< Daniyel 5 >
1 Sarki Belshazar ya yi babban biki domin dubban hakimansa ya kuma sha ruwan inabi tare da su.
Belshazzar manghai loh a boei thawngat hamla boeilen buhkoknah a saii tih thawngkhat mikhmuh ah misurtui a ok.
2 Yayinda Belshazar yake shan ruwan inabi, sai ya umarta a kawo zinariya da azurfan da Nebukadnezzar mahaifinsa ya kwaso daga haikali a Urushalima, saboda sarki da hakimansa, da matansa da ƙwarƙwaransa su sha da su.
Belshazzar loh, “Misurtui yukung ah a napa Nebukhadnezzar loh Jerusalem bawkim lamkah a loh sui neh cak hnopai te hang khuen lamtah te nen manghai neh a boei rhoek, a yuu rhoek neh a yula rhoek long khaw o saeh,” a ti.
3 Sai suka kawo kayan zinariyan nan da aka kwaso daga haikalin Allah a Urushalima, sarki kuwa da hakimansa, da matansa, da ƙwarƙwaransa suka yi ta sha da su.
Te dongah Jerusalem, Pathen im kah bawkim lamloh a loh sui hnopai te a khuen uh tih te nen Te manghai neh a boei rhoek long khaw, a yuu rhoek neh a yula rhoek long khaw a ok uh.
4 Yayinda suke shan ruwan inabin, sai suka yabi allolin zinariya da azurfa, da na tagulla, da na ƙarfe, da na itace da kuma na dutse.
Misurtui a ok uh vaengah sui pathen neh cak, rhohum, thi, thing, lungto te a koeh uh.
5 Nan da nan sai ga yatsotsin hannun mutum sun bayyana, suna yin rubutu a kan shafen bangon, kusa da wurin da ake ajiye fitilar fadar sarki. Sarki kuwa yana ganin hannun yayinda yake rubutu.
Amah tekah khonoek vaengah hlang kut dongkah kutdawn rhoek a caeh pah. Te phoeiah manghai hmaitung hmatoeng, manghai bawkim thoh dongkah taptlang dongah ca a daek pah. A daek vaengah ah khaw kut dongkah kutbom bueng ni manghai loh a hmuh.
6 Sai fuskarsa ta ruɗe, ya kuma ji tsoro ƙwarai har gwiwoyinsa suka yi ta bugun juna, ƙafafunsa kuma suka rasa ƙarfi.
Te dongah manghai Te a aa yat tih a poeknah loh amah a cahawh coeng. A hlit kah rhuhcong khaw phit tih a khuklu Te heben hebang la a khuek.
7 Sai sarki ya kira masu dabo, masanan taurari da masu duba, a kawo su, ya kuma ce wa masu hikima na Babilon, “Duk wanda ya karanta wannan rubutu ya kuma faɗa mini abin da yake nufi, za a sa masa rigar shunayya, a kuma sa masa sarƙar zinariya a wuyansa, zai zama na uku a cikin masu mulkin ƙasar.”
Manghai loh rhaitonghma rhoek khaw, Khalden rhoek khaw, aisi aka suep rhoekTe khue hamla thadueng neh pang. Te phoeiah manghai Te cal tih Babylon hlang cueih rhoek te, “Cadaek he a tae tih a thuingaihnah kai hamla aka thui hlang boeih te tah daidi hni a bai vetih a rhawn ah sui a oi vetih ram a pathum nah dongah boei ni,” a ti nah.
8 Sa’an nan sai dukan masu hikima suka zo ciki, amma ba su iya karanta rubutun ba ko su faɗa wa sarki abin da yake nufi.
Manghai kah hlang cueih boeih Te cet tah cet uh dae cadaek Te tae tih manghai taengah a thuingaihnah, thuicaih ham noeng uh pawh.
9 Saboda haka Sarki Belshazar ya firgita ƙwarai kuma fuskarsa ta ƙara ruɗewa. Hakimansa kuma suka rikice.
Te dongah manghai Belshazzar muep let tih a aa yat tih amah neh a boei rhoek khaw a lukil uh.
10 Sai sarauniya, da jin muryoyi na sarki da na hakimansa, ta shiga babban ɗakin liyafar. Ta ce, “Ya sarki, ranka yă daɗe! Kada ka firgita! Kada fuskarka ta ruɗe!
Manghai neh a boei rhoek kah ol kong ah manghainu khaw buhkoknah im la cet. Manghainu long khaw a voek tih, “Manghai tah kumhal duela hing saeh, na poeknah loh nang n'let sak boel saeh lamtah na aa yat boel saeh.
11 Akwai wani mutum a masarautarka wanda yake da ruhun alloli masu tsarki a cikinsa. A zamanin mahaifinka an gane cewa yana da basira da hazaka da hikima kamar na alloli. Sarki Nebukadnezzar mahaifinka, mahaifinka sarki, na ce, ya naɗa shugaban masu dabo, da masu sihiri, masanan taurari da kuma masu duba.
Na ram ah he a khuiah Pathen kah mueihla cim aka khueh hlang om ta. Na pa tue vaengah khaw vangnah, lungmingnah neh cueihnah he a khuiah Pathen kah cueihnah bangla tueng ta. Na pa manghai Nebukhadnezzar loh anih Te na pa manghai kah hmayuep, rhaitonghma, Khalden neh aisi aka suep kah boei la a khueh ta.
12 Wannan mutum Daniyel, wanda sarki ya kira Belteshazar, an gane yana da ruhu nagari, da ilimi, da ganewa don yin fassarar mafarkai, da bayyana ma’anar kacici-kacici, da warware al’amura masu wuya. Ka kira Daniyel shi kuwa zai faɗa maka abin da rubutun nan yake nufi.”
Te kong dongah tah a mueihla lang tih mingnah, lungmingnah neh mang a thuicaih. Olkael aka phoe tih rhuhcong aka hlam khaw amah la Daniel dongah tueng coeng. Anih Te manghai loh a ming Belteshazzar la a khueh tih Daniel la aka coeng he khue lamtah a thuingaihnah a thui bitni,” a ti nah.
13 Saboda haka aka kawo Daniyel a gaban sarki, sai sarki ya ce masa, “Kai ne Daniyel ɗin nan, ɗaya daga cikin kamammu waɗanda mahaifina sarki ya kawo daga Yahuda?
Te dongah Daniel Te manghai taengla a khuen tih manghai loh a voek. Te vaengah Daniel te, “Judah hlangsol ca lamkah Daniel he nang namah dae a? A pa manghai loh Judah lamkah a khuen te.
14 Na sami labari cewa kana da ruhun alloli a cikinka da kuma basira, da hazaka da kuma fitacciyar hikima.
Nang kawng he na khuiah Pathen mueihla om tih vangnah, lungmingnah, cueihnah loh na khuiah bahoeng tueng coeng tila ka yaak coeng.
15 An kawo masu hikima da masu dabo a gabana domin su karanta wannan rubutu su kuma faɗa mini abin da yake nufi, amma ba su iya ba.
Ka taengah cadaek he tae uh saeh lamtah a thuingaihnah Te kai hamla thuicaih saeh tila hlang cueih la rhaitonghma khaw hang khuen uh coeng dae ol kah thuingaihnah Te thui hamla a noeng uh moenih.
16 Na sami labari cewa kana iya ba da fassara da kuma warware matsaloli masu wuya. In har ka iya karanta wannan rubutun ka kuma faɗa mini abin da yake nufi, za a sa maka riga shunayya, a kuma sa sarƙar zinariya a wuyanka. Za ka zama na uku a cikin masu mulkin ƙasar.”
Nang namah tah thuingaihnah thuicaih ham neh rhuhcong pataeng hlam ham na noeng rhoe na noeng tila ka yaak coeng. Cadaek Te tae ham neh a thuingaihnah Te kai taengah thuicaih ham na noeng la na noeng atah daidi hni na bai vetih a oi pataeng sui oi ni na rhawn ah na oi eh. Te phoeiah ram khuiah a pathum nah la na boei ni,” a ti nah.
17 Sai Daniyel ya amsa wa sarki ya ce, “Za ka iya ajiye kyautar wa kanka ko kuma ka ba wa wani. Duk da haka, zan karanta wa sarki rubutun, in kuma faɗa abin da yake nufi.
Te dongah Daniel loh manghai te a doo tih, “Na kutdoe he namah ham om saeh lamtah na thapang te a tloe taengah pae mai. Tedae cadaek Te manghai hamla kan tae vetih a thuingaihnah kan thuicaih bitni.
18 “Ya sarki, Allah Mafi Ɗaukaka ya ba mahaifinka Nebukadnezzar sarauta, da girma, da ɗaukaka, da martaba.
Manghai nang, namah he a sangkoek kah sangkoek Pathen loh ram neh lennah khaw, thangpomnah neh hinyahnah khaw na pa Nebukhadnezzar taengah a paek.
19 Saboda irin matsayin da ya ba shi, dukan mutane da al’ummai da kuma dukan harsuna suka ji tsoronsa suka yi rawar jiki a gabansa. Bisa ga ganin damarsa yakan kashe wani, ya bar wani da rai, haka kuma yakan ɗaukaka wani, ya ƙasƙantar da wani.
Anih te lennah a paek dongah namtu pilnam cungkuem neh olcom olcae aka om rhoek loh thuen la thuen uh tih a taengah birhih uh. A ngaih a om te om bangla a ngawn tih a ngaih a om te a om bangla a hing sak. A ngaih a om te a om bangla a pacuet tih a ngaih a om te a om bangla a kunyun sak.
20 Amma da lokacin da zuciyarsa ta cika da girman kai ta kuma taurare, sai aka kore shi daga gadon sarautarsa, aka raba shi kuma da darajarsa.
Tedae a thinko te a pacuet tih altha hamla a mueihla a phuel dongah a ram kah ngolkhoel lamloh rhum tih a thangpomnah Te anih lamloh a khoe pauh.
21 Aka kore shi daga cikin mutane aka kuma ba shi tunani irin na dabba; ya yi zama tare da jakunan jeji, ya kuma ci ciyawa kamar shanu; jikinsa kuma ya jiƙe da raɓa, har zuwa lokacin da ya gane, ashe, Allah Maɗaukaki ne mai iko duka a kan dukan mulkoki a duniya, yake kuma ba da mulki ga duk wanda ya ga dama.
Te phoeiah hlang ca rhoek taeng lamloh a vai tih a thinko Te rhamsa la a khueh pah. A khosaknah khaw marhang lueng neh om tih vaito bangla rham a cah uh. Hlang kah ram soah a sangkoek kah a sangkoek Pathen loh a hung tih a ngaih taengah te te a pai sak tila a ming hil a pum Te vaan kah buem neh a saep sak.
22 “Amma kai ɗansa, Ya Belshazar, ba ka ƙasƙantar da kanka ba, ko da yake ka san wannan duka.
He kong he boeih na ming lalah a capa Belshazzar nang khaw na thinko na kunyun sak moenih.
23 A maimakon, sai ka nuna wa Ubangiji na sama girman kai. Ka sa aka kawo maka su kwaf na zinariya daga haikalinsa, da kai da hakimanka, da matanka da ƙwarƙwaranka kuka sha ruwan inabi da su. Kuka yabi allolin zinariya da na azurfa, da na tagulla, da na baƙin ƙarfe, da na itace, da na dutse waɗanda ba sa ji, ba sa gani, ba sa da gane kome. Amma ba ka girmama Allah ba, wanda ranka da dukan harkokinka suna a hannunsa.
Vaan kah Boeipa taengah lat a pacuet uh tih a im kah hnopai te namah taengla hang khuen uh. Namah neh na boei rhoek long khaw, na boei rhoek neh na yuu rhoek long khaw, na yula rhoek long khaw te nen Te misurtui a ok uh. Te phoeiah cak, sui, rhohum, thi, thing neh lungto pathen, aka hmu thai pawh, aka ya thai pawh, aka ming thai pawt te na koeh uh. Pathen amah kut ah na maal om tih na longpuei boeih he amah taengah om dae na hinyah moenih.
24 Saboda haka ya aiko da hannun da ya yi rubutun nan.
Te dongah ni amah taeng lamloh kut dongkah kutbom te a tueih pah tih cadaek he a daek pah.
25 “Wannan shi ne rubutun da aka yi, Mene, mene, tekel, farsin
Te cadaek te, “Mene, Mene, Tekel neh Uparsin,” la a daek.
26 “Abin da kalmomin nan suke nufi shi ne, “Mene, Allah ya ƙayyade yawan kwanakin mulkinka ya kuma kawo su ga ƙarshe.
Mene ollung kah a thuingaihnah he tah Pathen loh na ram he a khueh dae a khah coeng.
27 “Tekel, An kuma auna ka a ma’auni aka tarar ka kāsa.
Tekel tah coi dongah n'khiing dae a vawt m'hmuh.
28 “Feres, An raba mulkinka aka ba wa Medes da Farisa.”
Peres, na ram rhek tih Media neh Persia taengah a paek,” a ti nah.
29 Sai Belshazar ya umarta, aka sa wa Daniyel riga mai shunayya, aka sa sarƙar zinariya a wuyansa, aka kuma yi shela, cewa yanzu shi ne na uku a cikin masu mulkin ƙasar.
Te dongah Belshazzar loh a thui bangla Daniel te daidi a bai sakuh. A oi khaw sui oi Te a rhawn ah a oi sak. Anih te a ram ah a pathum nah aka hung la om ham a hoe uh.
30 A wannan dare aka kashe Belshazar, sarkin Babiloniyawa,
Amah te khoyin ah Belshazzar manghai Te Khalden loh a ngawn.
31 Dariyus mutumin Medes kuwa ya karɓi mulkin, yana da shekara sittin da biyu.
Te dongah Median kah Media Darius he kum sawmrhuk kum nit a lo ca vaengah ram a dang.