< Daniyel 7 >

1 A shekara ta fari ta mulkin Belshazar sarkin Babilon, Daniyel ya yi mafarki, wahayoyi kuma suka ratsa tunaninsa a sa’ad da yake a kwance a gadonsa. Sai ya rubuta abin da mafarkin ya ƙunsa.
Ngomnyaka wokuqala kaBelishazari inkosi yeBhabhiloni, uDaniyeli wabona iphupho lemibono yekhanda lakhe embhedeni wakhe. Lapho walibhala iphupho, wakhuluma indikimba yezindaba.
2 Daniyel ya ce, “A cikin wahayina da dare na duba, a gabana kuwa ga kusurwoyi huɗu na sama suna gurɓata babban teku.
UDaniyeli waphendula wathi: Ngabona embonweni wami ebusuku, khangela-ke, imimoya yomine yamazulu yavumbuluka phezu kolwandle olukhulu.
3 Sai ga dabbobi huɗu, kowannensu ya yi dabam da sauran, suna fitowa daga teku.
Izilo ezine ezinkulu zakhuphuka elwandle, zehlukile esinye kwesinye.
4 “Na farkon ya yi kamar zaki kuma yana da fikafikai kamar gaggafa. Ina kallo, sai aka fizge fikafikanta, aka ɗaga ta sama, aka sa ta tsaya a kan ƙafafu biyu kamar mutum, aka ba ta tunani irin na mutum.
Esokuqala sasinjengesilwane, esilempiko zenkozi. Ngakhangela zaze zacuthwa impiko zaso, sasesiphakanyiswa sisuswa emhlabeni, samiswa ngenyawo njengomuntu, sanikwa inhliziyo yomuntu.
5 “A gabana kuma ga dabba ta biyu, wadda ta yi kamar beyar. Aka ɗaga ta a gefenta guda, tana kuwa da haƙarƙarai uku a bakinta a tsakanin haƙoranta. Aka faɗa mata, ‘Tashi ki cika cikinki da ɗanyen nama!’
Khangela-ke esinye isilo, esesibili, sasinjengebhere, sazimisa ehlangothini olulodwa, silembambo ezintathu emlonyeni waso phakathi kwamazinyo aso. Basebesithi njalo kuso: Sukuma, udle inyama enengi.
6 “Bayan haka, na duba, a gabana kuwa ga wata dabba wadda ta yi kamar Damisa, a bayanta kuma tana da fikafikai huɗu irin na tsuntsu. Wannan dabbar tana da kawuna huɗu, aka kuma ba ta iko tă yi mulki.
Emva kwalokhu ngabona, khangela-ke esinye, sasinjengengwe, silempiko ezine zenyoni emhlana waso, njalo isilo sasilamakhanda amane, lokubusa kwaphiwa kuso.
7 “Bayan haka, a cikin wahayina da dare na duba, a gabana kuwa ga dabba ta huɗu, wadda take da bantsoro da banrazana da kuma iko ƙwarai. Tana da manyan haƙoran ƙarfe; ta ragargaje ta cinye abin da ta kama, ta kuma tattaka duk abin da ya rage a ƙarƙashin ƙafafunta. Ta bambanta da dukan sauran dabbobin da suka riga ta, tana kuma da ƙahoni goma.
Emva kwalokhu ngabona emibonweni yebusuku, khangela-ke isilo sesine, esesabekayo, esethusayo, silamandla kakhulukazi, silamazinyo amakhulu ensimbi, sadla safohloza, sanyathela okuseleyo ngenyawo zaso. Njalo sasehlukile kuzo zonke izilo ezazingaphambi kwaso; futhi sasilempondo ezilitshumi.
8 “Yayinda nake cikin tunani game da ƙahonin nan, a gabana kuwa ga wani ƙaho, ɗan ƙanƙani, wanda ya fito daga cikinsu; kuma an tumɓuke uku daga cikin ƙahonin farko kafin wannan. Wannan ƙaho yana da idanu kamar na mutum da kuma bakin da yake maganganun fariya.
Ngakhangelisisa izimpondo, khangela-ke, kwenyuka phakathi kwazo olunye uphondo oluncinyane; lezintathu zezimpondo zokuqala zasitshunwa ngezimpande phambi kwalo; khangela-ke, amehlo anjengamehlo omuntu aba sephondweni lolu, lomlomo okhuluma izinto ezinkulu.
9 “Ina cikin dubawa, “sai aka ajiye kursiyoyi, sai ga wani wanda yake tun fil azal ya zauna a mazauninsa. Rigarsa ta yi fari fat kamar ƙanƙara; gashin kansa sun yi fari kamar ulu. Kursiyinsa kuma harshen wuta, dukan ƙafafun kursiyin masu kama da keken yaƙin, wuta ne.
Ngakhangela, kwaze kwabekwa izihlalo zobukhosi, kwahlala oMdala wezinsuku, ozembatho zakhe zazimhlophe njengeliqhwa elikhithikileyo, lenwele zekhanda lakhe njengoboya bemvu obuhlanzekileyo; isihlalo sakhe sobukhosi sililangabi lomlilo, amavili aso angumlilo ovuthayo.
10 Kogin wuta yana gudu, yana fitowa daga gabansa. Dubun dubbai sun yi masa hidima; dubu goma sau dubu goma sun tsaya a gabansa. Aka zauna don shari’a, aka kuma buɗe littattafai.
Isifudlana somlilo sageleza saphuma phambi kwakhe. Inkulungwane zezinkulungwane zamkhonza, lezinkulungwane ezilitshumi zezinkulungwane ezilitshumi zema phambi kwakhe. Isahlulelo sazimisa, lezincwadi zavulwa.
11 “Sa’an nan na ci gaba da kallo saboda kalmomin fariyar da wannan ƙaho yake furtawa. Na yi ta kallo har sai da aka yanke dabbar, aka kuma hallaka jikinta a cikin wuta.
Lapho ngakhangela ngenxa yomsindo wamazwi amakhulu uphondo olwawakhulumayo. Ngakhangela saze sabulawa isilo, lomzimba waso wachithwa, wanikelwa emlilweni obhebhayo.
12 (An tuɓe sauran dabbobin daga mulkinsu, amma aka bar su su rayu na wani lokaci.)
Mayelana lezinye izilo, umbuso wazo wasuswa, kanti ukwelulwa empilweni kwanikwa kuzo kwaze kwaba yisikhathi esimisiweyo lethuba.
13 “A wahayina na dare, na ga a gabana wani kamar ɗan mutum yana saukowa tare da gizagizan sama. Ya kusaci Wannan wanda yake Tun fil azal aka kuma kai shi gabansa.
Ngabona emibonweni yebusuku, khangela-ke, onjengendodana yomuntu weza ngamayezi amazulu, wafika kuMdala wezinsuku, basebemsondeza phambi kwakhe.
14 Aka ba shi mulki, daraja da kuma mafificin iko; dukan mutane, da al’ummai, da mutane daga kowane harshe suka yi masa sujada. Mulkinsa kuwa dawwammamen mulki ne da ba zai ƙare ba, sarautarsa kuma ba ta taɓa lalacewa.
Wasenikwa ukubusa, lodumo, lombuso, ukuze bonke abantu, izizwe, lezindimi kumkhonze. Ukubusa kwakhe kuyikubusa kwaphakade, okungayikudlula, lombuso wakhe ngongayikuchithwa.
15 “Ni, Daniyel, ruhuna ya damu ƙwarai, kuma wahayin da ya ratsa tunanina ya dame ni.
Mina Daniyeli, umoya wami wadabuka phakathi komzimba, lemibono yekhanda lami yangethusa.
16 Sai na matsa kusa da ɗaya daga cikin waɗanda suke tsaye a can, na tambaye shi gaskiya ma’anar waɗannan al’amura. “Don haka sai ya faɗa mini, ya kuma ba ni fassarar waɗannan al’amura.
Ngasondela komunye wababemi khona, ngabuza kuye iqiniso lakho konke lokhu. Wasengitshela, wangazisa ingcazelo yezindaba.
17 ‘Waɗannan manyan dabbobi huɗu, Masarautai ne huɗu waɗanda za su taso a duniya.
Lezizilo ezinkulu, zozine, zingamakhosi amane, azasukuma evela emhlabeni.
18 Amma tsarkaka na Mafi Ɗaukaka za su karɓi wannan sarauta, za su kuwa mallake ta har abada, I, har abada abadin.’
Kodwa abangcwele boPhezukonke bazakwemukela umbuso, babe lombuso kuze kube phakade, ngitsho kuze kube nini lanini.
19 “Sa’an nan kuma sai na so in san ma’anar wannan dabba ta huɗu, wadda ta yi dabam da sauran dabbobin da suke da matuƙar bantsoro, da take da haƙoran ƙarfe da kuma farcen tagulla, dabbar ta ragargaje ta cinye abin da ta kama, ta kuma tattaka duk abin da ya rage a ƙarƙashin ƙafafunta.
Lapho ngathanda ukwazi iqiniso ngesilo sesine, esasehlukile kuzo zonke, sisesabeka kakhulukazi, omazinyo aso ayengawensimbi, lenzipho zaso zingezethusi; sadla, safohloza, sanyathela okuseleyo ngenyawo zaso;
20 Na kuma so in gane game da ƙahonin nan guda goma da suke a kanta da kuma game da ƙahon nan da ya fito, wanda aka tumɓuke ƙahoni uku a gabansa, ƙahon nan da yake da idanu da bakin da yake furta manyan maganganun fariya, wanda ya yi kamar ya fi sauran girma.
langezimpondo ezilitshumi ezazisekhanda laso, lolunye olwenyukayo, lezawa phambi kwalo ezintathu; ngitsho lolophondo olwalulamehlo, lomlomo owakhuluma izinto ezinkulu, lokubonakala kwalo kwakukukhulu kulezinye.
21 Ina cikin dubawa, sai ga wannan ƙaho yana yaƙi da tsarkaka yana kuma cin nasara a kansu,
Ngabona, ukuthi loluphondo lusilwa labangcwele, lwabanqoba,
22 sai da Wannan wanda yake tun fil azal ya zo ya furta hukunci, aka kuma ba tsarkaka na Mafi Ɗaukaka gaskiya, lokaci kuwa ya cika sai suka karɓi mulki.
kwaze kwafika oMdala wezinsuku, lesahlulelo saphiwa abangcwele boPhezukonke; kwasekufika isikhathi esimisiweyo sokuthi abangcwele babe lombuso.
23 “Sai ya ba ni wannan bayani, ‘Dabbar nan ta huɗu, ita ce mulki na huɗu da zai bayyana a duniya. Zai bambanta da dukan sauran mulkoki, zai kuma cinye dukan duniya, yă tattake ta, yă kuma ragargaje ta.
Watsho njalo: Isilo sesine sizakuba ngumbuso wesine emhlabeni, ozakwehluka kuyo yonke imibuso, sidle wonke umhlaba, siwunyathelele phansi, siwufohloze.
24 Ƙahonin nan goma, sarakuna ne goma waɗanda za su taso daga wannan mulki. Bayansu kuma, wani sarki zai taso, wanda ya sha dabam da waɗanda suka riga shi. Zai rinjayi sarakunan nan uku.
Mayelana lempondo ezilitshumi, amakhosi alitshumi azasukuma evela kulo umbuso, lenye izasukuma emva kwawo. Yona-ke izakwehluka kwawokuqala, iwehlisele phansi amakhosi amathathu.
25 Zai yi maganar saɓo a kan Mafi Ɗaukaka, zai kuma tsananta wa tsarkaka yă kuma yi ƙoƙarin sāke lokuta da shari’u. Za a miƙa tsarkaka a hannunsa na wani lokaci, lokuta da kuma rabin lokaci.
Njalo izakhuluma amazwi imelene loPhezukonke, ihluphe njalonjalo abangcwele boPhezukonke, inakane ngokuguqula izikhathi lomlayo; njalo bazanikelwa esandleni sayo kuze kube yisikhathi lezikhathi lengxenye yesikhathi.
26 “‘Amma majalisa za tă yi zama, za a karɓe ikonsa, a kuma hallaka shi gaba ɗaya har abada.
Kodwa isahlulelo sizahlala, basuse umbuso wayo, ukuthi bawuchithe bawuqede kuze kube sekupheleni.
27 Sa’an nan za a ba da mulki, iko da girma na mulkokin da suke a ƙarƙashin dukan sammai ga tsarkaka, mutane na Mafi Ɗaukaka. Mulkinsa kuwa mulki ne marar matuƙa, kuma dukan masu mulki za su yabe shi, su kuma yi masa biyayya.’
Njalo umbuso lokubusa lobukhulu bemibuso ngaphansi kwamazulu wonke kuzanikwa abantu babangcwele boPhezukonke, ombuso wabo ngumbuso ongulaphakade, lemibuso yonke izamkhonza ilalele.
28 “Wannan shi ne ƙarshen batun. Ni, Daniyel na damu ƙwarai da irin tunanina, kuma fuskata ta rikice, amma na riƙe batun a zuciyata.”
Kuze kube lapha yisicino sendaba. Mina Daniyeli, imicabango yami yangethusa kakhulu, lokucwebezela kobuso bami kwaguquka kimi; kodwa ngalugcina udaba enhliziyweni yami.

< Daniyel 7 >