< Daniyel 4 >

1 Daga sarki Nebukadnezzar. Zuwa ga mutane da al’ummai da kuma kowane yare, da suke zama a duniya. Salama mai yawa ta tabbata a gare ku!
Kral Nebukadnessar dünyadaki bütün halklara, uluslara ve her dilden insanlara şu bildiriyi gönderdi: “Esenliğiniz bol olsun!
2 Ina murna in shaida muku game da alamu da al’ajabai waɗanda Allah Mafi Ɗaukaka ya yi ta wurina.
Yüce Tanrı'nın benim için gerçekleştirdiği belirtileri ve şaşılası işleri size bildirmeyi uygun gördüm.
3 Alamunsa da girma suke,
“Belirtileri ne büyük! Şaşılası işleri ne yüce! Krallığı ebedi krallıktır, Egemenliği kuşaklar boyu sürecek.
4 Ni, Nebukadnezzar, ina zaune a gidana cikin fadata, ina jin daɗi ina bunkasa.
“Ben, Nebukadnessar, evimde huzur, sarayımda gönenç içindeydim.
5 Na yi mafarkin da ya ba ni tsoro. A sa’ad da nake kwance a gadona, siffofi da wahayoyi da suka bi ta cikin tunanina sun firgita ni.
Beni korkutan bir düş gördüm. Yatağımda yatarken düşüncelerimle görümlerim beni ürküttü.
6 Don haka na ba da umarni a tattaro dukan masu hikima na Babilon su bayyana a gabana domin su fassara mini mafarkin.
Düşün ne anlama geldiğini açıklamaları için Babil'in bütün bilgelerinin yanıma getirilmesini buyurdum.
7 Sa’ad da masu sihiri, da masu dabo, da masanan taurari da masu duba suka zo, na faɗa musu mafarkin, amma ba su iya fassarta mini mafarkin ba.
Sihirbazlar, yıldızbilimciler, falcılar yanıma gelince, gördüğüm düşü onlara anlattımsa da ne anlama geldiğini açıklayamadılar.
8 A ƙarshe, sai Daniyel ya zo gabana na kuma faɗa masa mafarkin. (Ana ce da shi Belteshazar, wanda aka ba shi sunan allahna kuma ruhun alloli masu tsarki suna a bisansa.)
Sonunda ilahımın adından gelen Belteşassar adıyla çağrılan ve kendisinde kutsal ilahların ruhu bulunan Daniel yanıma geldi. Gördüğüm düşü ona anlattım.
9 Na ce, “Belteshazar, shugaban masu sihiri, na san ruhun alloli suna a kanka, babu wani asirin da zai fi ƙarfin ganewarka. Ga dai mafarkin da na yi, sai ka fassara mini.
“Ona şöyle dedim: Ey sihirbazların başkanı Belteşassar, sende kutsal ilahların ruhu olduğunu, her gizi açıklayabileceğini biliyorum. İşte gördüğüm düş: Ne anlama geldiğini bana açıkla.
10 Waɗannan su ne wahayin da na gani a lokacin da nake kwance a gadona, na duba, a gabana kuwa ga wani itace a kafe a tsakiyar duniya, yana da tsawo ƙwarai.
Yatarken gördüğüm görümler şunlar: Dünyanın ortasında çok yüksek bir ağaç gördüm.
11 Itacen ya yi girma ya kuma yi ƙarfi, har tsayinsa ya taɓa sarari sama; ana iya ganinsa a ko’ina a duniya.
Ağaç büyüdü, güçlendi, boyu göklere erişti. Dünyanın dört bucağından görülüyordu.
12 Ganyayensa suna da kyau, yana da’ya’ya jingim, abinci kuma domin kowa da kowa. A ƙarƙashinsa namun jeji suke samun wurin hutawa, kuma tsuntsayen sama suna zaune a bisa rassansa; daga cikinsa kowace halitta take cin abinci.
Yaprakları güzeldi, herkese yetecek kadar bol meyvesi vardı. Yabanıl hayvanlar gölgesinde barınıyor, gökte uçan kuşlar dallarına tünüyordu. Her canlı ondan besleniyordu.
13 “A cikin wahayin da gani sa’ad da nake kwance a kan gadona, Na duba, a gabana kuwa ga wani ɗan saƙo, mai tsarki, yana saukowa daga sama.
“Yatağımda yatarken gördüğüm görümlerde gökten inen bir gözcü, kutsal bir varlık gördüm.
14 Sai ya yi kira da babbar murya ya ce, ‘A sare itacen a kuma yayyanka rassansa; a karkaɗe ganyensa a kuma warwatsar da’ya’yansa. Bari dabbobi su tashi daga ƙarƙashinsa da kuma tsuntsayen da suke a rassansa.
Yüksek sesle, ‘Ağacı ve dallarını kesin, yapraklarını yolun, meyvesini atın’ diye bağırdı, ‘Altında barınan hayvanlarla dallarına tüneyen kuşlar kaçsın.
15 Amma a bar kututturen da kuma saiwoyinsa, a daure shi da ƙarfe da kuma tagulla, a bar shi a cikin ƙasa, a cikin ciyayin filaye. “‘Bari yă jiƙu da raɓar, bari yă zauna cikin dabbobi tare da tsire-tsiren duniya.
Ama köklerin bulunduğu kütüğü demirle, tunçla çevreleyip yerde, otların içinde bırakın. “‘Göğün çiyiyle ıslansın, hayvanlarla birlikte yerdeki otlardan pay alsın.
16 Bari a canja tunaninsa irin na mutane a ba shi tunani irin na dabbobi, har sau bakwai su wuce a kansa.
Ondaki insan yüreği değiştirilsin, yerine hayvan yüreği verilsin. Üzerinden yedi vakit geçsin.
17 “‘An sanar da wannan matsayi ne ta bakin’yan saƙo, masu tsarki ne kuwa suka sanar da hukuncin, domin masu rai su sani Mafi Ɗaukaka ne mai iko duka a bisa kowane mulkin mutane, yakan kuma ba wa duk wanda ya ga dama, yakan sanya talaka yă zama sarki.’
Bu yargıyı gözcüler, kararı kutsallar verdi. Öyle ki, her canlı Yüce Olan'ın insan krallıkları üzerinde egemenlik sürdüğünü ve onları dilediği kişiye, en hor görülen birine bile verebileceğini bilsin.’
18 “Wannan shi ne mafarkin da ni, Nebukadnezzar, na yi. Yanzu Belteshazar, sai ka faɗa mini abin da yake nufi, domin babu wani a cikin masu hikima a mulkina da ya iya fassara mini shi. Amma za ka iya, domin ruhun alloli masu tsarki yana a bisanka.”
“İşte ben Kral Nebukadnessar'ın gördüğü düş! Şimdi, ey Belteşassar, bunun ne anlama geldiğini söyle. Çünkü krallığımdaki bilgelerin hiçbiri bu düşün ne anlama geldiğini bana açıklayamadı. Ama sen açıklayabilirsin, çünkü kutsal ilahların ruhu var sende.”
19 Sai Daniyel (wanda ake kira Belteshazar) ya tsaya zugum na ɗan lokaci, tunaninsa ya ba shi tsoro. Saboda haka sarki ya ce, “Belteshazar, kada ka bar mafarkin ko ma’anarsa ta tayar maka da hankali.” Belteshazar ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, in dai har mafarkin zai tsaya a kan abokan gābanka da ma’anarsa kuma ta faɗa kan maƙiyan!
O zaman öbür adı Belteşassar olan Daniel bir süre şaşkın şaşkın durdu, düşünceleri onu ürküttü. Bunun üzerine kral, “Ey Belteşassar, bu düş de yorumu da seni ürkütmesin” dedi. Belteşassar, “Ey efendim, keşke bu düş senden nefret edenlerin, yorumu da düşmanlarının başına gelseydi!” diye karşılık verdi,
20 Itacen da ka gani; wanda ya yi girma da ƙarfe, da tsayinsa ya taɓa sararin sama, wanda ana ganinsa ko’ina a duniya,
“Büyüyen, güçlenen, boyu göklere erişen, dünyadaki herkesçe görülebilen bir ağaç gördün.
21 wanda ganyayensa masu kyau ne yana da’ya’yan itace da yawa, wanda yake ba da abinci ga duka, yana ba da wurin hutu ga namun jeji, kuma rassansa suna ɗauke da sheƙar tsuntsayen sama.
Yaprakları güzeldi, meyvesi herkese yetecek kadar boldu. Yabanıl hayvanlar altında barınır, gökte uçan kuşlar dallarına tünerdi.
22 Ya sarki kai ne itacen nan! Ka yi girma da ƙarfi; girmanka kuma ta kai har sama, mulkinka kuma ya kai ko’ina a duniya.
Ey kral, o ağaç sensin! Sen büyüdün, güçlendin. Büyüklüğün giderek göklere erişti, egemenliğin dünyanın dört bucağına yayıldı.
23 “Ya sarki ka ga ɗan saƙon mai tsarkin nan, yana saukowa daga sama yana cewa, ‘A sare itacen a hallaka shi, amma a bar kututturensa daure da ƙarfe da tagulla, a bar shi can a ɗanyar ciyawar filaye, ya jiƙe da raɓa, ya zauna tare da namun jeji har shekara bakwai.’
“Sen, ey kral, bir gözcünün, kutsal bir varlığın gökten indiğini gördün. ‘Ağacı kesip yok edin, ama köklerin bulunduğu kütüğü demirle, tunçla çevreleyip yerde, otların içinde bırakın. Göğün çiyiyle ıslansın; üzerinden yedi vakit geçinceye dek yabanıl hayvanlarla birlikte pay alsın’ diyordu.
24 “Ga fassarar, ya sarki, wannan ita ce doka wadda Mafi Ɗaukaka ya bayar a kan ranka yă daɗe, sarkina.
“Ey efendim kral, düşün anlamı ve Yüce Olan'ın senin başına getireceği yargı şudur:
25 Za a kore ka daga cikin mutane, za ka kuma zauna cikin namun jeji; za ka ci ciyawa kamar shanu, za ka jiƙe da raɓa har shekara bakwai cif sa’an nan za ka sani cewa Mafi Ɗaukaka ne mai iko duka a kan dukan mulkoki a duniya, yake kuma ba da mulki ga duk wanda ya ga dama.
İnsanlar arasından kovulacak, yabanıl hayvanlarla yaşayacaksın; öküz gibi otla beslenecek, göğün çiyiyle ıslanacaksın. Yüce Olan'ın insan krallıkları üzerinde egemenlik sürdüğünü ve krallığı dilediği kişiye verdiğini anlayıncaya dek yedi vakit geçecek.
26 Umarni na barin kututturen itacen da saiwoyinsa yana nufin cewa za a maido maka da mulkinka a lokacin da ka gane cewa Mai sama ne yake mulki.
Köklerin bulunduğu kütüğün bırakılması için buyruk verildi. Bunun anlamı şu: Sen göklerin egemenlik sürdüğünü anlayınca krallığın sana geri verilecek.
27 Saboda haka, ya sarki, ina roƙonka ka karɓi shawarar da zan ba ka; ka furta zunubanka ta wurin yin abin da yake daidai. Ka bar muguntarka, ka aikata alheri ga waɗanda ake wulaƙantawa, wataƙila za a ƙara tsawon kwanakinka da salama.”
Bu yüzden, ey kral, öğüdümü benimse: Doğru olanı yaparak günahından, düşkünlere iyilik ederek suçlarından vazgeç. Olur ya, gönencin uzun sürer.”
28 Duk wannan kuwa ya faru da sarki Nebukadnezzar.
Bunların hepsi Kral Nebukadnessar'ın başına geldi.
29 Bayan wata goma sha biyu, a sa’ad da sarki yake takawa a bisan saman ɗakin fadar Babilon,
On iki ay sonra kral Babil Sarayı'nın damında geziniyordu.
30 sai ya ce, “Ba wannan ita ce Babilon babba da na gina domin wurin zaman sarautar Babilon, da ikona kuma domin ɗaukakar darajata ba?”
Kral, “İşte onurum ve yüceliğim için üstün gücümle krallığımın başkenti olarak kurduğum büyük Babil!” dedi.
31 Tun kalmomin suna cikin bakinsa sai ya ji murya daga sama tana cewa, “Wannan shi ne abin da aka zartar a kanka, Sarki Nebukadnezzar. An karɓe ikon mulkinka.
Daha sözünü bitirmeden gökten bir ses duyuldu: “Ey Kral Nebukadnessar, krallık senden alındı.
32 Za a kore ka daga cikin mutane za ka kuma yi rayuwa tare da namun jeji. Za ka ci ciyawa kamar sa har shekara bakwai cif, sa’an nan za ka gane Mafi Ɗaukaka ne mai iko duka a kan dukan mulkoki a duniya, yake kuma ba da mulki ga duk wanda ya ga dama.”
İnsanlar arasından kovulacak, yabanıl hayvanlarla yaşayacaksın. Öküz gibi otla besleneceksin. Yüce Olan'ın insan krallıkları üzerinde egemenlik sürdüğünü ve krallığı dilediği kişiye verdiğini anlayıncaya dek yedi vakit geçecek.”
33 Nan da nan abin da aka faɗa a kan Nebukadnezzar tabbatarsa ya cika. Aka kore shi daga cikin mutane ya kuma shiga cin ciyawa kamar shanu. Jikinsa ya jiƙe da raɓa, har gashinsa ya yi tsawo kamar fikafikan gaggafa, kumbarsa kuma suka yi tsawo kamar na tsuntsu.
Nebukadnessar'a ilişkin bu söz hemen yerine geldi. İnsanlar arasından kovuldu. Öküz gibi otla beslendi. Bedeni göğün çiyiyle ıslandı. Saçı kartal tüyü, tırnakları kuş pençesi gibi uzadı.
34 A ƙarshen waɗannan kwanaki, ni, Nebukadnezzar, na ɗaga idanuna sama, sai hankalina ya komo mini. Na kuwa yabi Maɗaukaki, na girmama shi, na ɗaukaka shi wanda yake rayayye har abada.
Belirlenen sürenin sonunda ben Nebukadnessar gözlerimi göğe kaldırdım ve kendime geldim. Yüce Olan'ı övdüm. Sonsuza dek Diri Olan'ı onurlandırıp yücelttim. O'nun egemenliği ebedi egemenliktir, Krallığı kuşaklar boyu sürecek.
35 Dukan mutanen duniya
Dünyada yaşayanlar bir hiç sayılır. O gökteki güçlere de dünyada yaşayanlara da Dilediğini yapar. O'nun elini durduracak, O'na, “Ne yapıyorsun?” diyecek kimse yoktur.
36 A lokacin nan hankalina ya komo mini, sai aka mayar mini da masarautata mai daraja, da martabata, da girmana.’Yan majalisata da fadawana suka nemo ni. Aka maido ni kan gadon sarautata da daraja fiye da ta dā.
O anda aklım başıma geldi. Krallığımın yüceliği için onurum ve görkemim bana geri verildi. Danışmanlarımla soylu adamlarım beni aradılar. Krallığıma kavuştum, bana daha büyük yücelik verildi.
37 Yanzu ni, Nebukadnezzar, ina yabon Sarkin sama, ina waƙa ina kuma darjanta shi, saboda dukan abin da ya yi mini, mai kyau ne kuma dukan hanyoyinsa gaskiya ne. Kuma duk masu tafiya da girman kai zai ƙasƙantar da su.
Ben Nebukadnessar Göklerin Kralı'na şükrederim. O'nu över, yüceltirim. Çünkü bütün yaptıkları gerçek, yolları doğrudur; kendini beğenmişleri alçaltmaya gücü yeter.

< Daniyel 4 >