< Daniyel 5 >
1 Sarki Belshazar ya yi babban biki domin dubban hakimansa ya kuma sha ruwan inabi tare da su.
Belshazzar the king has made a great feast to one thousand of his great men, and before the one thousand he is drinking wine;
2 Yayinda Belshazar yake shan ruwan inabi, sai ya umarta a kawo zinariya da azurfan da Nebukadnezzar mahaifinsa ya kwaso daga haikali a Urushalima, saboda sarki da hakimansa, da matansa da ƙwarƙwaransa su sha da su.
Belshazzar has said—while tasting the wine—to bring in the vessels of gold and of silver that his father Nebuchadnezzar had taken from the temple that [is] in Jerusalem, that the king may drink with them, and his great men, his wives, and his concubines.
3 Sai suka kawo kayan zinariyan nan da aka kwaso daga haikalin Allah a Urushalima, sarki kuwa da hakimansa, da matansa, da ƙwarƙwaransa suka yi ta sha da su.
Then they have brought in the vessels of gold that had been taken out of the temple of the house of God that [is] in Jerusalem, and the king and his great men, his wives and his concubines, have drunk with them;
4 Yayinda suke shan ruwan inabin, sai suka yabi allolin zinariya da azurfa, da na tagulla, da na ƙarfe, da na itace da kuma na dutse.
they have drunk wine, and have praised the gods of gold, and of silver, of bronze, of iron, of wood, and of stone.
5 Nan da nan sai ga yatsotsin hannun mutum sun bayyana, suna yin rubutu a kan shafen bangon, kusa da wurin da ake ajiye fitilar fadar sarki. Sarki kuwa yana ganin hannun yayinda yake rubutu.
In that hour fingers of a man’s hand have come forth, and they are writing in front of the lampstand, on the plaster of the wall of the king’s palace: and the king is seeing the extremity of the hand that is writing;
6 Sai fuskarsa ta ruɗe, ya kuma ji tsoro ƙwarai har gwiwoyinsa suka yi ta bugun juna, ƙafafunsa kuma suka rasa ƙarfi.
then the king’s countenance has changed, and his thoughts trouble him, and the joints of his loins are loosed, and his knees are striking against one another.
7 Sai sarki ya kira masu dabo, masanan taurari da masu duba, a kawo su, ya kuma ce wa masu hikima na Babilon, “Duk wanda ya karanta wannan rubutu ya kuma faɗa mini abin da yake nufi, za a sa masa rigar shunayya, a kuma sa masa sarƙar zinariya a wuyansa, zai zama na uku a cikin masu mulkin ƙasar.”
The king calls mightily, to bring up the enchanters, the Chaldeans, and the soothsayers. The king has answered and said to the wise men of Babylon, that, “Any man who reads this writing, and shows me its interpretation, he puts on purple, and a bracelet of gold [is] on his neck, and he rules third in the kingdom.”
8 Sa’an nan sai dukan masu hikima suka zo ciki, amma ba su iya karanta rubutun ba ko su faɗa wa sarki abin da yake nufi.
Then all the wise men of the king are coming up, and they are not able to read the writing, and to make known the interpretation to the king;
9 Saboda haka Sarki Belshazar ya firgita ƙwarai kuma fuskarsa ta ƙara ruɗewa. Hakimansa kuma suka rikice.
then King Belshazzar is greatly troubled, and his countenance is changing in him, and his great men are perplexed.
10 Sai sarauniya, da jin muryoyi na sarki da na hakimansa, ta shiga babban ɗakin liyafar. Ta ce, “Ya sarki, ranka yă daɗe! Kada ka firgita! Kada fuskarka ta ruɗe!
The queen, on account of the words of the king and his great men, has come up to the banquet-house. The queen has answered and said, “O king, live for all ages; do not let your thoughts trouble you, nor your countenance be changed:
11 Akwai wani mutum a masarautarka wanda yake da ruhun alloli masu tsarki a cikinsa. A zamanin mahaifinka an gane cewa yana da basira da hazaka da hikima kamar na alloli. Sarki Nebukadnezzar mahaifinka, mahaifinka sarki, na ce, ya naɗa shugaban masu dabo, da masu sihiri, masanan taurari da kuma masu duba.
there is a man in your kingdom in whom [is] the spirit of the holy gods: and in the days of your father, light, and understanding, and wisdom—as the wisdom of the gods—was found in him; and your father King Nebuchadnezzar, chief of the scribes, enchanters, Chaldeans, soothsayers, established him—your father, O king—
12 Wannan mutum Daniyel, wanda sarki ya kira Belteshazar, an gane yana da ruhu nagari, da ilimi, da ganewa don yin fassarar mafarkai, da bayyana ma’anar kacici-kacici, da warware al’amura masu wuya. Ka kira Daniyel shi kuwa zai faɗa maka abin da rubutun nan yake nufi.”
because that an excellent spirit, and knowledge, and understanding, interpreting of dreams, and showing of enigmas, and loosing of knots was found in him, in Daniel, whose name the king made Belteshazzar: now let Daniel be called, and the interpretation he shows.”
13 Saboda haka aka kawo Daniyel a gaban sarki, sai sarki ya ce masa, “Kai ne Daniyel ɗin nan, ɗaya daga cikin kamammu waɗanda mahaifina sarki ya kawo daga Yahuda?
Then Daniel has been caused to come up before the king; the king has answered and said to Daniel, “You are that Daniel who [is] of the sons of the expulsion of Judah, whom my father the king brought in out of Judah?
14 Na sami labari cewa kana da ruhun alloli a cikinka da kuma basira, da hazaka da kuma fitacciyar hikima.
And I have heard of you, that the spirit of the gods [is] in you, and light, and understanding, and excellent wisdom have been found in you.
15 An kawo masu hikima da masu dabo a gabana domin su karanta wannan rubutu su kuma faɗa mini abin da yake nufi, amma ba su iya ba.
And now, caused to come up before me have been the wise men, the enchanters, that they may read this writing, and its interpretation to cause me to know: and they are not able to show the interpretation of the thing:
16 Na sami labari cewa kana iya ba da fassara da kuma warware matsaloli masu wuya. In har ka iya karanta wannan rubutun ka kuma faɗa mini abin da yake nufi, za a sa maka riga shunayya, a kuma sa sarƙar zinariya a wuyanka. Za ka zama na uku a cikin masu mulkin ƙasar.”
and I have heard of you, that you are able to give interpretations, and to loose knots: now, behold—you are able to read the writing, and its interpretation to cause me to know—purple you put on, and a bracelet of gold [is] on your neck, and you rule third in the kingdom.”
17 Sai Daniyel ya amsa wa sarki ya ce, “Za ka iya ajiye kyautar wa kanka ko kuma ka ba wa wani. Duk da haka, zan karanta wa sarki rubutun, in kuma faɗa abin da yake nufi.
Then Daniel has answered and said before the king, “Your gifts be to yourself, and give your fee to another; nevertheless, the writing I read to the king, and the interpretation I cause him to know;
18 “Ya sarki, Allah Mafi Ɗaukaka ya ba mahaifinka Nebukadnezzar sarauta, da girma, da ɗaukaka, da martaba.
you, O king, God Most High, a kingdom, and greatness, and glory, and honor, gave to your father Nebuchadnezzar:
19 Saboda irin matsayin da ya ba shi, dukan mutane da al’ummai da kuma dukan harsuna suka ji tsoronsa suka yi rawar jiki a gabansa. Bisa ga ganin damarsa yakan kashe wani, ya bar wani da rai, haka kuma yakan ɗaukaka wani, ya ƙasƙantar da wani.
and because of the greatness that He gave to him, all peoples, nations, and languages were trembling and fearing before him: whom he willed he was slaying, and whom he willed he was keeping alive, and whom he willed he was raising up, and whom he willed he was making low;
20 Amma da lokacin da zuciyarsa ta cika da girman kai ta kuma taurare, sai aka kore shi daga gadon sarautarsa, aka raba shi kuma da darajarsa.
and when his heart was high, and his spirit was strong to act proudly, he has been caused to come down from the throne of his kingdom, and his glory they have caused to pass away from him,
21 Aka kore shi daga cikin mutane aka kuma ba shi tunani irin na dabba; ya yi zama tare da jakunan jeji, ya kuma ci ciyawa kamar shanu; jikinsa kuma ya jiƙe da raɓa, har zuwa lokacin da ya gane, ashe, Allah Maɗaukaki ne mai iko duka a kan dukan mulkoki a duniya, yake kuma ba da mulki ga duk wanda ya ga dama.
and he is driven from the sons of men, and his heart has been like with the beasts, and with the wild donkeys [is] his dwelling; they cause him to eat the herb like oxen, and by the dew of the heavens is his body wet, until he has known that God Most High is ruler in the kingdom of men, and whom He wills He raises up over it.
22 “Amma kai ɗansa, Ya Belshazar, ba ka ƙasƙantar da kanka ba, ko da yake ka san wannan duka.
And you, his son, Belshazzar, have not humbled your heart, though all this you have known;
23 A maimakon, sai ka nuna wa Ubangiji na sama girman kai. Ka sa aka kawo maka su kwaf na zinariya daga haikalinsa, da kai da hakimanka, da matanka da ƙwarƙwaranka kuka sha ruwan inabi da su. Kuka yabi allolin zinariya da na azurfa, da na tagulla, da na baƙin ƙarfe, da na itace, da na dutse waɗanda ba sa ji, ba sa gani, ba sa da gane kome. Amma ba ka girmama Allah ba, wanda ranka da dukan harkokinka suna a hannunsa.
and against the Lord of the heavens you have lifted up yourself; and the vessels of His house they have brought in before you, and you, and your great men, your wives, and your concubines, are drinking wine with them, and gods of silver, and of gold, of bronze, of iron, of wood, and of stone, that are not seeing, nor hearing, nor knowing, you have praised: and the God in whose hand [is] your breath, and all your ways, Him you have not honored.
24 Saboda haka ya aiko da hannun da ya yi rubutun nan.
Then from before Him is the extremity of the hand sent, and the writing is noted down;
25 “Wannan shi ne rubutun da aka yi, Mene, mene, tekel, farsin
and this [is] the writing that is noted down: Numbered, Numbered, Weighed, and Divided.
26 “Abin da kalmomin nan suke nufi shi ne, “Mene, Allah ya ƙayyade yawan kwanakin mulkinka ya kuma kawo su ga ƙarshe.
This [is] the interpretation of the thing: Numbered—God has numbered your kingdom, and has finished it.
27 “Tekel, An kuma auna ka a ma’auni aka tarar ka kāsa.
Weighed—You are weighed in the balances, and have been found lacking.
28 “Feres, An raba mulkinka aka ba wa Medes da Farisa.”
Divided—Your kingdom is divided, and it has been given to the Medes and Persians.”
29 Sai Belshazar ya umarta, aka sa wa Daniyel riga mai shunayya, aka sa sarƙar zinariya a wuyansa, aka kuma yi shela, cewa yanzu shi ne na uku a cikin masu mulkin ƙasar.
Then Belshazzar has spoken, and they have clothed Daniel with purple, and a bracelet of gold [is] on his neck, and they have proclaimed concerning him that he is the third ruler in the kingdom.
30 A wannan dare aka kashe Belshazar, sarkin Babiloniyawa,
In that night Belshazzar king of the Chaldeans is slain,
31 Dariyus mutumin Medes kuwa ya karɓi mulkin, yana da shekara sittin da biyu.
and Darius the Mede has received the kingdom when a son of sixty-two years.