< Daniyel 5 >

1 Sarki Belshazar ya yi babban biki domin dubban hakimansa ya kuma sha ruwan inabi tare da su.
Belshazzar the king made a great feast for a thousand of his noblemen, and he drank wine in front of all one thousand of them.
2 Yayinda Belshazar yake shan ruwan inabi, sai ya umarta a kawo zinariya da azurfan da Nebukadnezzar mahaifinsa ya kwaso daga haikali a Urushalima, saboda sarki da hakimansa, da matansa da ƙwarƙwaransa su sha da su.
While Belshazzar tasted the wine, he gave orders to bring the containers made of gold or silver that Nebuchadnezzar his father had taken out of the temple in Jerusalem, from which he, his noblemen, and his wives and concubines could drink.
3 Sai suka kawo kayan zinariyan nan da aka kwaso daga haikalin Allah a Urushalima, sarki kuwa da hakimansa, da matansa, da ƙwarƙwaransa suka yi ta sha da su.
The servants brought the gold containers that had been taken out of the temple, the house of God, in Jerusalem. The king, his noblemen, and his wives and concubines drank from them.
4 Yayinda suke shan ruwan inabin, sai suka yabi allolin zinariya da azurfa, da na tagulla, da na ƙarfe, da na itace da kuma na dutse.
They drank the wine and praised their idols made of gold and silver, bronze, iron, wood, and stone.
5 Nan da nan sai ga yatsotsin hannun mutum sun bayyana, suna yin rubutu a kan shafen bangon, kusa da wurin da ake ajiye fitilar fadar sarki. Sarki kuwa yana ganin hannun yayinda yake rubutu.
At that moment the fingers of a human hand appeared in front of the lampstand and wrote on the plaster wall in the king's palace. The king could see part of the hand as it wrote.
6 Sai fuskarsa ta ruɗe, ya kuma ji tsoro ƙwarai har gwiwoyinsa suka yi ta bugun juna, ƙafafunsa kuma suka rasa ƙarfi.
Then the king's face changed and his thoughts frightened him; his limbs could not support him, and his knees were knocking together.
7 Sai sarki ya kira masu dabo, masanan taurari da masu duba, a kawo su, ya kuma ce wa masu hikima na Babilon, “Duk wanda ya karanta wannan rubutu ya kuma faɗa mini abin da yake nufi, za a sa masa rigar shunayya, a kuma sa masa sarƙar zinariya a wuyansa, zai zama na uku a cikin masu mulkin ƙasar.”
The king shouted a command to bring in those who claimed to speak with the dead, wise men, and astrologers. The king said to those known for their wisdom in Babylon, “Whoever explains this writing and its meaning will be clothed with purple and will have a gold chain around his neck. He will have the authority of the third highest ruler in the kingdom.”
8 Sa’an nan sai dukan masu hikima suka zo ciki, amma ba su iya karanta rubutun ba ko su faɗa wa sarki abin da yake nufi.
Then all the king's men who were known for their wisdom came in, but they could not read the writing or explain its meaning to the king.
9 Saboda haka Sarki Belshazar ya firgita ƙwarai kuma fuskarsa ta ƙara ruɗewa. Hakimansa kuma suka rikice.
Then King Belshazzar was greatly alarmed and the look on his face changed. His noblemen were perplexed.
10 Sai sarauniya, da jin muryoyi na sarki da na hakimansa, ta shiga babban ɗakin liyafar. Ta ce, “Ya sarki, ranka yă daɗe! Kada ka firgita! Kada fuskarka ta ruɗe!
Now the queen came into the banquet house because of what the king and his nobles had said. The queen said, “King, live forever! Do not let your thoughts trouble you. Do not let the look on your face change.
11 Akwai wani mutum a masarautarka wanda yake da ruhun alloli masu tsarki a cikinsa. A zamanin mahaifinka an gane cewa yana da basira da hazaka da hikima kamar na alloli. Sarki Nebukadnezzar mahaifinka, mahaifinka sarki, na ce, ya naɗa shugaban masu dabo, da masu sihiri, masanan taurari da kuma masu duba.
There is a man in your kingdom who has the spirit of the holy gods. In the days of your father, light and understanding and wisdom like the wisdom of the gods was found in him. King Nebuchadnezzar, your father the king, made him chief of the magicians, as well as chief of those who speak with the dead, of the wise men, and of the astrologers.
12 Wannan mutum Daniyel, wanda sarki ya kira Belteshazar, an gane yana da ruhu nagari, da ilimi, da ganewa don yin fassarar mafarkai, da bayyana ma’anar kacici-kacici, da warware al’amura masu wuya. Ka kira Daniyel shi kuwa zai faɗa maka abin da rubutun nan yake nufi.”
An excellent spirit, knowledge, understanding, interpreting of dreams, explaining riddles and solving problems—these qualities were found in this man Daniel, whom the king named Belteshazzar. Now call for Daniel and he will tell you the meaning of what has been written.”
13 Saboda haka aka kawo Daniyel a gaban sarki, sai sarki ya ce masa, “Kai ne Daniyel ɗin nan, ɗaya daga cikin kamammu waɗanda mahaifina sarki ya kawo daga Yahuda?
Then Daniel was brought before the king. The king said to him, “You are that Daniel, one of the people of the exiles of Judah, whom my father the king brought out of Judah.
14 Na sami labari cewa kana da ruhun alloli a cikinka da kuma basira, da hazaka da kuma fitacciyar hikima.
I have heard about you, that the spirit of the gods is in you, and that light and understanding and excellent wisdom are found in you.
15 An kawo masu hikima da masu dabo a gabana domin su karanta wannan rubutu su kuma faɗa mini abin da yake nufi, amma ba su iya ba.
Now the men known for wisdom and those who claim to speak with the dead have been brought in before me to read this writing and make known to me its interpretation, but they could not make known the interpretation of it.
16 Na sami labari cewa kana iya ba da fassara da kuma warware matsaloli masu wuya. In har ka iya karanta wannan rubutun ka kuma faɗa mini abin da yake nufi, za a sa maka riga shunayya, a kuma sa sarƙar zinariya a wuyanka. Za ka zama na uku a cikin masu mulkin ƙasar.”
I have heard that you can give interpretations and solve problems. Now if you can read the writing and tell me its meaning, you will be clothed with purple and have a gold chain placed around your neck, and you will have the authority of the third highest ruler in the kingdom.”
17 Sai Daniyel ya amsa wa sarki ya ce, “Za ka iya ajiye kyautar wa kanka ko kuma ka ba wa wani. Duk da haka, zan karanta wa sarki rubutun, in kuma faɗa abin da yake nufi.
Then Daniel answered before the king, “Let your gifts be for yourself, and give your rewards to another person. Nevertheless, I will read the writing to you, king, and will tell you the meaning.
18 “Ya sarki, Allah Mafi Ɗaukaka ya ba mahaifinka Nebukadnezzar sarauta, da girma, da ɗaukaka, da martaba.
As for you, king, the Most High God gave Nebuchadnezzar your father the kingdom, greatness, honor, and majesty.
19 Saboda irin matsayin da ya ba shi, dukan mutane da al’ummai da kuma dukan harsuna suka ji tsoronsa suka yi rawar jiki a gabansa. Bisa ga ganin damarsa yakan kashe wani, ya bar wani da rai, haka kuma yakan ɗaukaka wani, ya ƙasƙantar da wani.
Because of the greatness God gave him, all peoples, nations, and languages trembled and feared him. He put to death those he wanted to die, and he kept alive those he wished to live. He raised up those he wanted, and he humbled those he wished.
20 Amma da lokacin da zuciyarsa ta cika da girman kai ta kuma taurare, sai aka kore shi daga gadon sarautarsa, aka raba shi kuma da darajarsa.
But when his heart was arrogant and his spirit was hardened so that he acted presumptuously, he was brought down from his kingly throne, and they took away his majesty.
21 Aka kore shi daga cikin mutane aka kuma ba shi tunani irin na dabba; ya yi zama tare da jakunan jeji, ya kuma ci ciyawa kamar shanu; jikinsa kuma ya jiƙe da raɓa, har zuwa lokacin da ya gane, ashe, Allah Maɗaukaki ne mai iko duka a kan dukan mulkoki a duniya, yake kuma ba da mulki ga duk wanda ya ga dama.
He was driven away from humanity, he had the mind of an animal, and he lived with the wild donkeys. He ate grass like an ox. His body was wet with the dew from the heavens until he learned that the Most High God rules over the kingdoms of people and that he sets over them anyone he wishes.
22 “Amma kai ɗansa, Ya Belshazar, ba ka ƙasƙantar da kanka ba, ko da yake ka san wannan duka.
You his son, Belshazzar, have not humbled your heart, even though you knew all this.
23 A maimakon, sai ka nuna wa Ubangiji na sama girman kai. Ka sa aka kawo maka su kwaf na zinariya daga haikalinsa, da kai da hakimanka, da matanka da ƙwarƙwaranka kuka sha ruwan inabi da su. Kuka yabi allolin zinariya da na azurfa, da na tagulla, da na baƙin ƙarfe, da na itace, da na dutse waɗanda ba sa ji, ba sa gani, ba sa da gane kome. Amma ba ka girmama Allah ba, wanda ranka da dukan harkokinka suna a hannunsa.
You have lifted yourself up against the Lord of heaven. From his house they brought you the containers that you, your nobles, your wives and your concubines drank wine from, and you praised the idols made of silver and gold, bronze, iron, wood, and stone—idols that do not see, hear, or know anything. You have not honored the God who holds your breath in his hand and who knows all your ways.
24 Saboda haka ya aiko da hannun da ya yi rubutun nan.
Then God sent out a hand from his presence and this writing was done.
25 “Wannan shi ne rubutun da aka yi, Mene, mene, tekel, farsin
This is the writing that was done: 'Mene, Mene, Tekel, and Pharsin.'
26 “Abin da kalmomin nan suke nufi shi ne, “Mene, Allah ya ƙayyade yawan kwanakin mulkinka ya kuma kawo su ga ƙarshe.
This is its meaning: 'Mene,' 'God has numbered your kingdom and brought it to an end.'
27 “Tekel, An kuma auna ka a ma’auni aka tarar ka kāsa.
'Tekel,' 'you are weighed in the scales and are found lacking.'
28 “Feres, An raba mulkinka aka ba wa Medes da Farisa.”
'Peres,' 'your kingdom is divided and is given to the Medes and Persians.'”
29 Sai Belshazar ya umarta, aka sa wa Daniyel riga mai shunayya, aka sa sarƙar zinariya a wuyansa, aka kuma yi shela, cewa yanzu shi ne na uku a cikin masu mulkin ƙasar.
Then Belshazzar gave a command, and they clothed Daniel with purple. A chain of gold was put around his neck, and the king made a proclamation about him that he would have the authority of the third highest ruler in the kingdom.
30 A wannan dare aka kashe Belshazar, sarkin Babiloniyawa,
That night Belshazzar, the Babylonian king, was killed,
31 Dariyus mutumin Medes kuwa ya karɓi mulkin, yana da shekara sittin da biyu.
and Darius the Mede received the kingdom when he was about sixty-two years old.

< Daniyel 5 >