< Daniyel 6 >

1 Ya gamshi Dariyus ya naɗa muƙaddasai 120 su yi shugabanci a duk fāɗin masarautar,
Il plut à Darius d’établir sur le royaume cent vingt satrapes; afin qu’il y en eût dans tout son royaume;
2 ya naɗa mutum uku a bisa waɗannan muƙaddasan, Daniyel yana ɗaya daga cikin mutum ukun nan. Sai aka sa muƙaddasan nan a ƙarƙashin waɗannan uku ɗin domin kada sarki ya yi hasarar kome.
Et au-dessus d’eux, trois princes, dont un était Daniel; afin que les satrapes leur rendissent compte, et que le roi n’eût aucune peine.
3 To, Daniyel dai ya yi ficce a cikin shugabannin nan uku har da muƙaddasan ma, saboda waɗansu halaye nagari da yake da su, wanda ya sa sarki ya yi shiri ya ɗora shi a kan dukan mulkinsa.
Ainsi Daniel était au-dessus de tous les princes et satrapes, parce que l’esprit de Dieu était plus abondant en lui.
4 A kan haka, shugabannin nan uku da muƙaddasan nan suka yi ƙoƙari su sami wani laifi a kan Daniyel a yadda yake tafiyar da aikin shugabancinsa, amma ba su samu ba. Ba su same shi da wani laifin cin hanci ba, domin shi amintacce ne kuma babu wani aibi a kansa ko rashin kula.
Or le roi pensait à l’établir sur tout le royaume; d’où les princes et les satrapes cherchaient à trouver un moyen d’accusation contre Daniel du côté du roi; et ils ne purent découvrir aucune cause de suspicion, parce qu’il était fidèle, et qu’aucune faute et aucun soupçon ne se trouvaient en lui.
5 A ƙarshe waɗannan mutane suka ce; “Ba za mu taɓa samun wani laifin da za mu kama Daniyel da shi ba, sai dai ko abin ya shafi dokar Allahnsa.”
Ces hommes dirent donc: Nous ne trouverons contre ce Daniel aucun moyen d’accusation, si ce n’est dans la loi de son Dieu.
6 Saboda haka shugabannin nan suka haɗu da muƙaddasan nan suka tafi wurin sarki a ƙungiyance suka ce, “Ya Sarki Dariyus, ranka yă daɗe!
Alors les princes et les satrapes surprirent le roi, et lui parlèrent ainsi: Darius, roi, vivez à jamais.
7 Shugabannin masarauta, da masu mulki, da muƙaddasai, da mashawarta da gwamnoni duk sun amince cewa sarki yă kafa doka yă kuma yi umarni cewa a cikin kwana talatin nan gaba duk wanda ya yi addu’a ga wani allah ko mutum, in ba a gare ka ba, ya sarki, jefa shi cikin kogon zakoki.
Tous les princes de votre royaume, les magistrats et les satrapes, les sénateurs et les juges, sont d’avis qu’un décret impérial paraisse, et un édit: Que quiconque fera quelque demande à quelque dieu ou à quelque homme que ce soit d’ici à trente jours, sinon à vous, ô roi, qu’il soit jeté dans la fosse aux lions.
8 Yanzu, ya sarki, sai ka yi umarni ka kuma yi shi a rubuce saboda kada a canja shi, bisa ga dokar Medes da Farisa, waɗanda ba a iya sokewa.”
Maintenant donc, ô roi, confirmez cet avis, et écrivez le décret, afin que ce qui a été statué par les Mèdes et par les Perses ne soit pas changé, et qu’il ne soit permis à personne de le transgresser.
9 Sai Sarki Dariyus ya ba da umarnin a rubuce.
Or le roi Darius proposa l’édit, et le publia.
10 To, da Daniyel ya ji labarin cewa an fitar da doka, sai ya tafi gidansa a ɗakinsa na sama inda tagogin ɗakin suke duban wajen Urushalima. Sau uku yakan durƙusa yă yi addu’a yana yin godiya ga Allahnsa, kamar yadda ya saba yi.
Lorsque Daniel eut appris cela, c’est-à-dire la loi portée, il entra dans sa maison; et, les fenêtres ouvertes, il fléchissait les genoux dans sa chambre haute trois fois le jour, tourné vers Jérusalem, et il adorait, et rendait grâce devant son Dieu, comme il avait accoutumé de faire auparavant.
11 Sai waɗannan mutane suka tafi a ƙungiyance suka kuma iske Daniyel yana addu’a yana roƙon Allah yă taimake shi.
Ces hommes donc, épiant très soigneusement, trouvèrent Daniel priant et suppliant son Dieu.
12 Sai suka tafi wurin sarki suka yi masa magana game da dokar mulkinsa, suka ce, “Ashe, ba ka yi doka cewa a cikin kwana talatin nan gaba duk wanda aka tarar yana addu’a ga wani allah ko mutum in ba kai ba, ya sarki, za ka jefa shi a cikin ramin zakoki ba?” Sarki ya amsa ya ce, “Dokar tana nan daram bisa ga dokar Medes da Farisa, waɗanda ba a iya sokewa.”
Et, venant auprès du roi, ils lui dirent touchant l’édit: Ô roi, est-ce que vous n’avez pas décidé que tout homme qui jusqu’après trente jours prierait quelqu’un des dieux ou des hommes, sinon vous, ô roi, serait jeté dans la fosse aux lions? Le roi, leur répondant, dit: Cette parole est véritable, selon le décret des Mèdes et des Perses, qu’il n’est pas permis de transgresser.
13 Sai suka ce wa sarki, “Daniyel ɗin nan, wanda yake ɗaya daga cikin waɗanda aka kwaso daga Yahuda, bai kula da kai ba, ya sarki, balle fa dokar da ka yi. Har yanzu yana addu’a sau uku a rana.”
Alors, répondant, ils dirent au roi: Daniel, un des enfants de la captivité de Juda, n’a tenu aucun compte de votre loi et de l’édit que vous avez porté; mais trois fois par jour il fait sa prière accoutumée.
14 Da sarki ya ji haka, sai ya damu sosai, ya ƙudura yă ceci Daniyel, ya yi ta fama har fāɗuwar rana yadda zai yi yă kuɓutar da shi.
Lorsque le roi eut entendu cette parole, il fut extrêmement contristé, et il appliqua son cœur à délivrer Daniel, et jusqu’au coucher du soleil il travaillait à le sauver.
15 Sai mutanen nan suka je wurin sarki a ƙungiyance suka ce masa, “Ka tuna, ya sarki; cewa bisa ga dokar Medes da Farisa, babu umarni ko dokar da sarki ya yi da za a iya sokewa.”
Mais ces hommes, comprenant le roi, lui dirent: Sachez, ô roi, que c’est une loi des Mèdes et des Perses, que tout décret que le roi a porté ne peut être changé.
16 Saboda haka sai sarki ya ba da umarni suka kuma kawo Daniyel suka jefa shi cikin ramin zakoki. Sarki ya ce wa Daniyel, “Bari Allahn nan wanda kake bauta masa kullum, yă cece ka!”
Alors le roi ordonna; et ils amenèrent Daniel, et le jetèrent dans la fosse aux lions. Et le roi dit à Daniel: Ton Dieu, que tu adores toujours, c’est lui qui te délivrera.
17 Aka kawo dutsen aka rufe bakin ramin, sa’an nan sarki ya hatimce shi da zobensa da kuma zoban manyan mutanensa, don kada wani yă canja yanayin Daniyel.
Et l’on apporta une pierre, et elle fut placée sur l’ouverture de la fosse, que le roi scella de son anneau et de l’anneau de ses grands, afin qu’il ne fût rien fait contre Daniel.
18 Sa’an nan sarki ya koma fadarsa ya kwana bai ci ba, kuma babu wata liyafar da aka kawo masa. Ya kuma kāsa barci.
Et le roi s’en alla à sa maison, et il se coucha sans avoir soupe; et l’on n’apporta pas de nourriture devant lui; de plus, le sommeil même s’éloigna de lui.
19 Gari yana wayewa, sai sarki ya tashi ya hanzarta zuwa ramin zakoki.
Après cela, le roi, s’étant levé au point du jour, alla en se hâtant à la fosse aux lions;
20 Da ya yi kusa da ramin zakokin, sai ya kira Daniyel da muryar mai cike da damuwa ya ce, “Daniyel bawan Allah mai rai, ko Allahn nan naka wanda kake bauta wa kullum, ya iya cetonka daga zakoki?”
Et, s’étant approché de la fosse, il appela Daniel d’une voix mêlée de larmes, et lui parla ainsi: Daniel, serviteur du Dieu vivant, ton Dieu que tu sers toujours a-t-il pu te délivrer des lions?
21 Sai Daniyel ya amsa ya ce, “Ran sarki, yă daɗe!
Et Daniel, répondant au roi, dit: Ô roi, vivez à jamais;
22 Allahna ya aiko da mala’ikansa, ya kuwa rufe bakunan zakoki. Ba su yi mini rauni ba, gama an same ni marar laifi ne a gabansa. Ban kuwa taɓa yin wani abu marar kyau a gabanka ba, ya sarki.”
Mon Dieu a envoyé son ange, et a fermé les gueules des lions, et ils ne m’ont pas fait de mal, parce que devant lui la justice a été trouvée en moi; mais même devant vous, ô roi, je n’ai pas fait de faute.
23 Sai sarki ya cika da murna ƙwarai, ya kuma yi umarni a ciro Daniyel daga ramin zakoki. Kuma da aka fito da Daniyel daga ramin, ba a sami wani rauni a jikinsa ba, domin ya dogara ga Allahnsa.
Alors le roi se réjouit beaucoup à cause de lui, et il ordonna que Daniel fût tiré de la fosse; et Daniel fut tiré de la fosse, et on ne trouva aucune blessure en lui, parce qu’il avait cru en son Dieu.
24 Sai sarki ya umarta, a kawo mutanen nan da suka yi wa Daniyel maƙarƙashiya, a tura su, da’ya’yansu, da matansu cikin ramin zakoki. Kafin ma su kai ƙurewar ramin, sai zakoki suka hallaka su suka yayyage su, suka yi kaca-kaca da su.
Or, le roi ayant commandé, les hommes qui avaient accusé Daniel furent amenés, et jetés dans la fosse aux lions, eux, leurs fils et leurs femmes; et ils n’étaient pas parvenus jusqu’au pavé de la fosse, que les bons les saisirent et brisèrent tous leurs os.
25 Sa’an nan Sarki Dariyus ya rubuta wa dukan mutane, da al’ummai da kuma mutanen dukan harsunan a duk fāɗin ƙasar. “Bari yă yi nasara sosai!
Alors Darius le roi écrivit à tous les peuples, aux tribus, et aux langues, habitant dans toute la terre: Que la paix se multiplie pour vous.
26 “Na fitar da doka cewa a cikin dukan iyakar ƙasar mulkina, dole mutane su ji tsoro su kuma girmama Allah na Daniyel.
Par moi est établi le décret, que dans tout mon empire et mon royaume, on tremble et on craigne le Dieu de Daniel, car c’est lui qui est le Dieu vivant et éternel dans les siècles; et son royaume ne sera pas détruit, et sa puissance subsistera éternellement.
27 Yakan kuɓutar ya kuma ceci;
C’est lui qui est le libérateur et le sauveur, faisant des prodiges et des merveilles dans le ciel et sur la terre; lui qui a délivré Daniel de la fosse aux lions.
28 Daniyel kuwa ya bunkasa a lokacin mulkin Dariyus da kuma mulkin Sairus na Farisa.
Or Daniel continua d’être en dignité jusqu’au règne de Darius, et au règne de Cyrus, roi de Perse.

< Daniyel 6 >