< Daniyel 5 >

1 Sarki Belshazar ya yi babban biki domin dubban hakimansa ya kuma sha ruwan inabi tare da su.
Paççah Belyşassaree aazırne cune insanıs xədın otxhun-ulyodğiy hele, manbışika çaxır ulyoğa.
2 Yayinda Belshazar yake shan ruwan inabi, sai ya umarta a kawo zinariya da azurfan da Nebukadnezzar mahaifinsa ya kwaso daga haikali a Urushalima, saboda sarki da hakimansa, da matansa da ƙwarƙwaransa su sha da su.
Belyşassaree çaxır ulyodğuyle qiyğa əmr haa'a, cune dekkee Navuxodonosoree İyerusalimeene Allahne xaançe qığı'iyn k'ınəəğəyniy nuk'rayn g'abbı cusqa alleva. Paççahıs, cune k'anebınbışika, cune yedaaşika, cune caariyebışika mançee çaxır ulyoğas ıkkiykan.
3 Sai suka kawo kayan zinariyan nan da aka kwaso daga haikalin Allah a Urushalima, sarki kuwa da hakimansa, da matansa, da ƙwarƙwaransa suka yi ta sha da su.
Manke maqa Allahne İyerusalimeene xaançe qığı'iyn k'ınəəğəyn g'abbı adayle. Paççahee vucee, cus k'anebınbışe, cune yedaaşe, cune caariyebışe mançee çaxır ulyoğa.
4 Yayinda suke shan ruwan inabin, sai suka yabi allolin zinariya da azurfa, da na tagulla, da na ƙarfe, da na itace da kuma na dutse.
Manbışe çaxır ulyoğa-ulyoğa k'ınəəğəyke, nuk'rayke, yezıke, yivayke, yiveke, g'ayeyke hav'uyn allahar axtı qaa'a vuxha.
5 Nan da nan sai ga yatsotsin hannun mutum sun bayyana, suna yin rubutu a kan shafen bangon, kusa da wurin da ake ajiye fitilar fadar sarki. Sarki kuwa yana ganin hannun yayinda yake rubutu.
Mane gahıl maa'ad, insanne xılen t'ubar g'ece giyğal, paççahne sarayne xənne axtıne şamdamıs k'anene cabırıl, mane t'ubaaşe hucoomecad oyk'anan. Paççahık'le mane xılen oyk'anang'a, g'ece ıxha.
6 Sai fuskarsa ta ruɗe, ya kuma ji tsoro ƙwarai har gwiwoyinsa suka yi ta bugun juna, ƙafafunsa kuma suka rasa ƙarfi.
Man g'acu, paççahne aq'vaylin rangcad ayk'an, mana mançile məxı'r qəyq'ən giyğal, q'aratsabı çiçıs qiyxhar, iykaras dəxə axva.
7 Sai sarki ya kira masu dabo, masanan taurari da masu duba, a kawo su, ya kuma ce wa masu hikima na Babilon, “Duk wanda ya karanta wannan rubutu ya kuma faɗa mini abin da yake nufi, za a sa masa rigar shunayya, a kuma sa masa sarƙar zinariya a wuyansa, zai zama na uku a cikin masu mulkin ƙasar.”
Paççahee it'umna ts'ir hav'u eyhen: – Cadu ha'anbı, Baabilin k'oran ək'elynanbı, falçer zasqa see'e! Abıyne Baabilyne k'orane ək'elynanbışik'le paççahee inəxüd eyhe: – Şavaayiy man otk'unin, nenvayiy uvhu mang'ulqa paççahaaşin karbı alya'as, gardanaqab k'ınəəğəyna tsep qaa'as, cuker paççahiyvalina xhebır'esda insan ha'as.
8 Sa’an nan sai dukan masu hikima suka zo ciki, amma ba su iya karanta rubutun ba ko su faɗa wa sarki abin da yake nufi.
Paççahın gırgın k'oran ək'elynanbı aqa ikkepç'eeyiyb, manbışisse man qətqəsıd əxə deş, paççahık'le maa nenvayiy otk'unva eyhesıd əxə deş.
9 Saboda haka Sarki Belshazar ya firgita ƙwarai kuma fuskarsa ta ƙara ruɗewa. Hakimansa kuma suka rikice.
Manke paççah sık'ırar geer qəyq'ən, aq'vad hak xhinne qexhe. Mang'us k'anebınbıb nyaqame vuxhesınbı aaxva.
10 Sai sarauniya, da jin muryoyi na sarki da na hakimansa, ta shiga babban ɗakin liyafar. Ta ce, “Ya sarki, ranka yă daɗe! Kada ka firgita! Kada fuskarka ta ruɗe!
Kraliçayk'le paççahıniy cune k'anenbışin sesbı g'ayxhı mihmanarnane gozeeqa qiyeele. Kraliçee eyhen: – Paççah, geer qa'ana! Nişilecar qı'məyq'ən, hak xhinne qımexhe.
11 Akwai wani mutum a masarautarka wanda yake da ruhun alloli masu tsarki a cikinsa. A zamanin mahaifinka an gane cewa yana da basira da hazaka da hikima kamar na alloli. Sarki Nebukadnezzar mahaifinka, mahaifinka sarki, na ce, ya naɗa shugaban masu dabo, da masu sihiri, masanan taurari da kuma masu duba.
Yiğne paççahiyvalee, muq'addasne allahaaşin rı'hnana sa insan vor. Yiğne dekkıne gahıl, mana gırgın kar ats'anava, ək'elikanava, allahaaşina xhinne k'orana ək'elynanava qıvaats'a ıxha. Yiğne dekkee, paççah Navuxodonosoree, mana sehirbazaaşina, cadu ha'anbışda, Baabilyne k'orane ək'elynanbışda, falçeeşina xərna gixhxhı.
12 Wannan mutum Daniyel, wanda sarki ya kira Belteshazar, an gane yana da ruhu nagari, da ilimi, da ganewa don yin fassarar mafarkai, da bayyana ma’anar kacici-kacici, da warware al’amura masu wuya. Ka kira Daniyel shi kuwa zai faɗa maka abin da rubutun nan yake nufi.”
Mane insanın do Daniyalniy vod. Qiyğa paççahee mang'un do badal hı'ı, Belyteşassar ha'a. Mana k'orana ək'elynana, ats'alynana, geer ək'elikana, nyak'bı nen eyhenbıyiy eyhes əxəna, dağamne karbışde sirrılqa hixharas əxəna, alikkı-gikkiyke vuk'ul qığaahana insan ıxha. Eyhe, vasqa mana Daniyal qot'lecen, mang'veeyid vak'le maa'ad nenvayiy otk'un eyhesın.
13 Saboda haka aka kawo Daniyel a gaban sarki, sai sarki ya ce masa, “Kai ne Daniyel ɗin nan, ɗaya daga cikin kamammu waɗanda mahaifina sarki ya kawo daga Yahuda?
Manke paççahısqa Daniyal ayra'a, paççahee mang'uke qiyghanan: – Yizde paççah dekkee, Yahudeençe ögilqa gyapq'ır qabıyne çühüt'yaaşina dişde Daniyal ğu vor?
14 Na sami labari cewa kana da ruhun alloli a cikinka da kuma basira, da hazaka da kuma fitacciyar hikima.
Zak'le yiğne hək'ee g'ayxhiyn, vaqa allahaaşin rı'h, nuraaniyvalla, ats'al, k'orana ək'el vobva.
15 An kawo masu hikima da masu dabo a gabana domin su karanta wannan rubutu su kuma faɗa mini abin da yake nufi, amma ba su iya ba.
Zasqa k'oran ək'elynanbıyiy sehirbazar abı, maa'ad hucooyiy otk'unva qətqı' eyhesva. Man nen eyhenenva manbışisse zak'le eyhes əxı' deş.
16 Na sami labari cewa kana iya ba da fassara da kuma warware matsaloli masu wuya. In har ka iya karanta wannan rubutun ka kuma faɗa mini abin da yake nufi, za a sa maka riga shunayya, a kuma sa sarƙar zinariya a wuyanka. Za ka zama na uku a cikin masu mulkin ƙasar.”
Yiğneme hək'ee zak'le g'ayxhiyn, ğu alikkı-gikkiyke vuk'ul yugba qığahava. Həşdemee vasse maa'ad otk'uniyn qətqı', maa'ad nenvayiy otk'un eyhes əxeene, yiğne tanalqa paççahaaşin karbı alya'as, gardanaqab k'ınəəğəyna tsep qaa'as. Yizde paççahiyvaleyir xhebır'esda insan ha'as.
17 Sai Daniyel ya amsa wa sarki ya ce, “Za ka iya ajiye kyautar wa kanka ko kuma ka ba wa wani. Duk da haka, zan karanta wa sarki rubutun, in kuma faɗa abin da yake nufi.
Daniyalee paççahık'le eyhen: – Ğu helesın paybı vascad ixhe, helesva eyhen mukaafatbıd maa sang'us hele. Maa'ad otk'uniynıd zıcad qətqı' vak'le eyhesın.
18 “Ya sarki, Allah Mafi Ɗaukaka ya ba mahaifinka Nebukadnezzar sarauta, da girma, da ɗaukaka, da martaba.
Paççah, Allah-Ta'aalee yiğne dekkıs Navuxodonosorus paççahiyvalla, xəbvalla, guc, qıvaatsıvallaniy huvu.
19 Saboda irin matsayin da ya ba shi, dukan mutane da al’ummai da kuma dukan harsuna suka ji tsoronsa suka yi rawar jiki a gabansa. Bisa ga ganin damarsa yakan kashe wani, ya bar wani da rai, haka kuma yakan ɗaukaka wani, ya ƙasƙantar da wani.
Allahee mang'us huvuyne xəbvalike gırgın xalq'bı, milletbı, menne-menne mizyaaşil yuşan haa'anbı mang'ule qəvəyq'ən vuxha. Manava uvhumee, manbışde caneeqa zeze ooxha vuxha. Paççahıs gyapt'as vukkananbı gyabat'a, g'avkkas vukkanbı g'ookka, axtı qaa'as vukkananbı axtı qaa'a, avqa qaa'asınbıb avqa qaa'a vuxha.
20 Amma da lokacin da zuciyarsa ta cika da girman kai ta kuma taurare, sai aka kore shi daga gadon sarautarsa, aka raba shi kuma da darajarsa.
Mang'une yik'en zale ğayrı deşdava eyhemee, mang'vee q'ı't'y keççumee, mana paççahne taxtıle gyaqqana, xəbvallab xıleençe g'ooşena.
21 Aka kore shi daga cikin mutane aka kuma ba shi tunani irin na dabba; ya yi zama tare da jakunan jeji, ya kuma ci ciyawa kamar shanu; jikinsa kuma ya jiƙe da raɓa, har zuwa lokacin da ya gane, ashe, Allah Maɗaukaki ne mai iko duka a kan dukan mulkoki a duniya, yake kuma ba da mulki ga duk wanda ya ga dama.
Mana insanaaşençer g'e'eşşena, mang'una ək'elib həyvanaaşina ək'el xhinnecab qooxhe. Mana əməleeşika axva ıxha, yatsın xhinneyib mang'vee ok' opxhan vuxha. Mang'un tanıd xəəne çiyin hoyğal ıxha. Allah Ta'aalee insanaaşin paççahiyvallabıd vuk'lek ıkkekkava qiyğa mang'ulqa hiyxhar. Mang'vee, Cus ıkkanar paççahiyvalina xərna ha'ana.
22 “Amma kai ɗansa, Ya Belshazar, ba ka ƙasƙantar da kanka ba, ko da yake ka san wannan duka.
Vak'lemee, mang'une duxayk'le Belyşassarık'le man gırgın ats'a ıxha. Ğumee, Allahne ögil k'ıl qıxhesde cigee,
23 A maimakon, sai ka nuna wa Ubangiji na sama girman kai. Ka sa aka kawo maka su kwaf na zinariya daga haikalinsa, da kai da hakimanka, da matanka da ƙwarƙwaranka kuka sha ruwan inabi da su. Kuka yabi allolin zinariya da na azurfa, da na tagulla, da na baƙin ƙarfe, da na itace, da na dutse waɗanda ba sa ji, ba sa gani, ba sa da gane kome. Amma ba ka girmama Allah ba, wanda ranka da dukan harkokinka suna a hannunsa.
ğucar ğu xəəne Xudavandayne ögil axtı qı'ı. Mang'une xaadın g'abbı vasqa allyı'ı ğunad, vas k'anebınbışed, yiğne yedaaşed, yiğne caariyebışed mançeençe çaxırbı ulyodğu. Ğu k'ınəəğəyke, nuk'rayke, yezake, yivayke, yiveke, g'ayeyke hav'une allahaaşilqa şukur hav'u. Mane allahaaşik'le g'iyxhed deş, g'eced deş, manbışik'le vuççudud ats'a deş. Vas nafas huvuna, ğu haa'ana gırgına işib vaats'ana Allah ğu axtıcar qı'ı deş.
24 Saboda haka ya aiko da hannun da ya yi rubutun nan.
Mançil-allad Mang'vee, xıl g'axuvu, man ok'anas alikkı.
25 “Wannan shi ne rubutun da aka yi, Mene, mene, tekel, farsin
Cabırıl invaniy otk'un vod: MENE, MENE, TEKEL, PARSİN.
26 “Abin da kalmomin nan suke nufi shi ne, “Mene, Allah ya ƙayyade yawan kwanakin mulkinka ya kuma kawo su ga ƙarshe.
Otk'uninçina mə'na ina vob: MENE (qətqəs) – Allahee ğu paççahnan yiğbı qətqı', manbı ç'əvı'iynbı.
27 “Tekel, An kuma auna ka a ma’auni aka tarar ka kāsa.
TEKEL (gyoorkas) – ğu terezyugul gyoorku geer sibıkra qarı.
28 “Feres, An raba mulkinka aka ba wa Medes da Farisa.”
PARSİN (bit'al ha'as) – yiğna paççahiyvalla bit'al hav'u, Midiyabışisiy Farsbışis huvu.
29 Sai Belshazar ya umarta, aka sa wa Daniyel riga mai shunayya, aka sa sarƙar zinariya a wuyansa, aka kuma yi shela, cewa yanzu shi ne na uku a cikin masu mulkin ƙasar.
Manke Belyşassarne əmrıka Daniyalılqa paççahaaşin tanalinbı alya'a, gardanaqa k'ınəəğəyna tsep qaa'a, mang'uke paççahiyvalina xhebır'esda insan hı'ıva ses adaççe.
30 A wannan dare aka kashe Belshazar, sarkin Babiloniyawa,
Manecar xəmde Baabilyna paççah Belyşassar g'ek'ana.
31 Dariyus mutumin Medes kuwa ya karɓi mulkin, yana da shekara sittin da biyu.
Mang'une cigee yixhts'ale q'ölle sennana Midiyabışikena Dara donana paççah eyxhe.

< Daniyel 5 >