< Daniyel 6 >

1 Ya gamshi Dariyus ya naɗa muƙaddasai 120 su yi shugabanci a duk fāɗin masarautar,
It pleased Darius to set over the kingdom a hundred and twenty satraps, which should be over the whole kingdom,
2 ya naɗa mutum uku a bisa waɗannan muƙaddasan, Daniyel yana ɗaya daga cikin mutum ukun nan. Sai aka sa muƙaddasan nan a ƙarƙashin waɗannan uku ɗin domin kada sarki ya yi hasarar kome.
and over them three presidents, of whom Daniel was one, that the satraps might give accounts to them, and the king might have no damage.
3 To, Daniyel dai ya yi ficce a cikin shugabannin nan uku har da muƙaddasan ma, saboda waɗansu halaye nagari da yake da su, wanda ya sa sarki ya yi shiri ya ɗora shi a kan dukan mulkinsa.
Then this Daniel was eminent above the presidents and satraps, because an excellent spirit was in him; and the king thought to set him over the whole realm.
4 A kan haka, shugabannin nan uku da muƙaddasan nan suka yi ƙoƙari su sami wani laifi a kan Daniyel a yadda yake tafiyar da aikin shugabancinsa, amma ba su samu ba. Ba su same shi da wani laifin cin hanci ba, domin shi amintacce ne kuma babu wani aibi a kansa ko rashin kula.
Then the presidents and satraps sought to find occasion against Daniel in relation to the kingdom; but they could find no occasion nor fault; because he was faithful, and no error nor fault was found in him.
5 A ƙarshe waɗannan mutane suka ce; “Ba za mu taɓa samun wani laifin da za mu kama Daniyel da shi ba, sai dai ko abin ya shafi dokar Allahnsa.”
Then said these men, We shall not find any occasion against this Daniel, unless we find it against him concerning the law of his God.
6 Saboda haka shugabannin nan suka haɗu da muƙaddasan nan suka tafi wurin sarki a ƙungiyance suka ce, “Ya Sarki Dariyus, ranka yă daɗe!
Then these presidents and satraps rushed together to the king, and spake thus to him: King Darius, live forever!
7 Shugabannin masarauta, da masu mulki, da muƙaddasai, da mashawarta da gwamnoni duk sun amince cewa sarki yă kafa doka yă kuma yi umarni cewa a cikin kwana talatin nan gaba duk wanda ya yi addu’a ga wani allah ko mutum, in ba a gare ka ba, ya sarki, jefa shi cikin kogon zakoki.
All the presidents of the kingdom, the governors and the satraps, the counsellors and the prefects, have consulted together to establish a royal statute, and to make a firm decree, that whoever shall ask a petition of any god or man for thirty days, save of thee, O king, he shall be cast into the den of lions.
8 Yanzu, ya sarki, sai ka yi umarni ka kuma yi shi a rubuce saboda kada a canja shi, bisa ga dokar Medes da Farisa, waɗanda ba a iya sokewa.”
Now, O king, establish the decree and sign the writing that it be not changed, according to the law of the Medes and Persians which altereth not.
9 Sai Sarki Dariyus ya ba da umarnin a rubuce.
Wherefore King Darius signed the writing and the decree.
10 To, da Daniyel ya ji labarin cewa an fitar da doka, sai ya tafi gidansa a ɗakinsa na sama inda tagogin ɗakin suke duban wajen Urushalima. Sau uku yakan durƙusa yă yi addu’a yana yin godiya ga Allahnsa, kamar yadda ya saba yi.
Now when Daniel knew that the writing was signed, he went into his house, his windows being open in his chamber toward Jerusalem, and three times a day he kneeled upon his knees, and prayed and gave thanks before his God, as he had done before.
11 Sai waɗannan mutane suka tafi a ƙungiyance suka kuma iske Daniyel yana addu’a yana roƙon Allah yă taimake shi.
Then these men rushed together, and found Daniel praying and making supplication before his God.
12 Sai suka tafi wurin sarki suka yi masa magana game da dokar mulkinsa, suka ce, “Ashe, ba ka yi doka cewa a cikin kwana talatin nan gaba duk wanda aka tarar yana addu’a ga wani allah ko mutum in ba kai ba, ya sarki, za ka jefa shi a cikin ramin zakoki ba?” Sarki ya amsa ya ce, “Dokar tana nan daram bisa ga dokar Medes da Farisa, waɗanda ba a iya sokewa.”
Then they came near and spake before the king concerning the royal decree: Hast thou not signed a decree, that every man who shall ask a petition of any god or man within thirty days, save of thee, O king, shall be cast into the den of lions? The king answered and said, The thing is true, according to the law of the Medes and Persians, which altereth not.
13 Sai suka ce wa sarki, “Daniyel ɗin nan, wanda yake ɗaya daga cikin waɗanda aka kwaso daga Yahuda, bai kula da kai ba, ya sarki, balle fa dokar da ka yi. Har yanzu yana addu’a sau uku a rana.”
Then answered they and said before the king, Daniel, who is of the sons of the captives of Judah, regardeth not thee, O king, nor the decree which thou hast signed, but maketh his petition three times a day.
14 Da sarki ya ji haka, sai ya damu sosai, ya ƙudura yă ceci Daniyel, ya yi ta fama har fāɗuwar rana yadda zai yi yă kuɓutar da shi.
Then the king, when he heard these words, was much troubled, and set his heart to deliver him; and he labored till the going down of the sun to deliver him.
15 Sai mutanen nan suka je wurin sarki a ƙungiyance suka ce masa, “Ka tuna, ya sarki; cewa bisa ga dokar Medes da Farisa, babu umarni ko dokar da sarki ya yi da za a iya sokewa.”
Then these men assembled before the king, and said to the king, Know, O king, that the law of the Medes and Persians is, that no decree or statute which the king establisheth may be changed.
16 Saboda haka sai sarki ya ba da umarni suka kuma kawo Daniyel suka jefa shi cikin ramin zakoki. Sarki ya ce wa Daniyel, “Bari Allahn nan wanda kake bauta masa kullum, yă cece ka!”
Then the king commanded that they should bring Daniel and cast him into the den of lions. And the king spake and said to Daniel, May thy God, whom thou servest continually, deliver thee!
17 Aka kawo dutsen aka rufe bakin ramin, sa’an nan sarki ya hatimce shi da zobensa da kuma zoban manyan mutanensa, don kada wani yă canja yanayin Daniyel.
And a stone was brought and laid upon the mouth of the den; and the king sealed it with his own signet, and with the signet of his lords, that nothing concerning Daniel might be changed.
18 Sa’an nan sarki ya koma fadarsa ya kwana bai ci ba, kuma babu wata liyafar da aka kawo masa. Ya kuma kāsa barci.
Then the king went to his palace, and passed the night fasting, and suffered not the concubines to be brought to him; and his sleep went from him.
19 Gari yana wayewa, sai sarki ya tashi ya hanzarta zuwa ramin zakoki.
Then the king arose very early in the morning, and went in haste to the den of lions.
20 Da ya yi kusa da ramin zakokin, sai ya kira Daniyel da muryar mai cike da damuwa ya ce, “Daniyel bawan Allah mai rai, ko Allahn nan naka wanda kake bauta wa kullum, ya iya cetonka daga zakoki?”
And when he came to the den, he cried with a troubled voice to Daniel; and the king spake and said to Daniel, O Daniel, servant of the living God, has thy God, whom thou servest continually, been able to deliver thee from the lions?
21 Sai Daniyel ya amsa ya ce, “Ran sarki, yă daɗe!
Then said Daniel to the king, O king, live forever!
22 Allahna ya aiko da mala’ikansa, ya kuwa rufe bakunan zakoki. Ba su yi mini rauni ba, gama an same ni marar laifi ne a gabansa. Ban kuwa taɓa yin wani abu marar kyau a gabanka ba, ya sarki.”
My God hath sent his angel, and hath shut the lions' mouths, so that they have not hurt me; forasmuch as before him innocency was found in me; and also before thee, O king, have I done no wrong.
23 Sai sarki ya cika da murna ƙwarai, ya kuma yi umarni a ciro Daniyel daga ramin zakoki. Kuma da aka fito da Daniyel daga ramin, ba a sami wani rauni a jikinsa ba, domin ya dogara ga Allahnsa.
Then was the king exceedingly glad, and commanded that they should take Daniel up out of the den. So Daniel was taken up out of the den, and no manner of hurt was found upon him, because he trusted in his God.
24 Sai sarki ya umarta, a kawo mutanen nan da suka yi wa Daniyel maƙarƙashiya, a tura su, da’ya’yansu, da matansu cikin ramin zakoki. Kafin ma su kai ƙurewar ramin, sai zakoki suka hallaka su suka yayyage su, suka yi kaca-kaca da su.
And the king commanded, and they brought those men who had accused Daniel, and cast them into the den of lions, them, their children, and their wives; and the lions had the mastery of them, and broke all their bones before they came to the bottom of the den.
25 Sa’an nan Sarki Dariyus ya rubuta wa dukan mutane, da al’ummai da kuma mutanen dukan harsunan a duk fāɗin ƙasar. “Bari yă yi nasara sosai!
Then King Darius wrote to all people, nations, and languages, that dwell in all the earth: Peace be multiplied to you!
26 “Na fitar da doka cewa a cikin dukan iyakar ƙasar mulkina, dole mutane su ji tsoro su kuma girmama Allah na Daniyel.
I make a decree, that in every government of my kingdom men tremble and fear before the God of Daniel; for he is the living God that endureth forever, and whose kingdom shall not be destroyed, and whose dominion shall endure to the end.
27 Yakan kuɓutar ya kuma ceci;
It is he that delivereth and rescueth, and worketh signs and wonders in heaven and in earth, who hath delivered Daniel from the power of the lions.
28 Daniyel kuwa ya bunkasa a lokacin mulkin Dariyus da kuma mulkin Sairus na Farisa.
This Daniel prospered in the reign of Darius, and in the reign of Cyrus the Persian.

< Daniyel 6 >