< Daniyel 7 >
1 A shekara ta fari ta mulkin Belshazar sarkin Babilon, Daniyel ya yi mafarki, wahayoyi kuma suka ratsa tunaninsa a sa’ad da yake a kwance a gadonsa. Sai ya rubuta abin da mafarkin ya ƙunsa.
I Belsazar, Kongen af Babels, første Aar saa Daniel en Drøm og sit Hoveds Syner paa sit Leje; da skrev han Drømmen op, Hovedindholdet fremsatte han.
2 Daniyel ya ce, “A cikin wahayina da dare na duba, a gabana kuwa ga kusurwoyi huɗu na sama suna gurɓata babban teku.
Daniel fortalte og sagde: Jeg saa i mit Syn om Natten, og se, de fire Vejr under Himmelen brøde frem paa det store Hav.
3 Sai ga dabbobi huɗu, kowannensu ya yi dabam da sauran, suna fitowa daga teku.
Og der opsteg fire store Dyr af Havet, det ene anderledes end det andet.
4 “Na farkon ya yi kamar zaki kuma yana da fikafikai kamar gaggafa. Ina kallo, sai aka fizge fikafikanta, aka ɗaga ta sama, aka sa ta tsaya a kan ƙafafu biyu kamar mutum, aka ba ta tunani irin na mutum.
Det første var som en Løve, og det havde Vinger som en Ørn; jeg saa til, indtil dets Vinger bleve afrevne, og det blev rettet i Vejret fra Jorden og rejst op paa Fødderne som et Menneske, og det blev givet et Menneskehjerte.
5 “A gabana kuma ga dabba ta biyu, wadda ta yi kamar beyar. Aka ɗaga ta a gefenta guda, tana kuwa da haƙarƙarai uku a bakinta a tsakanin haƙoranta. Aka faɗa mata, ‘Tashi ki cika cikinki da ɗanyen nama!’
Og se, et andet Dyr, næstefter, ligt en Bjørn, og det rejste sig til den ene Side, og det havde tre Ribben i sin Mund, imellem sine Tænder; og man sagde saaledes til det: Staa op, æd meget Kød!
6 “Bayan haka, na duba, a gabana kuwa ga wata dabba wadda ta yi kamar Damisa, a bayanta kuma tana da fikafikai huɗu irin na tsuntsu. Wannan dabbar tana da kawuna huɗu, aka kuma ba ta iko tă yi mulki.
Derefter saa jeg, og se, et andet Dyr, ligt en Parder, og det havde fire Vinger som af en Fugl paa sin Ryg; og dette. Dyr havde fire Hoveder, og der blev givet det Magt.
7 “Bayan haka, a cikin wahayina da dare na duba, a gabana kuwa ga dabba ta huɗu, wadda take da bantsoro da banrazana da kuma iko ƙwarai. Tana da manyan haƙoran ƙarfe; ta ragargaje ta cinye abin da ta kama, ta kuma tattaka duk abin da ya rage a ƙarƙashin ƙafafunta. Ta bambanta da dukan sauran dabbobin da suka riga ta, tana kuma da ƙahoni goma.
Derefter saa jeg i Nattesynerne og se, et fjerde Dyr, frygteligt og forfærdeligt og meget stærkt, og det havde store Jerntænder, det aad og knuste og nedtraadte det overblevne med sine Fødder; og det var anderledes end alle de Dyr, som havde været før det, og det havde ti Horn.
8 “Yayinda nake cikin tunani game da ƙahonin nan, a gabana kuwa ga wani ƙaho, ɗan ƙanƙani, wanda ya fito daga cikinsu; kuma an tumɓuke uku daga cikin ƙahonin farko kafin wannan. Wannan ƙaho yana da idanu kamar na mutum da kuma bakin da yake maganganun fariya.
Jeg agtede nøje paa Hornene, og se, et andet lidet Horn skød op imellem dem, og tre af de forrige Horn bleve oprykkede for det; og se, der var Øjne som Menneskeøjne paa dette Horn, og en Mund, som talte store Ting.
9 “Ina cikin dubawa, “sai aka ajiye kursiyoyi, sai ga wani wanda yake tun fil azal ya zauna a mazauninsa. Rigarsa ta yi fari fat kamar ƙanƙara; gashin kansa sun yi fari kamar ulu. Kursiyinsa kuma harshen wuta, dukan ƙafafun kursiyin masu kama da keken yaƙin, wuta ne.
Jeg blev ved at se, indtil Stole bleve satte frem, og den Gamle af Dage satte sig; hans Klæder vare hvide som Sne og Haaret paa hans Hoved som ren Uld, hans Stol var Ildsluer, Hjulene derpaa brøndende Ild.
10 Kogin wuta yana gudu, yana fitowa daga gabansa. Dubun dubbai sun yi masa hidima; dubu goma sau dubu goma sun tsaya a gabansa. Aka zauna don shari’a, aka kuma buɗe littattafai.
En Strøm af Ild brød frem og gik ud fra ham; tusinde Gange tusinde tjente ham, og ti Tusinde Gange ti Tusinde stode for ham; Retten blev sat og Bøgerne opladte.
11 “Sa’an nan na ci gaba da kallo saboda kalmomin fariyar da wannan ƙaho yake furtawa. Na yi ta kallo har sai da aka yanke dabbar, aka kuma hallaka jikinta a cikin wuta.
Da saa jeg til, fordi man havde hørt de store Ord, som Hornet havde talt; jeg saa til, indtil Dyret blev ihjelslaget og dets Legeme lagt øde og givet hen til at brændes i Ilden.
12 (An tuɓe sauran dabbobin daga mulkinsu, amma aka bar su su rayu na wani lokaci.)
Og hvad de øvrige Dyr angaar, var deres Magt forbi, og dem havde det været givet, hvor længe de skulde leve til Tid og Stund.
13 “A wahayina na dare, na ga a gabana wani kamar ɗan mutum yana saukowa tare da gizagizan sama. Ya kusaci Wannan wanda yake Tun fil azal aka kuma kai shi gabansa.
Jeg vedblev at se i Synerne om Natten, og se, med Himmelens Skyer kom der en som en Menneskens Søn, og han kom lige hen til den Gamle af Dage, og blev ført frem for ham.
14 Aka ba shi mulki, daraja da kuma mafificin iko; dukan mutane, da al’ummai, da mutane daga kowane harshe suka yi masa sujada. Mulkinsa kuwa dawwammamen mulki ne da ba zai ƙare ba, sarautarsa kuma ba ta taɓa lalacewa.
Og ham blev givet Magt og Ære og Rige, og alle Folk, Stammer og Tungemaal skulde tjene ham; hans Herredømme er et evigt Herredømme, som ikke forgaar, og hans Rige et uforkrænkeligt.
15 “Ni, Daniyel, ruhuna ya damu ƙwarai, kuma wahayin da ya ratsa tunanina ya dame ni.
For mig, Daniel, blev min Aand i det legemlige Hylster bedrøvet, og mit Hoveds Syner forfærdede mig.
16 Sai na matsa kusa da ɗaya daga cikin waɗanda suke tsaye a can, na tambaye shi gaskiya ma’anar waɗannan al’amura. “Don haka sai ya faɗa mini, ya kuma ba ni fassarar waɗannan al’amura.
Jeg gik frem til een af dem, som stode der, for at søge Vished af ham om alt dette; og han sagde mig det og kundgjorde mig Udtydningen paa Tingene.
17 ‘Waɗannan manyan dabbobi huɗu, Masarautai ne huɗu waɗanda za su taso a duniya.
Disse store Dyr, af hvilke der er fire, betyde, at fire Konger skulle opstaa af Jorden.
18 Amma tsarkaka na Mafi Ɗaukaka za su karɓi wannan sarauta, za su kuwa mallake ta har abada, I, har abada abadin.’
Men den Højestes hellige skulle modtage Riget og besidde Riget evindelig, ja, indtil Evighedernes Evighed.
19 “Sa’an nan kuma sai na so in san ma’anar wannan dabba ta huɗu, wadda ta yi dabam da sauran dabbobin da suke da matuƙar bantsoro, da take da haƙoran ƙarfe da kuma farcen tagulla, dabbar ta ragargaje ta cinye abin da ta kama, ta kuma tattaka duk abin da ya rage a ƙarƙashin ƙafafunta.
Da vilde jeg gerne have Vished angaaende det fjerde Dyr, som var anderledes end alle de andre, meget forfærdeligt, havde Jerntænder og Kobberkløer, aad, knuste og nedtraadte det overblevne med sine Fødder,
20 Na kuma so in gane game da ƙahonin nan guda goma da suke a kanta da kuma game da ƙahon nan da ya fito, wanda aka tumɓuke ƙahoni uku a gabansa, ƙahon nan da yake da idanu da bakin da yake furta manyan maganganun fariya, wanda ya yi kamar ya fi sauran girma.
og angaaende de ti Horn, som vare paa dets Hoved, samt det andet, som skød op, og for hvilke tre faldt; og dette var det Horn, som havde Øjne og en Mund, der talte store Ting, og hvis Udseende var større end de andres ved Siden af det.
21 Ina cikin dubawa, sai ga wannan ƙaho yana yaƙi da tsarkaka yana kuma cin nasara a kansu,
Jeg havde set, at samme Horn førte Krig imod de hellige og fik Overhaand over dem,
22 sai da Wannan wanda yake tun fil azal ya zo ya furta hukunci, aka kuma ba tsarkaka na Mafi Ɗaukaka gaskiya, lokaci kuwa ya cika sai suka karɓi mulki.
indtil den Gamle af Dage kom, og Retten blev tilkendt den Højestes hellige, og Tiden kom, da de hellige toge Riget i Besiddelse.
23 “Sai ya ba ni wannan bayani, ‘Dabbar nan ta huɗu, ita ce mulki na huɗu da zai bayyana a duniya. Zai bambanta da dukan sauran mulkoki, zai kuma cinye dukan duniya, yă tattake ta, yă kuma ragargaje ta.
Han sagde saaledes: Det fjerde Dyr betyder, at der skal være et fjerde Rige paa Jorden, som skal blive anderledes end alle Rigerne; og det skal opæde al Jorden og søndertræde den og knuse den.
24 Ƙahonin nan goma, sarakuna ne goma waɗanda za su taso daga wannan mulki. Bayansu kuma, wani sarki zai taso, wanda ya sha dabam da waɗanda suka riga shi. Zai rinjayi sarakunan nan uku.
Men de ti Horn betyde, at der af samme Rige skal opstaa ti Konger; og en anden skal opstaa efter dem, og han skal være anderledes end de foregaaende og nedtrykke tre Konger.
25 Zai yi maganar saɓo a kan Mafi Ɗaukaka, zai kuma tsananta wa tsarkaka yă kuma yi ƙoƙarin sāke lokuta da shari’u. Za a miƙa tsarkaka a hannunsa na wani lokaci, lokuta da kuma rabin lokaci.
Og han skal tale Ord imod den Højeste og undertrykke den Højestes hellige og tænke paa at forandre Tider og Lov, og de skulle gives i hans Haand indtil een Tid og Tider og en halv Tid.
26 “‘Amma majalisa za tă yi zama, za a karɓe ikonsa, a kuma hallaka shi gaba ɗaya har abada.
Derefter skal Retten sættes, og man skal fratage ham hans Magt for at ødelægge og tilintetgøre den indtil Enden.
27 Sa’an nan za a ba da mulki, iko da girma na mulkokin da suke a ƙarƙashin dukan sammai ga tsarkaka, mutane na Mafi Ɗaukaka. Mulkinsa kuwa mulki ne marar matuƙa, kuma dukan masu mulki za su yabe shi, su kuma yi masa biyayya.’
Men Riget og Herredømmet og Rigernes Magt under al Himmelen skal gives til et Folk af den Højestes hellige; hans Rige er et evigt Rige, og alle Herredømmer skulle tjene og lyde ham.
28 “Wannan shi ne ƙarshen batun. Ni, Daniyel na damu ƙwarai da irin tunanina, kuma fuskata ta rikice, amma na riƙe batun a zuciyata.”
Hermed var Ordet til Ende. Mig, Daniel, forvirrede mine Tanker meget, og jeg Skiftede Farve; men jeg bevarede Ordet i mit Hjerte.