< Daniyel 7 >

1 A shekara ta fari ta mulkin Belshazar sarkin Babilon, Daniyel ya yi mafarki, wahayoyi kuma suka ratsa tunaninsa a sa’ad da yake a kwance a gadonsa. Sai ya rubuta abin da mafarkin ya ƙunsa.
Uti första årena Belsazars, Konungens i Babel, hade Daniel en dröm och syn på sin säng; och han skref den samma drömmen, och författade honom alltså:
2 Daniyel ya ce, “A cikin wahayina da dare na duba, a gabana kuwa ga kusurwoyi huɗu na sama suna gurɓata babban teku.
Jag, Daniel, såg en syn om nattene, och si, de fyra väder under himmelen stormade emot hvartannat på stora hafvena.
3 Sai ga dabbobi huɗu, kowannensu ya yi dabam da sauran, suna fitowa daga teku.
Och fyra stor djur stego upp utu hafvet, ju det ena annorlunda än det andra;
4 “Na farkon ya yi kamar zaki kuma yana da fikafikai kamar gaggafa. Ina kallo, sai aka fizge fikafikanta, aka ɗaga ta sama, aka sa ta tsaya a kan ƙafafu biyu kamar mutum, aka ba ta tunani irin na mutum.
Det första såsom ett lejon, och hade vingar såsom en örn; jag såg till, intilldess att vingarne vordo thy afryckte, och det vardt tagit bort af jordene, och det stod på sina fötter såsom en menniska; och thy vardt ett menniskligit hjerta gifvet.
5 “A gabana kuma ga dabba ta biyu, wadda ta yi kamar beyar. Aka ɗaga ta a gefenta guda, tana kuwa da haƙarƙarai uku a bakinta a tsakanin haƙoranta. Aka faɗa mata, ‘Tashi ki cika cikinki da ɗanyen nama!’
Och si, det andra djuret dernäst var likt enom björn, och stod på den ena sidone, och hade i sinom mun, ibland sina tänder, tre stora långa tänder; och man sade till det: Statt upp, och ät mycket kött.
6 “Bayan haka, na duba, a gabana kuwa ga wata dabba wadda ta yi kamar Damisa, a bayanta kuma tana da fikafikai huɗu irin na tsuntsu. Wannan dabbar tana da kawuna huɗu, aka kuma ba ta iko tă yi mulki.
Efter detta såg jag, och si, ett annat djur, likt enom parde, det hade fyra vingar, såsom en fogel, på sin rygg; och det samma djuret hade fyra hufvud, och thy vardt magt gifven.
7 “Bayan haka, a cikin wahayina da dare na duba, a gabana kuwa ga dabba ta huɗu, wadda take da bantsoro da banrazana da kuma iko ƙwarai. Tana da manyan haƙoran ƙarfe; ta ragargaje ta cinye abin da ta kama, ta kuma tattaka duk abin da ya rage a ƙarƙashin ƙafafunta. Ta bambanta da dukan sauran dabbobin da suka riga ta, tana kuma da ƙahoni goma.
Efter detta såg jag i denna synene om nattena, och si, det fjerde djuret var grufveligit och förskräckligit, och mägta starkt, och hade stora jerntänder; åt omkring sig, och förkrossade, och hvad qvart var, trampade det med sina fötter. Det var ock mycket annars än de förra, och hade tio horn.
8 “Yayinda nake cikin tunani game da ƙahonin nan, a gabana kuwa ga wani ƙaho, ɗan ƙanƙani, wanda ya fito daga cikinsu; kuma an tumɓuke uku daga cikin ƙahonin farko kafin wannan. Wannan ƙaho yana da idanu kamar na mutum da kuma bakin da yake maganganun fariya.
Då jag nu skådade hornen, si, då gick der ut ibland dem ett annat litet horn, för hvilko de tre främsta hornen afstött vordo; och si, det samma hornet hade ögon såsom menniskoögon, och en mun, den stor ting talade.
9 “Ina cikin dubawa, “sai aka ajiye kursiyoyi, sai ga wani wanda yake tun fil azal ya zauna a mazauninsa. Rigarsa ta yi fari fat kamar ƙanƙara; gashin kansa sun yi fari kamar ulu. Kursiyinsa kuma harshen wuta, dukan ƙafafun kursiyin masu kama da keken yaƙin, wuta ne.
Sådant såg jag, tilldess stolar framsatte vordo, och den gamle satte sig, hvilkens kläde var snöhvitt, och håret på hans hufvud såsom ren ull; hans stol var alltsammans eldslåge, och hans hjul brunno af eld.
10 Kogin wuta yana gudu, yana fitowa daga gabansa. Dubun dubbai sun yi masa hidima; dubu goma sau dubu goma sun tsaya a gabansa. Aka zauna don shari’a, aka kuma buɗe littattafai.
Och af honom utgick en lång eldstrimma: Tusende sinom tusend tjente honom, och tio sinom hundrade tusend stodo för honom. Domen vardt hållen, och böckerna vordo upplåtna.
11 “Sa’an nan na ci gaba da kallo saboda kalmomin fariyar da wannan ƙaho yake furtawa. Na yi ta kallo har sai da aka yanke dabbar, aka kuma hallaka jikinta a cikin wuta.
Jag såg till, för de stora ords skull, som det hornet talade; jag såg till, intilldess djuret dräpit vardt, och dess kropp förgicks, och i eld kastad vardt;
12 (An tuɓe sauran dabbobin daga mulkinsu, amma aka bar su su rayu na wani lokaci.)
Och de andra djurs välde också ute var; ty dem var en tid och stund bestämd, huru länge hvartdera vara skulle.
13 “A wahayina na dare, na ga a gabana wani kamar ɗan mutum yana saukowa tare da gizagizan sama. Ya kusaci Wannan wanda yake Tun fil azal aka kuma kai shi gabansa.
Jag såg i denna synene om nattene; och si, en kom i himmelens sky, såsom ens menniskos Son, allt intill den gamla, och han vardt framhafd för honom.
14 Aka ba shi mulki, daraja da kuma mafificin iko; dukan mutane, da al’ummai, da mutane daga kowane harshe suka yi masa sujada. Mulkinsa kuwa dawwammamen mulki ne da ba zai ƙare ba, sarautarsa kuma ba ta taɓa lalacewa.
Honom gaf han våld, äro och rike, att all land, och folk, och tungomål, skulle tjena honom: Hans välde är evigt, det icke förgås, och hans rike hafver ingen ända.
15 “Ni, Daniyel, ruhuna ya damu ƙwarai, kuma wahayin da ya ratsa tunanina ya dame ni.
Jag, Daniel, förskräckte mig derföre, och sådana syn förfärade mig.
16 Sai na matsa kusa da ɗaya daga cikin waɗanda suke tsaye a can, na tambaye shi gaskiya ma’anar waɗannan al’amura. “Don haka sai ya faɗa mini, ya kuma ba ni fassarar waɗannan al’amura.
Och jag gick till en af dem som der stodo, och bad honom, att han skulle gifva mig en viss undervisning om allt detta; och han talade med mig, och tedde mig hvad det betydde:
17 ‘Waɗannan manyan dabbobi huɗu, Masarautai ne huɗu waɗanda za su taso a duniya.
Dessa fyra stora djur äro fyra rike, som på jordena komma skola;
18 Amma tsarkaka na Mafi Ɗaukaka za su karɓi wannan sarauta, za su kuwa mallake ta har abada, I, har abada abadin.’
Men dens Högstas helige skola intaga riket och skola besitta det i evig tid.
19 “Sa’an nan kuma sai na so in san ma’anar wannan dabba ta huɗu, wadda ta yi dabam da sauran dabbobin da suke da matuƙar bantsoro, da take da haƙoran ƙarfe da kuma farcen tagulla, dabbar ta ragargaje ta cinye abin da ta kama, ta kuma tattaka duk abin da ya rage a ƙarƙashin ƙafafunta.
Sedan hade jag gerna vetat en viss undervisning om det fjerde djuret, hvilket platt annars var, än all de andra, ganska grufveligit; det jerntänder och kopparklor hade, det omkring sig åt, och förkrossade, och det qvart var med sina fötter trampade;
20 Na kuma so in gane game da ƙahonin nan guda goma da suke a kanta da kuma game da ƙahon nan da ya fito, wanda aka tumɓuke ƙahoni uku a gabansa, ƙahon nan da yake da idanu da bakin da yake furta manyan maganganun fariya, wanda ya yi kamar ya fi sauran girma.
Och om de tio horn på dess hufvud, och om det andra som uppväxte, för hvilko tre afföllo; och om det samma hornet som ögon hade, och en mun, som stor ting talade, och större var än de der bredvid voro.
21 Ina cikin dubawa, sai ga wannan ƙaho yana yaƙi da tsarkaka yana kuma cin nasara a kansu,
Och jag såg det samma hornet strida emot de heliga, och det behöll segren emot dem;
22 sai da Wannan wanda yake tun fil azal ya zo ya furta hukunci, aka kuma ba tsarkaka na Mafi Ɗaukaka gaskiya, lokaci kuwa ya cika sai suka karɓi mulki.
Tilldess den gamle kom, och höll dom för dens Högstas heligom, och tiden kom, att de helige intogo riket.
23 “Sai ya ba ni wannan bayani, ‘Dabbar nan ta huɗu, ita ce mulki na huɗu da zai bayyana a duniya. Zai bambanta da dukan sauran mulkoki, zai kuma cinye dukan duniya, yă tattake ta, yă kuma ragargaje ta.
Han sade alltså: Det fjerde djuret skall vara det fjerde riket på jordene, hvilket mägtigare skall vara än all rike; det skall uppäta, förtrampa och förkrossa all land.
24 Ƙahonin nan goma, sarakuna ne goma waɗanda za su taso daga wannan mulki. Bayansu kuma, wani sarki zai taso, wanda ya sha dabam da waɗanda suka riga shi. Zai rinjayi sarakunan nan uku.
De tio horn betyda tio Konungar, som i de rikena uppkomma skola; efter dem skall en annan uppkomma, han skall vara mägtigare än någor af de förra, och skall undertrycka tre Konungar.
25 Zai yi maganar saɓo a kan Mafi Ɗaukaka, zai kuma tsananta wa tsarkaka yă kuma yi ƙoƙarin sāke lokuta da shari’u. Za a miƙa tsarkaka a hannunsa na wani lokaci, lokuta da kuma rabin lokaci.
Han skall försmäda den Högsta, och för störa dens Högstas heliga; och skall taga sig före att förvandla tider och lag; men de skola varda gifne uti hans hand i en tid, och några tider, och en half tid.
26 “‘Amma majalisa za tă yi zama, za a karɓe ikonsa, a kuma hallaka shi gaba ɗaya har abada.
Derefter skall domen hållen varda; så skall då hans välde borttaget varda, så att han skall i grund förderfvad och förgjord varda.
27 Sa’an nan za a ba da mulki, iko da girma na mulkokin da suke a ƙarƙashin dukan sammai ga tsarkaka, mutane na Mafi Ɗaukaka. Mulkinsa kuwa mulki ne marar matuƙa, kuma dukan masu mulki za su yabe shi, su kuma yi masa biyayya.’
Men riket, magten och väldet under hela himmelen skall varda gifvit dens Högstas heligo folke, hvilkes rike evigt är; och allt välde skall tjena honom, och lyda honom.
28 “Wannan shi ne ƙarshen batun. Ni, Daniyel na damu ƙwarai da irin tunanina, kuma fuskata ta rikice, amma na riƙe batun a zuciyata.”
Det var änden på talet. Men jag, Daniel, vardt svårliga bedröfvad i mina tankar, och mitt ansigte förvandlade sig uppå mig; dock behöll jag talet i mitt hjerta.

< Daniyel 7 >