< Daniyel 4 >

1 Daga sarki Nebukadnezzar. Zuwa ga mutane da al’ummai da kuma kowane yare, da suke zama a duniya. Salama mai yawa ta tabbata a gare ku!
Inkosi uNebhukhadineza, Ezizweni zonke lebantwini benhlanga zonke abahlala emhlabeni wonke: Sengathi inganda kini inhlalakahle!
2 Ina murna in shaida muku game da alamu da al’ajabai waɗanda Allah Mafi Ɗaukaka ya yi ta wurina.
Kuyintokozo kimi ukulitshela ngezibonakaliso ezimangalisayo lezinkinga uNkulunkulu oPhezukonke angenzele zona.
3 Alamunsa da girma suke,
Zinkulu kangakanani izibonakaliso zakhe,
4 Ni, Nebukadnezzar, ina zaune a gidana cikin fadata, ina jin daɗi ina bunkasa.
Mina, Nebhukhadineza, ngangisekhaya esigodlweni sami, nganelisiwe njalo ngikhomba ngophakathi.
5 Na yi mafarkin da ya ba ni tsoro. A sa’ad da nake kwance a gadona, siffofi da wahayoyi da suka bi ta cikin tunanina sun firgita ni.
Ngehlelwa liphupho elangitshayisa uvalo. Ngathi ngilele embhedeni wami kwafika engqondweni yami izifanekiso lezibonakaliso ezangithuthumelisayo.
6 Don haka na ba da umarni a tattaro dukan masu hikima na Babilon su bayyana a gabana domin su fassara mini mafarkin.
Ngasengilaya ukuthi zonke izihlakaniphi zaseBhabhiloni zilethwe phambi kwami ukuthi zingihlahlulele lelophupho.
7 Sa’ad da masu sihiri, da masu dabo, da masanan taurari da masu duba suka zo, na faɗa musu mafarkin, amma ba su iya fassarta mini mafarkin ba.
Kwathi sebefikile omasalamusi, lezangoma, lezingcazi zezinkanyezi lezanuse ngazitshela lelophupho kodwa zehluleka ukungichasisela lona.
8 A ƙarshe, sai Daniyel ya zo gabana na kuma faɗa masa mafarkin. (Ana ce da shi Belteshazar, wanda aka ba shi sunan allahna kuma ruhun alloli masu tsarki suna a bisansa.)
Ekucineni uDanyeli wafika kimi ngamtshela ngephupho lelo. (Uthiwa nguBhelitheshazari, ngokuphathelene lebizo likankulunkulu wami, njalo umoya wabonkulunkulu abangcwele uphakathi kwakhe.)
9 Na ce, “Belteshazar, shugaban masu sihiri, na san ruhun alloli suna a kanka, babu wani asirin da zai fi ƙarfin ganewarka. Ga dai mafarkin da na yi, sai ka fassara mini.
Ngathi kuye, Bhelitheshazari, nduna yabomasalamusi, ngiyazi ukuthi umoya wabonkulunkulu abangcwele uphakathi kwakho, njalo kakukho okuyinkinga kuwe. Nanti iphupho lami; ngihlahlulela lona.
10 Waɗannan su ne wahayin da na gani a lokacin da nake kwance a gadona, na duba, a gabana kuwa ga wani itace a kafe a tsakiyar duniya, yana da tsawo ƙwarai.
Yile imibono eyangivelelayo ngilele embhedeni wami: Ngakhangela, ngabona kumi phambi kwami isihlahla phakathi komango. Ubude baso babule.
11 Itacen ya yi girma ya kuma yi ƙarfi, har tsayinsa ya taɓa sarari sama; ana iya ganinsa a ko’ina a duniya.
Isihlahla sakhula saba sikhulu saqina, isiqongo saso sakhotha umkhathi; sasibonakala lasemikhawulweni yomhlaba.
12 Ganyayensa suna da kyau, yana da’ya’ya jingim, abinci kuma domin kowa da kowa. A ƙarƙashinsa namun jeji suke samun wurin hutawa, kuma tsuntsayen sama suna zaune a bisa rassansa; daga cikinsa kowace halitta take cin abinci.
Amahlamvu aso ayebukeka, izithelo zaso zinengi kuso kukhona ukudla kwakho konke. Ngaphansi kwaso izinyamazana zeganga zafumana isiphephelo lezinyoni zemoyeni zazihlala emagatsheni aso; zonke izidalwa zisongiwa kuso.
13 “A cikin wahayin da gani sa’ad da nake kwance a kan gadona, Na duba, a gabana kuwa ga wani ɗan saƙo, mai tsarki, yana saukowa daga sama.
Ezibonakalisweni ezeza ngilele embhedeni wami, ngakhangela, ngabona khonapho phambi kwami kulesithunywa, singongcwele, sisehla sisuka ezulwini.
14 Sai ya yi kira da babbar murya ya ce, ‘A sare itacen a kuma yayyanka rassansa; a karkaɗe ganyensa a kuma warwatsar da’ya’yansa. Bari dabbobi su tashi daga ƙarƙashinsa da kuma tsuntsayen da suke a rassansa.
Samemeza ngelizwi elikhulu sathi: Gamulelani phansi isihlahla licakaze amagatsha aso; liwaphundle amahlamvu aso lihlakaze izithelo zaso. Yekelani izinyamazana zibaleke ngaphansi kwaso kanye lezinyoni emagatsheni aso.
15 Amma a bar kututturen da kuma saiwoyinsa, a daure shi da ƙarfe da kuma tagulla, a bar shi a cikin ƙasa, a cikin ciyayin filaye. “‘Bari yă jiƙu da raɓar, bari yă zauna cikin dabbobi tare da tsire-tsiren duniya.
Kodwa akuthi isidindi saso kanye lempande zakhona kusale kugxumekile emhlabathini phakathi kotshani beganga, kubotshiwe ngensimbi langethusi. Kagxanxwe ngamazolo avela phezulu, njalo kahlale lezinyamazana phakathi kwezihlahla zeganga.
16 Bari a canja tunaninsa irin na mutane a ba shi tunani irin na dabbobi, har sau bakwai su wuce a kansa.
Ingqondo yakhe kayiguqulwe isuke ebuntwini, aphiwe ingqondo yenyamazana, kuze kudlule iminyaka eyisikhombisa.
17 “‘An sanar da wannan matsayi ne ta bakin’yan saƙo, masu tsarki ne kuwa suka sanar da hukuncin, domin masu rai su sani Mafi Ɗaukaka ne mai iko duka a bisa kowane mulkin mutane, yakan kuma ba wa duk wanda ya ga dama, yakan sanya talaka yă zama sarki.’
“‘Isinqumo lesi sibikwa yizithunywa, zona ezingcwele yizo ezimemezela lesi isigwebo, ukuze kuthi abaphilayo bazi ukuthi oPhezukonke unguThixo yemibuso yabantu njalo uyabanikela loba kukubani amfunayo futhi enze babuswe ngumuntukazana.’
18 “Wannan shi ne mafarkin da ni, Nebukadnezzar, na yi. Yanzu Belteshazar, sai ka faɗa mini abin da yake nufi, domin babu wani a cikin masu hikima a mulkina da ya iya fassara mini shi. Amma za ka iya, domin ruhun alloli masu tsarki yana a bisanka.”
Yilo iphupho engibe lalo mina inkosi uNebhukhadineza. Manje-ke Bhelitheshazari, ngitshela ukuthi litshoni, ngoba kasikho isihlakaniphi embusweni wami esingangihlahlulela lona. Kodwa wena ungakwenza, ngoba umoya wabonkulunkulu abangcwele uphakathi kwakho.”
19 Sai Daniyel (wanda ake kira Belteshazar) ya tsaya zugum na ɗan lokaci, tunaninsa ya ba shi tsoro. Saboda haka sarki ya ce, “Belteshazar, kada ka bar mafarkin ko ma’anarsa ta tayar maka da hankali.” Belteshazar ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, in dai har mafarkin zai tsaya a kan abokan gābanka da ma’anarsa kuma ta faɗa kan maƙiyan!
Yikho uDanyeli (njalo othiwa nguBhelitheshazari) wakhathazeka kakhulu okwesikhathi esithile, imicabango yakhe yamethusa. Yikho inkosi yasisithi, “Bhelitheshazari, ungethuswa liphupho lelo kumbe yincazelo yalo.” UBhelitheshazari waphendula wathi, Nkosi yami, sengathi ngabe iphupho lelo liqonde labo abayizitha zakho lengcazelo yalo ikhomba labo abakuzondayo!
20 Itacen da ka gani; wanda ya yi girma da ƙarfe, da tsayinsa ya taɓa sararin sama, wanda ana ganinsa ko’ina a duniya,
Isihlahla osibonileyo, esakhula saba sikhulu saqina, isiqongo saso sikhotha isibhakabhaka size sibonakale emhlabeni wonke,
21 wanda ganyayensa masu kyau ne yana da’ya’yan itace da yawa, wanda yake ba da abinci ga duka, yana ba da wurin hutu ga namun jeji, kuma rassansa suna ɗauke da sheƙar tsuntsayen sama.
silamahlamvu abukekayo lezithelo ezinengi, sisipha ukudla kukho konke, siphe isiphephelo izinyamazana zeganga, emagatsheni aso silezindawo zezidleke zezinyoni zemoyeni,
22 Ya sarki kai ne itacen nan! Ka yi girma da ƙarfi; girmanka kuma ta kai har sama, mulkinka kuma ya kai ko’ina a duniya.
wena, Oh nkosi, uyilesosihlahla! Usube mkhulu waba lamandla; ubukhulu bakho sebandile sebuze buthinta isibhakabhaka, lombuso wakho usufinyelela ezindaweni ezikude ezomhlaba.
23 “Ya sarki ka ga ɗan saƙon mai tsarkin nan, yana saukowa daga sama yana cewa, ‘A sare itacen a hallaka shi, amma a bar kututturensa daure da ƙarfe da tagulla, a bar shi can a ɗanyar ciyawar filaye, ya jiƙe da raɓa, ya zauna tare da namun jeji har shekara bakwai.’
“Wena, Oh nkosi, wabona isithunywa, sona esingcwele, sisehla sivela ezulwini sisithi, ‘Sigamuleleni phansi isihlahla lisicakaze, kodwa litshiye isidindi, sibotshiwe ngensimbi langethusi, siphakathi kotshani beganga, impande zaso zisale emhlabathini. Kagxanxwe ngamazolo aphezulu; kaphile njengezinyamazana zeganga kuze kudlule iminyaka eyisikhombisa.’
24 “Ga fassarar, ya sarki, wannan ita ce doka wadda Mafi Ɗaukaka ya bayar a kan ranka yă daɗe, sarkina.
Nansi ingcazelo, Oh nkosi, njalo lesi yisimiso soPhezukonke asimisele umhlekazi wami inkosi:
25 Za a kore ka daga cikin mutane, za ka kuma zauna cikin namun jeji; za ka ci ciyawa kamar shanu, za ka jiƙe da raɓa har shekara bakwai cif sa’an nan za ka sani cewa Mafi Ɗaukaka ne mai iko duka a kan dukan mulkoki a duniya, yake kuma ba da mulki ga duk wanda ya ga dama.
Uzaxotshwa ebantwini uyehlala lezinyamazana zeganga: uzakudla utshani njengezinkomo, ugxanxwe ngamazolo aphezulu. Kuzakudlula iminyaka eyisikhombisa uze uvume ukuthi oPhezukonke uyabusa phezu kwemibuso yabantu ayinika ingqe ngulowo amthandayo.
26 Umarni na barin kututturen itacen da saiwoyinsa yana nufin cewa za a maido maka da mulkinka a lokacin da ka gane cewa Mai sama ne yake mulki.
Umlayo wokutshiya isidindi kanye lezimpande zaso utsho ukuthi umbuso wakho uzabuyiselwa kuwe nxatshana usuvuma ukuthi iZulu liyabusa.
27 Saboda haka, ya sarki, ina roƙonka ka karɓi shawarar da zan ba ka; ka furta zunubanka ta wurin yin abin da yake daidai. Ka bar muguntarka, ka aikata alheri ga waɗanda ake wulaƙantawa, wataƙila za a ƙara tsawon kwanakinka da salama.”
Ngakho-ke, Oh nkosi, kuhle ukuthi wamukele ukucebisa kwami: Yekela izono zakho wenze okulungileyo, lobubi bakho ube lomusa kwabancindezelweyo. Lapho-ke mhlawumbe ukuphumelela kwakho kungaqhubeka.”
28 Duk wannan kuwa ya faru da sarki Nebukadnezzar.
Konke lokhu kwenzakala enkosini uNebhukhadineza.
29 Bayan wata goma sha biyu, a sa’ad da sarki yake takawa a bisan saman ɗakin fadar Babilon,
Sekudlule izinyanga ezilitshumi lambili, inkosi ihambahamba ephahleni lwesigodlo saseBhabhiloni,
30 sai ya ce, “Ba wannan ita ce Babilon babba da na gina domin wurin zaman sarautar Babilon, da ikona kuma domin ɗaukakar darajata ba?”
yathi, “Kakusilo yini iBhabhiloni leli engalakha laba ngumuzi wobukhosi bami na?”
31 Tun kalmomin suna cikin bakinsa sai ya ji murya daga sama tana cewa, “Wannan shi ne abin da aka zartar a kanka, Sarki Nebukadnezzar. An karɓe ikon mulkinka.
Kwathi amazwi la elokhu esesemlonyeni wakhe kwehla ilizwi livela ezulwini lathi, “Nanku osukunqunyelwe, nkosi Nebhukhadineza: Amandla akho obukhosi asesusiwe kuwe.
32 Za a kore ka daga cikin mutane za ka kuma yi rayuwa tare da namun jeji. Za ka ci ciyawa kamar sa har shekara bakwai cif, sa’an nan za ka gane Mafi Ɗaukaka ne mai iko duka a kan dukan mulkoki a duniya, yake kuma ba da mulki ga duk wanda ya ga dama.”
Uzaxotshwa ebantwini uyehlala lezinyamazana zeganga; uzakudla utshani njengezinkomo. Kuzadlula iminyaka eyisikhombisa uze uvume ukuthi oPhezukonke uyabusa phezu kwemibuso yabantu ayiphe ingqe ngubani ngokuthanda kwakhe.”
33 Nan da nan abin da aka faɗa a kan Nebukadnezzar tabbatarsa ya cika. Aka kore shi daga cikin mutane ya kuma shiga cin ciyawa kamar shanu. Jikinsa ya jiƙe da raɓa, har gashinsa ya yi tsawo kamar fikafikan gaggafa, kumbarsa kuma suka yi tsawo kamar na tsuntsu.
Masinyane nje okwakutshiwo ngoNebhukhadineza kwagcwaliseka. Waxotshwa ebantwini wadla utshani njengezinkomo. Umzimba wakhe wagxanxwa ngamazolo aphezulu, inwele zakhe zakhula njengezinsiba zengqungqulu, kwathi inzipho zakhe zaba njengenkumba zenyoni.
34 A ƙarshen waɗannan kwanaki, ni, Nebukadnezzar, na ɗaga idanuna sama, sai hankalina ya komo mini. Na kuwa yabi Maɗaukaki, na girmama shi, na ɗaukaka shi wanda yake rayayye har abada.
Ekupheleni kwalesosikhathi, mina, Nebhukhadineza, ngaphakamisela amehlo ami ezulwini, ingqondo yami yabuya. Ngasengimdumisa oPhezukonke; ngambabaza, ngambonga yena ohlezi kuze kube phakade.
35 Dukan mutanen duniya
Imihlobo yonke yabantu bomhlaba
36 A lokacin nan hankalina ya komo mini, sai aka mayar mini da masarautata mai daraja, da martabata, da girmana.’Yan majalisata da fadawana suka nemo ni. Aka maido ni kan gadon sarautata da daraja fiye da ta dā.
Ngasonalesosikhathi ingqondo yami yabuya, udumo lwami lenkazimulo yami kwabuyiswa kimi ukusekela ubukhosi bombuso wami. Abeluleki bami lezikhulu zami bangidinga bangibuyisela esihlalweni sami sobukhosi, ngase ngisiba mkhulu kulakuqala.
37 Yanzu ni, Nebukadnezzar, ina yabon Sarkin sama, ina waƙa ina kuma darjanta shi, saboda dukan abin da ya yi mini, mai kyau ne kuma dukan hanyoyinsa gaskiya ne. Kuma duk masu tafiya da girman kai zai ƙasƙantar da su.
Ngakho-ke mina, Nebhukhadineza, ngiyayidumisa njalo ngiyayibabaza, ngiyiphakamise iNkosi yezulu, ngoba konke ekwenzayo kuqondile futhi lezindlela zayo zonke zilungile. Njalo bonke abazigqajayo iyabathobisa.

< Daniyel 4 >