< Daniyel 4 >

1 Daga sarki Nebukadnezzar. Zuwa ga mutane da al’ummai da kuma kowane yare, da suke zama a duniya. Salama mai yawa ta tabbata a gare ku!
Kralj Nebukadnezar vsem ljudstvom, narodom in jezikom, ki prebivajo po vsej zemlji: »Mir naj se vam pomnoži.
2 Ina murna in shaida muku game da alamu da al’ajabai waɗanda Allah Mafi Ɗaukaka ya yi ta wurina.
Zdelo se mi je dobro pokazati [preroška] znamenja in čudeže, ki jih je vzvišeni Bog izvršil napram meni.
3 Alamunsa da girma suke,
Kako velika so njegova [preroška] znamenja! In kako mogočni so njegovi čudeži! Njegovo kraljestvo je večno kraljestvo in njegovo gospostvo je od roda do roda.
4 Ni, Nebukadnezzar, ina zaune a gidana cikin fadata, ina jin daɗi ina bunkasa.
Jaz, Nebukadnezar, sem bil pri počitku v svoji hiši in uspešen v svoji palači.
5 Na yi mafarkin da ya ba ni tsoro. A sa’ad da nake kwance a gadona, siffofi da wahayoyi da suka bi ta cikin tunanina sun firgita ni.
Videl sem sanje, ki so me prestrašile in misli na moji postelji in videnja moje glave so me vznemirila.
6 Don haka na ba da umarni a tattaro dukan masu hikima na Babilon su bayyana a gabana domin su fassara mini mafarkin.
Zatorej sem izdal odlok, da privedejo predme vse modre može Babilona, da bi mi lahko dali spoznati razlago sanj.
7 Sa’ad da masu sihiri, da masu dabo, da masanan taurari da masu duba suka zo, na faɗa musu mafarkin, amma ba su iya fassarta mini mafarkin ba.
Potem so vstopili čarovniki, astrologi, Kaldejci in napovedovalci usode, in pred njimi sem jim povedal sanje, toda niso mi dali spoznati njihove razlage.
8 A ƙarshe, sai Daniyel ya zo gabana na kuma faɗa masa mafarkin. (Ana ce da shi Belteshazar, wanda aka ba shi sunan allahna kuma ruhun alloli masu tsarki suna a bisansa.)
Toda na koncu je prišel predme Daniel, katerega ime je bilo Beltšacár, glede na ime mojega boga in v katerem je duh svetih bogov. Pred njim sem povedal sanje, rekoč:
9 Na ce, “Belteshazar, shugaban masu sihiri, na san ruhun alloli suna a kanka, babu wani asirin da zai fi ƙarfin ganewarka. Ga dai mafarkin da na yi, sai ka fassara mini.
›Oh Beltšacár, gospodar čarovnikov, ker vem, da je v tebi duh svetih bogov in da te nobena skrivnost ne vznemirja, mi povej videnja mojih sanj, ki sem jih videl in njihovo razlago.‹
10 Waɗannan su ne wahayin da na gani a lokacin da nake kwance a gadona, na duba, a gabana kuwa ga wani itace a kafe a tsakiyar duniya, yana da tsawo ƙwarai.
Takšna so bila videnja moje glave na moji postelji. Videl sem in glej drevo [je bilo] sredi zemlje in njegova višina je bila velika.
11 Itacen ya yi girma ya kuma yi ƙarfi, har tsayinsa ya taɓa sarari sama; ana iya ganinsa a ko’ina a duniya.
Drevo je raslo in bilo močno in njegova višina je segala do neba in njegovo vidno polje do konca vse zemlje.
12 Ganyayensa suna da kyau, yana da’ya’ya jingim, abinci kuma domin kowa da kowa. A ƙarƙashinsa namun jeji suke samun wurin hutawa, kuma tsuntsayen sama suna zaune a bisa rassansa; daga cikinsa kowace halitta take cin abinci.
Njegovo listje je bilo lepo in njegovega sadu obilo in na njem je bilo hrane za vse. Živali polja so pod njim imele senco in perjad neba je prebivala v njegovih vejah in vse meso je bilo od njega nahranjeno.
13 “A cikin wahayin da gani sa’ad da nake kwance a kan gadona, Na duba, a gabana kuwa ga wani ɗan saƙo, mai tsarki, yana saukowa daga sama.
Videl sem v videnjih svoje glave na svoji postelji in glej, stražar in sveti je prišel dol z neba.
14 Sai ya yi kira da babbar murya ya ce, ‘A sare itacen a kuma yayyanka rassansa; a karkaɗe ganyensa a kuma warwatsar da’ya’yansa. Bari dabbobi su tashi daga ƙarƙashinsa da kuma tsuntsayen da suke a rassansa.
Glasno je zavpil in rekel takole: ›Posekajte drevo in odrežite njegove veje, otresite listje in raztresite njegov sad. Naj gredo živali proč izpod njega in perjad od njegovih mladik,
15 Amma a bar kututturen da kuma saiwoyinsa, a daure shi da ƙarfe da kuma tagulla, a bar shi a cikin ƙasa, a cikin ciyayin filaye. “‘Bari yă jiƙu da raɓar, bari yă zauna cikin dabbobi tare da tsire-tsiren duniya.
kljub temu pa pustite štor njegovih korenin v zemlji, celo v okovu iz železa in brona, v nežni travi polja in ta naj bo omočen z roso neba in njegov delež naj bo z živalmi na zemeljski travi.
16 Bari a canja tunaninsa irin na mutane a ba shi tunani irin na dabbobi, har sau bakwai su wuce a kansa.
Naj bo njegovo srce spremenjeno od človeškega in naj mu bo dano živalsko srce, in nad njim naj mine sedem dob.
17 “‘An sanar da wannan matsayi ne ta bakin’yan saƙo, masu tsarki ne kuwa suka sanar da hukuncin, domin masu rai su sani Mafi Ɗaukaka ne mai iko duka a bisa kowane mulkin mutane, yakan kuma ba wa duk wanda ya ga dama, yakan sanya talaka yă zama sarki.’
Ta stvar je po odloku stražarjev in zahteva po besedi svetih, z namenom, da bodo živi lahko spoznali, da Najvišji vlada v kraljestvu ljudi in ga daje komur hoče in postavi nadenj najnižjega izmed ljudi.
18 “Wannan shi ne mafarkin da ni, Nebukadnezzar, na yi. Yanzu Belteshazar, sai ka faɗa mini abin da yake nufi, domin babu wani a cikin masu hikima a mulkina da ya iya fassara mini shi. Amma za ka iya, domin ruhun alloli masu tsarki yana a bisanka.”
Te sanje sem jaz, kralj Nebukadnezar, videl. Torej ti, oh Beltšacár, razglasi njihovo razlago, ker vsi modri ljudje mojega kraljestva niso zmožni, da bi mi dali spoznati razlago, toda ti si zmožen, kajti duh svetih bogov je v tebi.‹«
19 Sai Daniyel (wanda ake kira Belteshazar) ya tsaya zugum na ɗan lokaci, tunaninsa ya ba shi tsoro. Saboda haka sarki ya ce, “Belteshazar, kada ka bar mafarkin ko ma’anarsa ta tayar maka da hankali.” Belteshazar ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, in dai har mafarkin zai tsaya a kan abokan gābanka da ma’anarsa kuma ta faɗa kan maƙiyan!
Potem je bil Daniel, katerega ime je bilo Beltšacár, za eno uro osupel in njegove misli so ga vznemirile. Kralj je spregovoril in rekel: »Beltšacár, ne pusti, da bi te sanje ali njihova razlaga vznemirile.« Beltšacár je odgovoril in rekel: »Moj gospod, sanje naj bodo njim, ki te sovražijo in njihova razlaga tvojim sovražnikom.
20 Itacen da ka gani; wanda ya yi girma da ƙarfe, da tsayinsa ya taɓa sararin sama, wanda ana ganinsa ko’ina a duniya,
Drevo, ki si ga videl, ki je raslo in je bilo močno, katerega višina je segla do neba in katerega vidno polje je po vsej zemlji,
21 wanda ganyayensa masu kyau ne yana da’ya’yan itace da yawa, wanda yake ba da abinci ga duka, yana ba da wurin hutu ga namun jeji, kuma rassansa suna ɗauke da sheƙar tsuntsayen sama.
katerega listje je bilo lepo in njegov sad obilen in je bilo na njem hrane za vse, pod katerim so prebivale živali polja in na čigar vejah je imela perjad neba svoje prebivališče.
22 Ya sarki kai ne itacen nan! Ka yi girma da ƙarfi; girmanka kuma ta kai har sama, mulkinka kuma ya kai ko’ina a duniya.
To si ti, oh kralj, ki si zrasel in postal močan, kajti tvoja veličina je zrasla in sega do neba in tvoje gospostvo do konca zemlje.
23 “Ya sarki ka ga ɗan saƙon mai tsarkin nan, yana saukowa daga sama yana cewa, ‘A sare itacen a hallaka shi, amma a bar kututturensa daure da ƙarfe da tagulla, a bar shi can a ɗanyar ciyawar filaye, ya jiƙe da raɓa, ya zauna tare da namun jeji har shekara bakwai.’
Medtem ko je kralj videl stražarja in svetega prihajati dol z neba in reči: ›Posekajte drevo in ga uničite, vendar od njega pustite v zemlji štor s koreninami, celo z okovom iz železa in brona, v nežni travi polja; in naj bo ta omočen z roso neba in njegov delež naj bo z živalmi polja, dokler nad njim ne mine sedem dob.‹
24 “Ga fassarar, ya sarki, wannan ita ce doka wadda Mafi Ɗaukaka ya bayar a kan ranka yă daɗe, sarkina.
To je razlaga, oh kralj in to je odlok Najvišjega, ki je prišel nad mojega gospoda kralja,
25 Za a kore ka daga cikin mutane, za ka kuma zauna cikin namun jeji; za ka ci ciyawa kamar shanu, za ka jiƙe da raɓa har shekara bakwai cif sa’an nan za ka sani cewa Mafi Ɗaukaka ne mai iko duka a kan dukan mulkoki a duniya, yake kuma ba da mulki ga duk wanda ya ga dama.
da te bodo pregnali od ljudi in tvoje prebivališče bo z živalmi polja in pripravili te bodo, da boš jedel travo kakor voli in močili te bodo z roso neba in sedem dob bo prešlo nad teboj, dokler ne spoznaš, da Najvišji vlada v kraljestvu ljudi in ga daje komurkoli on hoče.
26 Umarni na barin kututturen itacen da saiwoyinsa yana nufin cewa za a maido maka da mulkinka a lokacin da ka gane cewa Mai sama ne yake mulki.
Zapovedali so, da pustijo štor od drevesnih korenin; tvoje kraljestvo bo zagotovo pripadlo tebi, potem ko boš spoznal, da nebesa vladajo.
27 Saboda haka, ya sarki, ina roƙonka ka karɓi shawarar da zan ba ka; ka furta zunubanka ta wurin yin abin da yake daidai. Ka bar muguntarka, ka aikata alheri ga waɗanda ake wulaƙantawa, wataƙila za a ƙara tsawon kwanakinka da salama.”
Zatorej, oh kralj, naj ti bo moj nasvet sprejemljiv in svoje grehe zlomi s pravičnostjo in svoje krivičnosti z izkazovanjem usmiljenja revnim; če bi to lahko bilo podaljšanje tvoje umirjenosti.‹«
28 Duk wannan kuwa ya faru da sarki Nebukadnezzar.
Vse to je prišlo nad kralja Nebukadnezarja.
29 Bayan wata goma sha biyu, a sa’ad da sarki yake takawa a bisan saman ɗakin fadar Babilon,
Ob koncu dvanajstih mesecev je hodil v palači babilonskega kraljestva.
30 sai ya ce, “Ba wannan ita ce Babilon babba da na gina domin wurin zaman sarautar Babilon, da ikona kuma domin ɗaukakar darajata ba?”
Kralj je spregovoril in rekel: »Ali ni to veliki Babilon, ki sem ga jaz zgradil za hišo kraljestva po moči svoje oblasti in za čast svojega veličanstva?«
31 Tun kalmomin suna cikin bakinsa sai ya ji murya daga sama tana cewa, “Wannan shi ne abin da aka zartar a kanka, Sarki Nebukadnezzar. An karɓe ikon mulkinka.
Medtem ko je bila beseda v kraljevih ustih, je padel glas z neba, rekoč: »Oh kralj Nebukadnezar, tebi je govorjeno: ›Kraljestvo je odšlo od tebe.
32 Za a kore ka daga cikin mutane za ka kuma yi rayuwa tare da namun jeji. Za ka ci ciyawa kamar sa har shekara bakwai cif, sa’an nan za ka gane Mafi Ɗaukaka ne mai iko duka a kan dukan mulkoki a duniya, yake kuma ba da mulki ga duk wanda ya ga dama.”
Pregnali te bodo od ljudi in tvoje prebivališče bo z živalmi polja. Prisilili te bodo, da boš jedel travo kakor voli in sedem dob bo prešlo nad teboj, dokler ne spoznaš, da Najvišji vlada v kraljestvu ljudi in ga daje komurkoli on hoče.‹«
33 Nan da nan abin da aka faɗa a kan Nebukadnezzar tabbatarsa ya cika. Aka kore shi daga cikin mutane ya kuma shiga cin ciyawa kamar shanu. Jikinsa ya jiƙe da raɓa, har gashinsa ya yi tsawo kamar fikafikan gaggafa, kumbarsa kuma suka yi tsawo kamar na tsuntsu.
To isto uro je bila stvar nad Nebukadnezarjem izpolnjena. Pregnan je bil od ljudi, jedel travo kakor voli in njegovo telo je bilo omočeno z roso z neba, dokler njegovi lasje niso zrasli kakor orlovo perje in njegovi nohti kakor ptičji kremplji.
34 A ƙarshen waɗannan kwanaki, ni, Nebukadnezzar, na ɗaga idanuna sama, sai hankalina ya komo mini. Na kuwa yabi Maɗaukaki, na girmama shi, na ɗaukaka shi wanda yake rayayye har abada.
»In ob koncu dni sem jaz, Nebukadnezar, povzdignil svoje oči k nebu in moje razumevanje se je vrnilo k meni in blagoslovil sem Najvišjega in hvalil in častil njega, ki živi na veke, katerega gospostvo je večno gospostvo in njegovo kraljestvo je od roda do roda.
35 Dukan mutanen duniya
Vsi prebivalci zemlje so šteti kakor nič in on dela glede na svojo voljo v vojski nebes in med prebivalci zemlje, in nihče ne more zadržati njegove roke ali mu reči: ›Kaj počneš?‹
36 A lokacin nan hankalina ya komo mini, sai aka mayar mini da masarautata mai daraja, da martabata, da girmana.’Yan majalisata da fadawana suka nemo ni. Aka maido ni kan gadon sarautata da daraja fiye da ta dā.
Ob istem času se je moj razum vrnil k meni in zaradi slave mojega kraljestva sta se moja čast in moj sijaj vrnila k meni in moji svetovalci in moji velikaši so me poiskali, jaz pa sem bil utrjen v svojem kraljestvu in dodano mi je bilo odlično veličanstvo.
37 Yanzu ni, Nebukadnezzar, ina yabon Sarkin sama, ina waƙa ina kuma darjanta shi, saboda dukan abin da ya yi mini, mai kyau ne kuma dukan hanyoyinsa gaskiya ne. Kuma duk masu tafiya da girman kai zai ƙasƙantar da su.
Sedaj jaz, Nebukadnezar, hvalim, povzdigujem in častim Kralja nebes. Vsa njegova dela so resnica in njegove poti sodba, tiste pa, ki hodijo v ponosu, je zmožen ponižati.‹«

< Daniyel 4 >