< Daniyel 6 >
1 Ya gamshi Dariyus ya naɗa muƙaddasai 120 su yi shugabanci a duk fāɗin masarautar,
И бысть угодно пред царем, и постави во царстве князей сто и двадесять, еже быти им во всем царстве его,
2 ya naɗa mutum uku a bisa waɗannan muƙaddasan, Daniyel yana ɗaya daga cikin mutum ukun nan. Sai aka sa muƙaddasan nan a ƙarƙashin waɗannan uku ɗin domin kada sarki ya yi hasarar kome.
над ними же три чиновники, от нихже бе Даниил един, дабы отдавали им князи слово, яко да царю не стужают.
3 To, Daniyel dai ya yi ficce a cikin shugabannin nan uku har da muƙaddasan ma, saboda waɗansu halaye nagari da yake da su, wanda ya sa sarki ya yi shiri ya ɗora shi a kan dukan mulkinsa.
И бе Даниил над ними, яко дух бяше преизюбилен в нем, и царь постави его над всем царством своим.
4 A kan haka, shugabannin nan uku da muƙaddasan nan suka yi ƙoƙari su sami wani laifi a kan Daniyel a yadda yake tafiyar da aikin shugabancinsa, amma ba su samu ba. Ba su same shi da wani laifin cin hanci ba, domin shi amintacce ne kuma babu wani aibi a kansa ko rashin kula.
Чиновницы же и князи искаху вины обрести на Даниила: и всякия вины и соблазна и греха не обретоша на него, яко верен бяше.
5 A ƙarshe waɗannan mutane suka ce; “Ba za mu taɓa samun wani laifin da za mu kama Daniyel da shi ba, sai dai ko abin ya shafi dokar Allahnsa.”
И реща чиновницы не обрящем на Даниила вины, аще не в законех Бога его.
6 Saboda haka shugabannin nan suka haɗu da muƙaddasan nan suka tafi wurin sarki a ƙungiyance suka ce, “Ya Sarki Dariyus, ranka yă daɗe!
Тогда чиновницы и князи предсташа царю и реша ему: Дарие царю, во веки живи:
7 Shugabannin masarauta, da masu mulki, da muƙaddasai, da mashawarta da gwamnoni duk sun amince cewa sarki yă kafa doka yă kuma yi umarni cewa a cikin kwana talatin nan gaba duk wanda ya yi addu’a ga wani allah ko mutum, in ba a gare ka ba, ya sarki, jefa shi cikin kogon zakoki.
совещаша вси иже во царстве твоем воеводы и князи, ипати и обладающии странами, еже уставити устав царский и укрепити предел, яко аще кто попросит прошения от всякаго бога и человека до дний тридесяти, разве точию от тебе, царю, да ввержен будет в ров левский:
8 Yanzu, ya sarki, sai ka yi umarni ka kuma yi shi a rubuce saboda kada a canja shi, bisa ga dokar Medes da Farisa, waɗanda ba a iya sokewa.”
ныне убо, царю, устави предел и положи писание, яко да не изменится заповедь Мидска и Персска, (да никтоже преступит ея).
9 Sai Sarki Dariyus ya ba da umarnin a rubuce.
Тогда царь Дарий повеле вписати заповедь.
10 To, da Daniyel ya ji labarin cewa an fitar da doka, sai ya tafi gidansa a ɗakinsa na sama inda tagogin ɗakin suke duban wajen Urushalima. Sau uku yakan durƙusa yă yi addu’a yana yin godiya ga Allahnsa, kamar yadda ya saba yi.
Даниил же егда уведе, яко заповедь вчинися, вниде в дом свой: дверцы же отверсты ему в горнице его противу Иерусалима, в три же времена дне бяше прекланяя колена своя, моляся и исповедаяся пред Богом своим, якоже бе творя прежде.
11 Sai waɗannan mutane suka tafi a ƙungiyance suka kuma iske Daniyel yana addu’a yana roƙon Allah yă taimake shi.
Тогда мужие онии наблюдоша и обретоша Даниила просяща и молящася Богу своему,
12 Sai suka tafi wurin sarki suka yi masa magana game da dokar mulkinsa, suka ce, “Ashe, ba ka yi doka cewa a cikin kwana talatin nan gaba duk wanda aka tarar yana addu’a ga wani allah ko mutum in ba kai ba, ya sarki, za ka jefa shi a cikin ramin zakoki ba?” Sarki ya amsa ya ce, “Dokar tana nan daram bisa ga dokar Medes da Farisa, waɗanda ba a iya sokewa.”
и пришедше реша пред царем: царю, не вчинил ли еси ты предела, яко да всяк человек, иже аще попросит у всякаго бога и человека прошения до тридесяти дний, но точию у тебе, царю, да ввержется в ров левск? И рече царь: истинно слово, и заповедь Мидска и Персска не мимоидет.
13 Sai suka ce wa sarki, “Daniyel ɗin nan, wanda yake ɗaya daga cikin waɗanda aka kwaso daga Yahuda, bai kula da kai ba, ya sarki, balle fa dokar da ka yi. Har yanzu yana addu’a sau uku a rana.”
Тогда отвещаша пред царем и глаголаша: Даниил, иже от сынов плена Иудейска, не покорися заповеди твоей (и не раде) о пределе, егоже вчинил еси: в три бо времена дне просит у Бога своего прошений своих.
14 Da sarki ya ji haka, sai ya damu sosai, ya ƙudura yă ceci Daniyel, ya yi ta fama har fāɗuwar rana yadda zai yi yă kuɓutar da shi.
Тогда царь, яко слышав слово сие, зело опечалися о нем, и о Данииле пряшеся еже избавити его, и бе даже до вечера пряся еже избавити его.
15 Sai mutanen nan suka je wurin sarki a ƙungiyance suka ce masa, “Ka tuna, ya sarki; cewa bisa ga dokar Medes da Farisa, babu umarni ko dokar da sarki ya yi da za a iya sokewa.”
Тогда мужие онии глаголаша царю: веждь, царю яко Мидом и Персом не леть есть пременити всякаго предела и устава, егоже царь уставит.
16 Saboda haka sai sarki ya ba da umarni suka kuma kawo Daniyel suka jefa shi cikin ramin zakoki. Sarki ya ce wa Daniyel, “Bari Allahn nan wanda kake bauta masa kullum, yă cece ka!”
Тогда царь рече, и приведоша Даниила и ввергоша его в ров левск. И рече царь Даниилу: Бог твой, Емуже ты служиши присно, Той избавит тя.
17 Aka kawo dutsen aka rufe bakin ramin, sa’an nan sarki ya hatimce shi da zobensa da kuma zoban manyan mutanensa, don kada wani yă canja yanayin Daniyel.
И принесоша камень един и возложиша на устие рва, и запечата царь перстнем своим и перстнем вельмож своих, да не изменится деяние о Данииле.
18 Sa’an nan sarki ya koma fadarsa ya kwana bai ci ba, kuma babu wata liyafar da aka kawo masa. Ya kuma kāsa barci.
И отиде царь в дом свой и ляже без вечери, и яди не внесоша к нему: и сон отступи от него. И заключи Бог уста львом, и не стужиша Даниилу.
19 Gari yana wayewa, sai sarki ya tashi ya hanzarta zuwa ramin zakoki.
Тогда царь воста заутра на свете и со тщанием прииде ко рву левску.
20 Da ya yi kusa da ramin zakokin, sai ya kira Daniyel da muryar mai cike da damuwa ya ce, “Daniyel bawan Allah mai rai, ko Allahn nan naka wanda kake bauta wa kullum, ya iya cetonka daga zakoki?”
И егда приближися ко рву, возопи гласом крепким: Данииле, рабе Бога живаго! Бог твой, Емуже ты служиши присно, возможе ли избавити тя из уст львовых?
21 Sai Daniyel ya amsa ya ce, “Ran sarki, yă daɗe!
И рече Даниил цареви: царю, во веки живи:
22 Allahna ya aiko da mala’ikansa, ya kuwa rufe bakunan zakoki. Ba su yi mini rauni ba, gama an same ni marar laifi ne a gabansa. Ban kuwa taɓa yin wani abu marar kyau a gabanka ba, ya sarki.”
Бог мой посла Ангела Своего и затвори уста львов, и не вредиша мене, яко обретеся пред Ним правда моя, и пред тобою, царю, согрешения не сотворих.
23 Sai sarki ya cika da murna ƙwarai, ya kuma yi umarni a ciro Daniyel daga ramin zakoki. Kuma da aka fito da Daniyel daga ramin, ba a sami wani rauni a jikinsa ba, domin ya dogara ga Allahnsa.
Тогда царь вельми возвеселися о нем и рече Даниила извести из рва. И изведен бысть Даниил из рва, и всякаго тления не обретеся на нем яко верова в Бога своего.
24 Sai sarki ya umarta, a kawo mutanen nan da suka yi wa Daniyel maƙarƙashiya, a tura su, da’ya’yansu, da matansu cikin ramin zakoki. Kafin ma su kai ƙurewar ramin, sai zakoki suka hallaka su suka yayyage su, suka yi kaca-kaca da su.
И рече царь, и приведоша мужы оклеветавшыя Даниила и в ров левск ввергоша я и сыны их и жены их: и не доидоша дна рва, даже соодолеша им львы и вся кости их истончиша.
25 Sa’an nan Sarki Dariyus ya rubuta wa dukan mutane, da al’ummai da kuma mutanen dukan harsunan a duk fāɗin ƙasar. “Bari yă yi nasara sosai!
Тогда Дарий царь написа всем людем, племеном, языком, живущым во всей земли: мир вам да умножится:
26 “Na fitar da doka cewa a cikin dukan iyakar ƙasar mulkina, dole mutane su ji tsoro su kuma girmama Allah na Daniyel.
от лица моего заповедася заповедь сия во всей земли царства моего, да будут трепещуще и боящеся от лица Бога Даниилова, яко Той есть Бог живый и пребываяй во веки, и царство Его не разсыплется, и власть Его до конца:
27 Yakan kuɓutar ya kuma ceci;
подемлет и избавляет, и творит знамения и чудеса на небеси и на земли, иже избави Даниила от уст львовых.
28 Daniyel kuwa ya bunkasa a lokacin mulkin Dariyus da kuma mulkin Sairus na Farisa.
Даниил же управляше во царстве Дариеве и во царстве Кира Персянина.