< Daniyel 5 >

1 Sarki Belshazar ya yi babban biki domin dubban hakimansa ya kuma sha ruwan inabi tare da su.
Le roi Balthasar donna un grand festin à ses grands, au nombre de mille; et, en présence de ces mille, il buvait du vin.
2 Yayinda Belshazar yake shan ruwan inabi, sai ya umarta a kawo zinariya da azurfan da Nebukadnezzar mahaifinsa ya kwaso daga haikali a Urushalima, saboda sarki da hakimansa, da matansa da ƙwarƙwaransa su sha da su.
Sous l’influence de la boisson, Balthasar ordonna d’apporter les vases d’or et d’argent, que son père Nabuchodonosor avait enlevés du temple de Jérusalem, afin que le roi, ses grands, ses épouses et ses concubines s’en servissent pour boire.
3 Sai suka kawo kayan zinariyan nan da aka kwaso daga haikalin Allah a Urushalima, sarki kuwa da hakimansa, da matansa, da ƙwarƙwaransa suka yi ta sha da su.
Aussitôt on apporta les vases d’or qui avaient été enlevés de l’enceinte du temple de Dieu à Jérusalem. Le roi, ses grands, ses épouses et ses concubines s’en servirent pour boire.
4 Yayinda suke shan ruwan inabin, sai suka yabi allolin zinariya da azurfa, da na tagulla, da na ƙarfe, da na itace da kuma na dutse.
Ils burent du vin et glorifièrent les Dieux d’or et d’argent, d’airain, de fer, de bois et de pierre.
5 Nan da nan sai ga yatsotsin hannun mutum sun bayyana, suna yin rubutu a kan shafen bangon, kusa da wurin da ake ajiye fitilar fadar sarki. Sarki kuwa yana ganin hannun yayinda yake rubutu.
Au même moment, des doigts d’une main d’homme apparurent et écrivirent, face au candélabre, sur la chaux de la paroi du palais royal, et le roi vit cette main détachée qui écrivait.
6 Sai fuskarsa ta ruɗe, ya kuma ji tsoro ƙwarai har gwiwoyinsa suka yi ta bugun juna, ƙafafunsa kuma suka rasa ƙarfi.
Alors le roi changea de couleur, son esprit fut frappé de crainte; les attaches de ses reins se détendirent et ses genoux s’entrechoquèrent.
7 Sai sarki ya kira masu dabo, masanan taurari da masu duba, a kawo su, ya kuma ce wa masu hikima na Babilon, “Duk wanda ya karanta wannan rubutu ya kuma faɗa mini abin da yake nufi, za a sa masa rigar shunayya, a kuma sa masa sarƙar zinariya a wuyansa, zai zama na uku a cikin masu mulkin ƙasar.”
Le roi cria avec force qu’on amenât les sorciers, les astrologues et les augures; puis il prit la parole et dit aux sages de Babylone: "Tout homme qui lira cette inscription et m’en fera connaître le sens sera vêtu de pourpre, portera un collier d’or au cou et gouvernera en tiers le royaume."
8 Sa’an nan sai dukan masu hikima suka zo ciki, amma ba su iya karanta rubutun ba ko su faɗa wa sarki abin da yake nufi.
Tous les sages du roi étaient entrés; mais ils ne purent lire l’inscription ni en faire connaître le sens au roi.
9 Saboda haka Sarki Belshazar ya firgita ƙwarai kuma fuskarsa ta ƙara ruɗewa. Hakimansa kuma suka rikice.
Le roi Balthasar fut alors extrêmement effrayé, sa figure se décomposa, et ses grands furent bouleversés.
10 Sai sarauniya, da jin muryoyi na sarki da na hakimansa, ta shiga babban ɗakin liyafar. Ta ce, “Ya sarki, ranka yă daɗe! Kada ka firgita! Kada fuskarka ta ruɗe!
La reine, en raison des propos du roi et de ses grands, se rendit dans la salle du festin, elle prit la parole et dit: "Vive le roi à jamais! Que tes pensées cessent de t’épouvanter et que ton visage ne change pas de couleur!
11 Akwai wani mutum a masarautarka wanda yake da ruhun alloli masu tsarki a cikinsa. A zamanin mahaifinka an gane cewa yana da basira da hazaka da hikima kamar na alloli. Sarki Nebukadnezzar mahaifinka, mahaifinka sarki, na ce, ya naɗa shugaban masu dabo, da masu sihiri, masanan taurari da kuma masu duba.
Il est un homme dans ton royaume, qui est pénétré de l’esprit des Dieux saints, et chez qui, du temps de ton père, se sont rencontrées une perspicacité, une intelligence et une sagesse dignes des Dieux; aussi le roi Nabuchodonosor, ton père, l’a-t-il établi chef des magiciens, des devins, des astrologues et des augures, oui ton propre père, le roi!
12 Wannan mutum Daniyel, wanda sarki ya kira Belteshazar, an gane yana da ruhu nagari, da ilimi, da ganewa don yin fassarar mafarkai, da bayyana ma’anar kacici-kacici, da warware al’amura masu wuya. Ka kira Daniyel shi kuwa zai faɗa maka abin da rubutun nan yake nufi.”
Parce qu’un esprit supérieur, la science, l’intelligence, l’art d’interpréter les songes, d’éclaircir les énigmes, de résoudre les difficultés se sont rencontrés chez ce Daniel, que le roi avait surnommé Beltchaçar. Que Daniel soit donc mandé, et il dévoilera ce que cela signifie."
13 Saboda haka aka kawo Daniyel a gaban sarki, sai sarki ya ce masa, “Kai ne Daniyel ɗin nan, ɗaya daga cikin kamammu waɗanda mahaifina sarki ya kawo daga Yahuda?
Aussitôt Daniel fut introduit devant le roi; celui-ci prit la parole et lui dit: "C’Est donc toi ce Daniel, qui fait partie du groupe des exilés de Juda que le roi mon père a emmenés de Judée!
14 Na sami labari cewa kana da ruhun alloli a cikinka da kuma basira, da hazaka da kuma fitacciyar hikima.
J’Ai ouï dire que tu es rempli de l’esprit des Dieux, et qu’il se rencontre chez toi de la perspicacité, de l’intelligence et une sagesse supérieure.
15 An kawo masu hikima da masu dabo a gabana domin su karanta wannan rubutu su kuma faɗa mini abin da yake nufi, amma ba su iya ba.
Or, on a amené en ma présence les sages, les devins pour lire cette inscription et m’en faire connaître le sens; mais ils sont incapables de me révéler la signification de la chose.
16 Na sami labari cewa kana iya ba da fassara da kuma warware matsaloli masu wuya. In har ka iya karanta wannan rubutun ka kuma faɗa mini abin da yake nufi, za a sa maka riga shunayya, a kuma sa sarƙar zinariya a wuyanka. Za ka zama na uku a cikin masu mulkin ƙasar.”
Mais de toi j’ai ouï dire que tu sais donner des interprétations et résoudre les difficultés. Donc, si tu peux lire cette inscription et m’en faire connaître le sens, tu seras revêtu de pourpre, un collier d’or ornera ton cou, et tu gouverneras en tiers le royaume."
17 Sai Daniyel ya amsa wa sarki ya ce, “Za ka iya ajiye kyautar wa kanka ko kuma ka ba wa wani. Duk da haka, zan karanta wa sarki rubutun, in kuma faɗa abin da yake nufi.
Alors Daniel répliqua en disant au roi: "Garde tes dons pour toi, et gratifie d’autres de tes présents; toutefois je lirai l’inscription au roi et je lui en ferai connaître le sens.
18 “Ya sarki, Allah Mafi Ɗaukaka ya ba mahaifinka Nebukadnezzar sarauta, da girma, da ɗaukaka, da martaba.
O roi, le Dieu suprême avait donné à ton père Nabuchodonosor royauté, grandeur, majesté et magnificence.
19 Saboda irin matsayin da ya ba shi, dukan mutane da al’ummai da kuma dukan harsuna suka ji tsoronsa suka yi rawar jiki a gabansa. Bisa ga ganin damarsa yakan kashe wani, ya bar wani da rai, haka kuma yakan ɗaukaka wani, ya ƙasƙantar da wani.
Et à cause de la grandeur qui lui avait été octroyée, nations, peuples et langues tremblaient tous de peur devant lui: il tuait qui il voulait, laissait vivre qui il voulait, élevait ou abaissait qui il voulait.
20 Amma da lokacin da zuciyarsa ta cika da girman kai ta kuma taurare, sai aka kore shi daga gadon sarautarsa, aka raba shi kuma da darajarsa.
Mais lorsque son cœur s’enorgueillit et que son esprit s’enhardit jusqu’à l’arrogance, il fut précipité de son trône royal et se vit dépouillé de sa majesté.
21 Aka kore shi daga cikin mutane aka kuma ba shi tunani irin na dabba; ya yi zama tare da jakunan jeji, ya kuma ci ciyawa kamar shanu; jikinsa kuma ya jiƙe da raɓa, har zuwa lokacin da ya gane, ashe, Allah Maɗaukaki ne mai iko duka a kan dukan mulkoki a duniya, yake kuma ba da mulki ga duk wanda ya ga dama.
Il fut chassé de la société des hommes, et son cœur devint semblable à celui des bêtes; sa demeure fut avec les ânes sauvages, on lui donna comme aux bœufs de l’herbe pour nourriture, et son corps fut humecté par la rosée du ciel, jusqu’à ce qu’il reconnût que le Dieu suprême est maître de la royauté des hommes et qu’il y appelle qui lui plaît.
22 “Amma kai ɗansa, Ya Belshazar, ba ka ƙasƙantar da kanka ba, ko da yake ka san wannan duka.
Et toi, son fils Balthasar, tu n’as pas humilié ton cœur, bien que tu fusses instruit de tout cela.
23 A maimakon, sai ka nuna wa Ubangiji na sama girman kai. Ka sa aka kawo maka su kwaf na zinariya daga haikalinsa, da kai da hakimanka, da matanka da ƙwarƙwaranka kuka sha ruwan inabi da su. Kuka yabi allolin zinariya da na azurfa, da na tagulla, da na baƙin ƙarfe, da na itace, da na dutse waɗanda ba sa ji, ba sa gani, ba sa da gane kome. Amma ba ka girmama Allah ba, wanda ranka da dukan harkokinka suna a hannunsa.
Tu t’es insurgé contre le maître du ciel, en faisant apporter devant toi les vases de son temple pour y boire du vin, toi, tes grands, tes épouses et tes concubines; tu as célébré les Dieux d’argent et d’or, d’airain, de fer, de bois et de pierre, qui ne voient, ni n’entendent, ni ne savent rien. Quant au Dieu qui tient ton âme en ses mains et qui dirige toutes tes voies, tu ne l’as pas honoré.
24 Saboda haka ya aiko da hannun da ya yi rubutun nan.
C’Est pourquoi une main détachée a été envoyée par lui, et cette inscription a été tracée.
25 “Wannan shi ne rubutun da aka yi, Mene, mene, tekel, farsin
Or, voici l’inscription qui a été tracée: MENÊ, MENÊ, TEKÊL, OUFARSIN.
26 “Abin da kalmomin nan suke nufi shi ne, “Mene, Allah ya ƙayyade yawan kwanakin mulkinka ya kuma kawo su ga ƙarshe.
Et telle est l’explication de ces mots: MENÊ Dieu a compté les jours de ta royauté et en a décidé la fin;
27 “Tekel, An kuma auna ka a ma’auni aka tarar ka kāsa.
TEKÊL tu as été pesé dans la balance et trouvé trop léger;
28 “Feres, An raba mulkinka aka ba wa Medes da Farisa.”
PERES ton royaume a été divisé et donné aux Mèdes et aux Perses."
29 Sai Belshazar ya umarta, aka sa wa Daniyel riga mai shunayya, aka sa sarƙar zinariya a wuyansa, aka kuma yi shela, cewa yanzu shi ne na uku a cikin masu mulkin ƙasar.
Aussitôt Balthasar donna l’ordre de revêtir Daniel de pourpre, de lui mettre un collier d’or au cou et de proclamer qu’il gouvernerait en tiers le royaume.
30 A wannan dare aka kashe Belshazar, sarkin Babiloniyawa,
Cette même nuit Balthasar, le roi Chaldéen, fut mis à mort.
31 Dariyus mutumin Medes kuwa ya karɓi mulkin, yana da shekara sittin da biyu.
Et Darius le Mède reçut la royauté à l’âge de soixante-deux ans.

< Daniyel 5 >