< Daniyel 7 >
1 A shekara ta fari ta mulkin Belshazar sarkin Babilon, Daniyel ya yi mafarki, wahayoyi kuma suka ratsa tunaninsa a sa’ad da yake a kwance a gadonsa. Sai ya rubuta abin da mafarkin ya ƙunsa.
En la première année de Baltassar, roi de Babylone, Daniel vit un songe; mais cette vision de sa tête, il l’eut dans son lit; et écrivant le songe, il le recueillit en peu de paroles, et le rapportant sommairement, il dit:
2 Daniyel ya ce, “A cikin wahayina da dare na duba, a gabana kuwa ga kusurwoyi huɗu na sama suna gurɓata babban teku.
Je voyais dans ma vision, durant la nuit, et voici que les quatre vents du ciel combattaient sur la grande mer.
3 Sai ga dabbobi huɗu, kowannensu ya yi dabam da sauran, suna fitowa daga teku.
Et quatre grandes bêtes montaient de la mer, différentes entre elles.
4 “Na farkon ya yi kamar zaki kuma yana da fikafikai kamar gaggafa. Ina kallo, sai aka fizge fikafikanta, aka ɗaga ta sama, aka sa ta tsaya a kan ƙafafu biyu kamar mutum, aka ba ta tunani irin na mutum.
La première était comme une lionne, et elle avait des ailes d’aigle; je la regardais jusqu’à ce que ses ailes furent arrachées et qu’elle fut élevée de terre; et elle se tint sur ses pieds comme un homme; et un cœur d’homme lui fut donné.
5 “A gabana kuma ga dabba ta biyu, wadda ta yi kamar beyar. Aka ɗaga ta a gefenta guda, tana kuwa da haƙarƙarai uku a bakinta a tsakanin haƙoranta. Aka faɗa mata, ‘Tashi ki cika cikinki da ɗanyen nama!’
Et voici qu’une autre bête semblable à un ours, se tint à côté; et il y avait trois rangs dans sa gueule et dans ses dents, et on lui disait ainsi: Lève-toi, mange beaucoup de chairs.
6 “Bayan haka, na duba, a gabana kuwa ga wata dabba wadda ta yi kamar Damisa, a bayanta kuma tana da fikafikai huɗu irin na tsuntsu. Wannan dabbar tana da kawuna huɗu, aka kuma ba ta iko tă yi mulki.
Après cela je regardais, et voici une autre bête comme un léopard, et elle avait quatre ailes d’oiseau au-dessus d’elle; et cette bête avait quatre têtes, et la puissance lui fut donnée.
7 “Bayan haka, a cikin wahayina da dare na duba, a gabana kuwa ga dabba ta huɗu, wadda take da bantsoro da banrazana da kuma iko ƙwarai. Tana da manyan haƙoran ƙarfe; ta ragargaje ta cinye abin da ta kama, ta kuma tattaka duk abin da ya rage a ƙarƙashin ƙafafunta. Ta bambanta da dukan sauran dabbobin da suka riga ta, tana kuma da ƙahoni goma.
Après cela je regardais dans cette vision de nuit, et voici une quatrième bête terrible et merveilleuse, et extrêmement forte; elle avait de grandes dents de fer, mangeant, et mettant en pièces, et foulant les restes avec ses pieds; mais elle était différente des autres bêtes que j’avais vues avant elle; et elle avait dix cornes.
8 “Yayinda nake cikin tunani game da ƙahonin nan, a gabana kuwa ga wani ƙaho, ɗan ƙanƙani, wanda ya fito daga cikinsu; kuma an tumɓuke uku daga cikin ƙahonin farko kafin wannan. Wannan ƙaho yana da idanu kamar na mutum da kuma bakin da yake maganganun fariya.
Je considérai ses cornes, et voici qu’une autre petite corne s’éleva du milieu d’elles; et trois des premières cornes furent arrachées de sa face; et voici que des yeux comme des yeux d’un homme étaient à cette corne, et qu’une bouche disait de grandes choses.
9 “Ina cikin dubawa, “sai aka ajiye kursiyoyi, sai ga wani wanda yake tun fil azal ya zauna a mazauninsa. Rigarsa ta yi fari fat kamar ƙanƙara; gashin kansa sun yi fari kamar ulu. Kursiyinsa kuma harshen wuta, dukan ƙafafun kursiyin masu kama da keken yaƙin, wuta ne.
Je regardais jusqu’à ce que des trônes furent placés, et un vieillard s’assit; son vêtement était blanc comme la neige, et les cheveux de sa tête blancs comme une laine pure; son trône, des flammes de feu; ses roues, un feu brûlant.
10 Kogin wuta yana gudu, yana fitowa daga gabansa. Dubun dubbai sun yi masa hidima; dubu goma sau dubu goma sun tsaya a gabansa. Aka zauna don shari’a, aka kuma buɗe littattafai.
Un fleuve de feu et rapide sortait de sa face; des milliers de milliers d’anges le servaient, et dix milliers de centaines de milliers d’anges assistaient devant lui; le jugement se tint, et des livres furent ouverts.
11 “Sa’an nan na ci gaba da kallo saboda kalmomin fariyar da wannan ƙaho yake furtawa. Na yi ta kallo har sai da aka yanke dabbar, aka kuma hallaka jikinta a cikin wuta.
Je regardais à cause de la voix des grandes paroles que cette corne prononçait; et je vis que la bête fut tuée, et que son corps périt, et qu’il fut livré pour être brûlé par le feu;
12 (An tuɓe sauran dabbobin daga mulkinsu, amma aka bar su su rayu na wani lokaci.)
Je vis aussi que la puissance des autres bêtes leur fut ôtée, et que les temps de vie leur furent marqués jusqu’à un temps et un temps.
13 “A wahayina na dare, na ga a gabana wani kamar ɗan mutum yana saukowa tare da gizagizan sama. Ya kusaci Wannan wanda yake Tun fil azal aka kuma kai shi gabansa.
Je regardais donc dans la vision de nuit, et voici comme le fils d’un homme qui venait avec les nuées du ciel; et il s’avança jusqu’au vieillard, et ils le présentèrent devant lui.
14 Aka ba shi mulki, daraja da kuma mafificin iko; dukan mutane, da al’ummai, da mutane daga kowane harshe suka yi masa sujada. Mulkinsa kuwa dawwammamen mulki ne da ba zai ƙare ba, sarautarsa kuma ba ta taɓa lalacewa.
Et il lui donna la puissance, et l’honneur, et le royaume; et tous les peuples, tribus et langues le serviront; sa puissance est une puissance éternelle, qui ne lui sera pas enlevée; et son royaume, un royaume qui ne sera pas détruit.
15 “Ni, Daniyel, ruhuna ya damu ƙwarai, kuma wahayin da ya ratsa tunanina ya dame ni.
Mon esprit fut saisi d’effroi; moi Daniel, je fus épouvanté de ces choses, et les visions de ma tête me troublèrent.
16 Sai na matsa kusa da ɗaya daga cikin waɗanda suke tsaye a can, na tambaye shi gaskiya ma’anar waɗannan al’amura. “Don haka sai ya faɗa mini, ya kuma ba ni fassarar waɗannan al’amura.
Je m’approchai de l’un des assistants, et lui demandai la vérité sur toutes ces choses. Et il me donna l’interprétation des paroles, et il m’instruisit, disant:
17 ‘Waɗannan manyan dabbobi huɗu, Masarautai ne huɗu waɗanda za su taso a duniya.
Ces quatre grandes bêtes sont quatre royaumes qui s’élèveront de la terre.
18 Amma tsarkaka na Mafi Ɗaukaka za su karɓi wannan sarauta, za su kuwa mallake ta har abada, I, har abada abadin.’
Et les saints du Dieu très haut recevront le royaume, et ils le posséderont jusqu’au siècle et au siècle des siècles.
19 “Sa’an nan kuma sai na so in san ma’anar wannan dabba ta huɗu, wadda ta yi dabam da sauran dabbobin da suke da matuƙar bantsoro, da take da haƙoran ƙarfe da kuma farcen tagulla, dabbar ta ragargaje ta cinye abin da ta kama, ta kuma tattaka duk abin da ya rage a ƙarƙashin ƙafafunta.
Après cela je voulus soigneusement m’informer de la quatrième bête, qui était très différente de toutes les autres, et terrible; ses dents et ses ongles étaient de fer; elle mangeait, et mettait en pièces, et foulait les restes avec ses pieds;
20 Na kuma so in gane game da ƙahonin nan guda goma da suke a kanta da kuma game da ƙahon nan da ya fito, wanda aka tumɓuke ƙahoni uku a gabansa, ƙahon nan da yake da idanu da bakin da yake furta manyan maganganun fariya, wanda ya yi kamar ya fi sauran girma.
Je voulus m’informer aussi des dix cornes qu’elle avait à la tête, et de l’autre qui s’était élevée, devant laquelle étaient tombées trois cornes; et de cette corne qui avait des yeux et une bouche qui disait de grandes choses et était plus grande que les autres.
21 Ina cikin dubawa, sai ga wannan ƙaho yana yaƙi da tsarkaka yana kuma cin nasara a kansu,
Je regardais, et voici que cette corne faisait la guerre aux saints et prévalait sur eux,
22 sai da Wannan wanda yake tun fil azal ya zo ya furta hukunci, aka kuma ba tsarkaka na Mafi Ɗaukaka gaskiya, lokaci kuwa ya cika sai suka karɓi mulki.
Jusqu’à ce que vint l’ancien des jours, et qu’il donna le jugement aux saints du Très-Haut; et le temps arriva, et les saints possédèrent le royaume.
23 “Sai ya ba ni wannan bayani, ‘Dabbar nan ta huɗu, ita ce mulki na huɗu da zai bayyana a duniya. Zai bambanta da dukan sauran mulkoki, zai kuma cinye dukan duniya, yă tattake ta, yă kuma ragargaje ta.
Et il dit ainsi: La quatrième bête sera le quatrième royaume sur la terre, lequel sera plus grand que tous les autres royaumes, et dévorera toute la terre, et la foulera et la réduira en poudre.
24 Ƙahonin nan goma, sarakuna ne goma waɗanda za su taso daga wannan mulki. Bayansu kuma, wani sarki zai taso, wanda ya sha dabam da waɗanda suka riga shi. Zai rinjayi sarakunan nan uku.
Or les dix cornes de ce royaume même seront dix rois; et un autre s’élèvera après eux, et celui-ci sera plus puissant que les premiers, et il humiliera trois rois.
25 Zai yi maganar saɓo a kan Mafi Ɗaukaka, zai kuma tsananta wa tsarkaka yă kuma yi ƙoƙarin sāke lokuta da shari’u. Za a miƙa tsarkaka a hannunsa na wani lokaci, lokuta da kuma rabin lokaci.
Et il proférera des paroles contre le Très-Haut, et il brisera les saints du Très-Haut; et il pensera qu’il peut changer les temps et les lois; et ils seront livrés en sa main jusqu’à un temps, et deux temps, et la moitié d’un temps.
26 “‘Amma majalisa za tă yi zama, za a karɓe ikonsa, a kuma hallaka shi gaba ɗaya har abada.
Et le jugement se tiendra, afin que la puissance lui soit ôtée, et qu’il soit brisé, et qu’il périsse entièrement pour jamais;
27 Sa’an nan za a ba da mulki, iko da girma na mulkokin da suke a ƙarƙashin dukan sammai ga tsarkaka, mutane na Mafi Ɗaukaka. Mulkinsa kuwa mulki ne marar matuƙa, kuma dukan masu mulki za su yabe shi, su kuma yi masa biyayya.’
Mais que le royaume, et la puissance, et l’étendue du royaume, laquelle est sous le ciel entier, soit donnée au peuple des saints du Très-Haut, dont le royaume est un royaume éternel, et tous les rois le serviront et lui obéiront.
28 “Wannan shi ne ƙarshen batun. Ni, Daniyel na damu ƙwarai da irin tunanina, kuma fuskata ta rikice, amma na riƙe batun a zuciyata.”
Ici est la fin de la parole. Moi, Daniel, jetais beaucoup troublé par mes pensées, et ma face changea en moi; mais la parole, je la conservai dans mon cœur.