< Daniyel 7 >
1 A shekara ta fari ta mulkin Belshazar sarkin Babilon, Daniyel ya yi mafarki, wahayoyi kuma suka ratsa tunaninsa a sa’ad da yake a kwance a gadonsa. Sai ya rubuta abin da mafarkin ya ƙunsa.
In the first year of Belshazzar the king of Babylon, Daniel saw a dream and the visions of his head while on his couch: afterward he wrote down the dream, relating the principal things.
2 Daniyel ya ce, “A cikin wahayina da dare na duba, a gabana kuwa ga kusurwoyi huɗu na sama suna gurɓata babban teku.
Daniel commenced and said, I saw in my vision by night, and, behold, the four winds of heaven blew fiercely on the great sea.
3 Sai ga dabbobi huɗu, kowannensu ya yi dabam da sauran, suna fitowa daga teku.
And four great beasts came up from the sea, differing one from another.
4 “Na farkon ya yi kamar zaki kuma yana da fikafikai kamar gaggafa. Ina kallo, sai aka fizge fikafikanta, aka ɗaga ta sama, aka sa ta tsaya a kan ƙafafu biyu kamar mutum, aka ba ta tunani irin na mutum.
the first was like a lion, and had eagle's wings: I looked till its wings were plucked out, and it was lifted up from the earth, and was placed upon its feet as a man, and a human heart was given to it.
5 “A gabana kuma ga dabba ta biyu, wadda ta yi kamar beyar. Aka ɗaga ta a gefenta guda, tana kuwa da haƙarƙarai uku a bakinta a tsakanin haƙoranta. Aka faɗa mata, ‘Tashi ki cika cikinki da ɗanyen nama!’
And behold there was another, a second beast, like a bear, and on one side was it placed, with three ribs in its mouth between its teeth: and thus they said unto it, Arise, eat much flesh.
6 “Bayan haka, na duba, a gabana kuwa ga wata dabba wadda ta yi kamar Damisa, a bayanta kuma tana da fikafikai huɗu irin na tsuntsu. Wannan dabbar tana da kawuna huɗu, aka kuma ba ta iko tă yi mulki.
After this I looked, and lo there was another, like a leopard; and it had four wings of a bird on its back: the beast had also four heads; and dominion was given unto it.
7 “Bayan haka, a cikin wahayina da dare na duba, a gabana kuwa ga dabba ta huɗu, wadda take da bantsoro da banrazana da kuma iko ƙwarai. Tana da manyan haƙoran ƙarfe; ta ragargaje ta cinye abin da ta kama, ta kuma tattaka duk abin da ya rage a ƙarƙashin ƙafafunta. Ta bambanta da dukan sauran dabbobin da suka riga ta, tana kuma da ƙahoni goma.
After this I looked in the night visions, and behold there was a fourth beast, dreadful and terrible, and strong exceedingly; and it had great iron teeth: it devoured and ground up, and what was left it stamped with its feet; and it was different from all the beasts that were before it; and it had ten horns.
8 “Yayinda nake cikin tunani game da ƙahonin nan, a gabana kuwa ga wani ƙaho, ɗan ƙanƙani, wanda ya fito daga cikinsu; kuma an tumɓuke uku daga cikin ƙahonin farko kafin wannan. Wannan ƙaho yana da idanu kamar na mutum da kuma bakin da yake maganganun fariya.
I looked carefully at the horns, and, behold, another little horn came up between them, and three of the first horns were plucked up by the roots before the same; and, behold, there were eyes like the eyes of man in this horn, with a mouth speaking presumptuous things.
9 “Ina cikin dubawa, “sai aka ajiye kursiyoyi, sai ga wani wanda yake tun fil azal ya zauna a mazauninsa. Rigarsa ta yi fari fat kamar ƙanƙara; gashin kansa sun yi fari kamar ulu. Kursiyinsa kuma harshen wuta, dukan ƙafafun kursiyin masu kama da keken yaƙin, wuta ne.
I was looking until chairs were set down, and an Ancient of days seated himself, whose garment was white as snow, and the hair of whose head was like clean wool; his chair was like flames of fire, and his wheels like fire that burnt;
10 Kogin wuta yana gudu, yana fitowa daga gabansa. Dubun dubbai sun yi masa hidima; dubu goma sau dubu goma sun tsaya a gabansa. Aka zauna don shari’a, aka kuma buɗe littattafai.
A stream of fire issued and came forth from before him; thousand times thousands ministered unto him, and myriad times myriads stood before him: they sat down to hold judgment, and the books were opened.
11 “Sa’an nan na ci gaba da kallo saboda kalmomin fariyar da wannan ƙaho yake furtawa. Na yi ta kallo har sai da aka yanke dabbar, aka kuma hallaka jikinta a cikin wuta.
I looked then, because of the sound of the presumptuous words which the horn had spoken, —I looked till the beast was slain, and its body destroyed, and given over to the burning fire.
12 (An tuɓe sauran dabbobin daga mulkinsu, amma aka bar su su rayu na wani lokaci.)
But concerning the rest of the beasts, they had their dominion taken away: yet a longer duration of life was given unto them until the time and period.
13 “A wahayina na dare, na ga a gabana wani kamar ɗan mutum yana saukowa tare da gizagizan sama. Ya kusaci Wannan wanda yake Tun fil azal aka kuma kai shi gabansa.
I looked in the nightly visions, and, behold, with the clouds of heaven came one like a son of man, and he attained as far as the Ancient of days, and they brought him near before him.
14 Aka ba shi mulki, daraja da kuma mafificin iko; dukan mutane, da al’ummai, da mutane daga kowane harshe suka yi masa sujada. Mulkinsa kuwa dawwammamen mulki ne da ba zai ƙare ba, sarautarsa kuma ba ta taɓa lalacewa.
And there were given him dominion, and dignity, and government, and all people, nations, and languages had to serve him: his dominion is an everlasting dominion, which shall not pass away, and his kingdom is one which shall never be destroyed.
15 “Ni, Daniyel, ruhuna ya damu ƙwarai, kuma wahayin da ya ratsa tunanina ya dame ni.
My spirit was deeply shaken within me, Daniel, in the midst of its tenement, and the visions of my head troubled me.
16 Sai na matsa kusa da ɗaya daga cikin waɗanda suke tsaye a can, na tambaye shi gaskiya ma’anar waɗannan al’amura. “Don haka sai ya faɗa mini, ya kuma ba ni fassarar waɗannan al’amura.
I came near unto one of those that stood by, and asked him something certain concerning all this: and he spoke to me, and made known unto me the interpretation of the things.
17 ‘Waɗannan manyan dabbobi huɗu, Masarautai ne huɗu waɗanda za su taso a duniya.
These great beasts, of which there are four, are four kings, who are to arise on the earth.
18 Amma tsarkaka na Mafi Ɗaukaka za su karɓi wannan sarauta, za su kuwa mallake ta har abada, I, har abada abadin.’
But the saints of the Most High will obtain the kingdom, and possess the kingdom to eternity, even to all eternity for ever.
19 “Sa’an nan kuma sai na so in san ma’anar wannan dabba ta huɗu, wadda ta yi dabam da sauran dabbobin da suke da matuƙar bantsoro, da take da haƙoran ƙarfe da kuma farcen tagulla, dabbar ta ragargaje ta cinye abin da ta kama, ta kuma tattaka duk abin da ya rage a ƙarƙashin ƙafafunta.
Then I desired what is certain concerning the fourth beast, which was different from all these others, exceedingly dreadful, whose teeth were of iron, and whose nails of copper; which devoured, ground up, and stamped with its feet what was left;
20 Na kuma so in gane game da ƙahonin nan guda goma da suke a kanta da kuma game da ƙahon nan da ya fito, wanda aka tumɓuke ƙahoni uku a gabansa, ƙahon nan da yake da idanu da bakin da yake furta manyan maganganun fariya, wanda ya yi kamar ya fi sauran girma.
And concerning the ten horns that were in its head, and concerning the other which came up, and before which three fell down, even concerning that horn which had eyes, and a mouth which spoke presumptuous things, and whose appearance was greater than that of its companions.
21 Ina cikin dubawa, sai ga wannan ƙaho yana yaƙi da tsarkaka yana kuma cin nasara a kansu,
I had seen how the same horn had made war with the saints, and had prevailed against them:
22 sai da Wannan wanda yake tun fil azal ya zo ya furta hukunci, aka kuma ba tsarkaka na Mafi Ɗaukaka gaskiya, lokaci kuwa ya cika sai suka karɓi mulki.
Until the Ancient of days came, and procured justice unto the saints of the Most High; and the time came and the saints took possession of the kingdom.
23 “Sai ya ba ni wannan bayani, ‘Dabbar nan ta huɗu, ita ce mulki na huɗu da zai bayyana a duniya. Zai bambanta da dukan sauran mulkoki, zai kuma cinye dukan duniya, yă tattake ta, yă kuma ragargaje ta.
Thus said he, The fourth beast [signifieth that] a fourth kingdom will be upon earth, which is to be different from all kingdoms, and will devour all the earth, and will tread it down, and grind it up.
24 Ƙahonin nan goma, sarakuna ne goma waɗanda za su taso daga wannan mulki. Bayansu kuma, wani sarki zai taso, wanda ya sha dabam da waɗanda suka riga shi. Zai rinjayi sarakunan nan uku.
And the ten horns out of this kingdom [signify] that ten kings will arise; and another will rise after them, and he will be different from the first, and three kings will he bring low.
25 Zai yi maganar saɓo a kan Mafi Ɗaukaka, zai kuma tsananta wa tsarkaka yă kuma yi ƙoƙarin sāke lokuta da shari’u. Za a miƙa tsarkaka a hannunsa na wani lokaci, lokuta da kuma rabin lokaci.
And he will speak words against the Most High, and the saints of the Most High will he oppress, and think to change the festivals and the law: and they will be given up into his hand until a time and times and half a time.
26 “‘Amma majalisa za tă yi zama, za a karɓe ikonsa, a kuma hallaka shi gaba ɗaya har abada.
But they will sit down to hold judgment, and they will take away his dominion, to destroy and to annihilate it unto the end.
27 Sa’an nan za a ba da mulki, iko da girma na mulkokin da suke a ƙarƙashin dukan sammai ga tsarkaka, mutane na Mafi Ɗaukaka. Mulkinsa kuwa mulki ne marar matuƙa, kuma dukan masu mulki za su yabe shi, su kuma yi masa biyayya.’
And the kingdom and the dominion, and the power over the kingdoms under the whole heaven, will be given to the people of the saints of the Most High, whose kingdom is an everlasting kingdom, and all governments are to worship and obey him.
28 “Wannan shi ne ƙarshen batun. Ni, Daniyel na damu ƙwarai da irin tunanina, kuma fuskata ta rikice, amma na riƙe batun a zuciyata.”
Thus far is the end of the speech. As for me Daniel, my reflections troubled me greatly, and my color was changed on me; but I kept the speech in my heart.