahayin, gama ya shafi nan gaba mai tsawo ne.”
Og Synet om Aftenerne og Morgenerne, hvorom der er talt, er Sandhed; men luk du til for Synet, thi det skal ske efter mange Dage.
27 Ni, Daniyel, na gaji matuƙa na kuma yi rashin lafiya na kwanaki masu yawa. Sa’an nan sai na tashi na ci gaba da hidimar sarki. Wahayin ya shige mini duhu, ya fi ƙarfin fahimtata.
Og jeg, Daniel, var aldeles afmægtig og syg i flere Dage; siden stod jeg op og udrettede Kongens Gerning; og jeg var forfærdet over Synet, og der var ingen, som forstod det.