< Daniyel 4 >

1 Daga sarki Nebukadnezzar. Zuwa ga mutane da al’ummai da kuma kowane yare, da suke zama a duniya. Salama mai yawa ta tabbata a gare ku!
Nebuchadnezzar the king, unto all the peoples, the races and the tongues who are dwelling in all the earth, Let, your prosperity, abound!
2 Ina murna in shaida muku game da alamu da al’ajabai waɗanda Allah Mafi Ɗaukaka ya yi ta wurina.
The signs, and the wonders, which the most high God, hath wrought with me, it is pleasing before me to declare.
3 Alamunsa da girma suke,
His signs, how great! and, his wonders, how mighty! His kingdom, is an age-abiding kingdom, and, his dominion, lasteth from generation to generation.
4 Ni, Nebukadnezzar, ina zaune a gidana cikin fadata, ina jin daɗi ina bunkasa.
I, Nebuchadnezzar, was at peace in mine own house, and was prosperous in my palace.
5 Na yi mafarkin da ya ba ni tsoro. A sa’ad da nake kwance a gadona, siffofi da wahayoyi da suka bi ta cikin tunanina sun firgita ni.
A dream, I saw, and it made me afraid, —and, fancies upon my bed, and visions of my head, terrified me.
6 Don haka na ba da umarni a tattaro dukan masu hikima na Babilon su bayyana a gabana domin su fassara mini mafarkin.
Therefore made I a decree, to bring in before me, all the wise men of Babylon, —who, the interpretation of the dream, should make known to me.
7 Sa’ad da masu sihiri, da masu dabo, da masanan taurari da masu duba suka zo, na faɗa musu mafarkin, amma ba su iya fassarta mini mafarkin ba.
Then came in the sacred scribes, the magicians, the Chaldeans, and the astrologers, —and, the dream, told I before them, but, the interpretation, could they not make known to me.
8 A ƙarshe, sai Daniyel ya zo gabana na kuma faɗa masa mafarkin. (Ana ce da shi Belteshazar, wanda aka ba shi sunan allahna kuma ruhun alloli masu tsarki suna a bisansa.)
Howbeit, at last, came before me—Daniel, whose, name, was Belteshazzar, after the name of my god, and in whom is the spirit of the holy gods; and, the dream—before him, I told [saying]:
9 Na ce, “Belteshazar, shugaban masu sihiri, na san ruhun alloli suna a kanka, babu wani asirin da zai fi ƙarfin ganewarka. Ga dai mafarkin da na yi, sai ka fassara mini.
O Belteshazzar, chief of the sacred scribes, because I know that, the spirit of the holy gods, is in thee, —and no secret giveth thee trouble, [therefore], the visions of my dream which I have seen, and the interpretation thereof, do thou tell.
10 Waɗannan su ne wahayin da na gani a lokacin da nake kwance a gadona, na duba, a gabana kuwa ga wani itace a kafe a tsakiyar duniya, yana da tsawo ƙwarai.
The visions then of my head upon my bed [were these], —I was looking, when lo! a tree in the midst of the land, and, the height thereof, was great.
11 Itacen ya yi girma ya kuma yi ƙarfi, har tsayinsa ya taɓa sarari sama; ana iya ganinsa a ko’ina a duniya.
The tree, grew, and became strong, —and, the height thereof, reached unto the heavens, and, the view thereof, unto the end of all the land:
12 Ganyayensa suna da kyau, yana da’ya’ya jingim, abinci kuma domin kowa da kowa. A ƙarƙashinsa namun jeji suke samun wurin hutawa, kuma tsuntsayen sama suna zaune a bisa rassansa; daga cikinsa kowace halitta take cin abinci.
The foliage thereof, was beautiful, and, the fruit thereof, abundant, and there was food for all therein, —under it, the wild beast of the field found shade, and, among its branches, dwelt the birds of the heavens, and, therefrom, was well fed, all flesh.
13 “A cikin wahayin da gani sa’ad da nake kwance a kan gadona, Na duba, a gabana kuwa ga wani ɗan saƙo, mai tsarki, yana saukowa daga sama.
I was looking, in the visions of my head, upon my bed, when lo! a watcher and holy one, outer the heavens, coming down.
14 Sai ya yi kira da babbar murya ya ce, ‘A sare itacen a kuma yayyanka rassansa; a karkaɗe ganyensa a kuma warwatsar da’ya’yansa. Bari dabbobi su tashi daga ƙarƙashinsa da kuma tsuntsayen da suke a rassansa.
He cried aloud, and, thus, he said—Hew ye down the tree, and lop off its branches, strip off its leaves, and scatter its fruit, —let the wild beasts flee from under it, and the birds, out of its branches;
15 Amma a bar kututturen da kuma saiwoyinsa, a daure shi da ƙarfe da kuma tagulla, a bar shi a cikin ƙasa, a cikin ciyayin filaye. “‘Bari yă jiƙu da raɓar, bari yă zauna cikin dabbobi tare da tsire-tsiren duniya.
Nevertheless, the stock of its roots in the earth, leave ye, yea in a bond of iron and bronze, in the tender grass of the field, and, with the dew of the heavens, let it be drenched, and, with the wild beasts, be its portion, amongst, the herbage of the earth;
16 Bari a canja tunaninsa irin na mutane a ba shi tunani irin na dabbobi, har sau bakwai su wuce a kansa.
Let, its heart, from a man’s, be changed, and, the heart of a wild beast, be given to it, —and let seven seasons pass over it.
17 “‘An sanar da wannan matsayi ne ta bakin’yan saƙo, masu tsarki ne kuwa suka sanar da hukuncin, domin masu rai su sani Mafi Ɗaukaka ne mai iko duka a bisa kowane mulkin mutane, yakan kuma ba wa duk wanda ya ga dama, yakan sanya talaka yă zama sarki.’
By the decree of the watchers, is the thing, and [by] the mandate of the holy ones, the matter: to the intent that the living, may get to know, that the Most High, hath dominion, over the kingdom of men, and, to whomsoever he pleaseth, he giveth it, and, one low among men, he setteth up over it.
18 “Wannan shi ne mafarkin da ni, Nebukadnezzar, na yi. Yanzu Belteshazar, sai ka faɗa mini abin da yake nufi, domin babu wani a cikin masu hikima a mulkina da ya iya fassara mini shi. Amma za ka iya, domin ruhun alloli masu tsarki yana a bisanka.”
This dream, have, I, King Nebuchadnezzar, seen. Thou, therefore, O Belteshazzar, the interpretation, do thou tell, forasmuch as, all the wise men of my kingdom, are unable, the interpretation, to make known to me, but, thou, art able, because, the spirit of the holy gods, is in thee.
19 Sai Daniyel (wanda ake kira Belteshazar) ya tsaya zugum na ɗan lokaci, tunaninsa ya ba shi tsoro. Saboda haka sarki ya ce, “Belteshazar, kada ka bar mafarkin ko ma’anarsa ta tayar maka da hankali.” Belteshazar ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, in dai har mafarkin zai tsaya a kan abokan gābanka da ma’anarsa kuma ta faɗa kan maƙiyan!
Then, Daniel, whose name was Belteshazzar, was astonished for about one moment, and, his thoughts, troubled him. The king spake and said, O Belteshazzar, let neither, the dream, nor the interpretation, trouble thee. Belteshazzar answered and said, My Lord, The dream, be for them who hate thee, and, the interpretation, for them who are thy foes.
20 Itacen da ka gani; wanda ya yi girma da ƙarfe, da tsayinsa ya taɓa sararin sama, wanda ana ganinsa ko’ina a duniya,
The tree which thou sawest, which grew and became strong, whose, height, reached unto the heavens, and, the view, thereof to all the earth:
21 wanda ganyayensa masu kyau ne yana da’ya’yan itace da yawa, wanda yake ba da abinci ga duka, yana ba da wurin hutu ga namun jeji, kuma rassansa suna ɗauke da sheƙar tsuntsayen sama.
Whose, foliage, was beautiful, and whose, fruit, abundant, and, food for all, was in it, —under it, dwelt the wild beasts of the field, and, in the branches thereof, nestled the birds of the heavens:
22 Ya sarki kai ne itacen nan! Ka yi girma da ƙarfi; girmanka kuma ta kai har sama, mulkinka kuma ya kai ko’ina a duniya.
Thyself, it is, O king, in that thou art grown, and become strong, —and, thy greatness hath grown, and reached to the heavens, and, thy dominion, to the end of the earth.
23 “Ya sarki ka ga ɗan saƙon mai tsarkin nan, yana saukowa daga sama yana cewa, ‘A sare itacen a hallaka shi, amma a bar kututturensa daure da ƙarfe da tagulla, a bar shi can a ɗanyar ciyawar filaye, ya jiƙe da raɓa, ya zauna tare da namun jeji har shekara bakwai.’
And, whereas the king saw a watcher and holy one coming down out of the heavens, who said, Hew ye down the tree and despoil it, nevertheless, the stock of its roots—in the earth, leave ye, even in a bond of iron and bronze, in the tender grass of the field, —and, with the dew of the heavens, let it he drenched, and, along with the wild beasts of the field, be its portion, until that, seven seasons, pass over it.
24 “Ga fassarar, ya sarki, wannan ita ce doka wadda Mafi Ɗaukaka ya bayar a kan ranka yă daɗe, sarkina.
This, is the interpretation, O king, —and, the decree of the Most High, it is, which hath come upon my lord the king:
25 Za a kore ka daga cikin mutane, za ka kuma zauna cikin namun jeji; za ka ci ciyawa kamar shanu, za ka jiƙe da raɓa har shekara bakwai cif sa’an nan za ka sani cewa Mafi Ɗaukaka ne mai iko duka a kan dukan mulkoki a duniya, yake kuma ba da mulki ga duk wanda ya ga dama.
That, thee, are they going to drive forth from among men, and, along with the wild beasts of the field, shall be thy dwelling, and, grass—like oxen, will they suffer, thee, to eat, and, with the dew of the heavens, will they suffer, thee, to be drenched, and, seven seasons, shall pass over thee, —until that thou come to know, that the Most High, hath dominion, over the kingdom of men, and, to whomsoever he pleaseth, he giveth it.
26 Umarni na barin kututturen itacen da saiwoyinsa yana nufin cewa za a maido maka da mulkinka a lokacin da ka gane cewa Mai sama ne yake mulki.
And, whereas they gave word to leave the stock of the roots of the tree, thy kingdom, unto thee, is sure, —after that thou come to know, that the heavens, have dominion.
27 Saboda haka, ya sarki, ina roƙonka ka karɓi shawarar da zan ba ka; ka furta zunubanka ta wurin yin abin da yake daidai. Ka bar muguntarka, ka aikata alheri ga waɗanda ake wulaƙantawa, wataƙila za a ƙara tsawon kwanakinka da salama.”
Wherefore, O king, let, my counsel, be pleasing unto thee, thy sin, then, —by righteousness, break thou off, and, thine iniquities, by shewing favour to the oppressed, —if so be it may become the lengthening out of thy security.
28 Duk wannan kuwa ya faru da sarki Nebukadnezzar.
All this, came upon Nebuchadnezzar the king.
29 Bayan wata goma sha biyu, a sa’ad da sarki yake takawa a bisan saman ɗakin fadar Babilon,
At the end of twelve months, over the palace of the kingdom of Babylon, was he walking:
30 sai ya ce, “Ba wannan ita ce Babilon babba da na gina domin wurin zaman sarautar Babilon, da ikona kuma domin ɗaukakar darajata ba?”
the king spake and said, Is not, this, Babylon the great, —which, I myself, have built as the home of the kingdom, by the might of my power, and for the dignity of my majesty?
31 Tun kalmomin suna cikin bakinsa sai ya ji murya daga sama tana cewa, “Wannan shi ne abin da aka zartar a kanka, Sarki Nebukadnezzar. An karɓe ikon mulkinka.
While yet the word was in the mouth of the king, a voice, out of the heavens, fell, —Unto thee, is it said, O Nebuchadnezzar the king, The kingdom, hath departed from thee;
32 Za a kore ka daga cikin mutane za ka kuma yi rayuwa tare da namun jeji. Za ka ci ciyawa kamar sa har shekara bakwai cif, sa’an nan za ka gane Mafi Ɗaukaka ne mai iko duka a kan dukan mulkoki a duniya, yake kuma ba da mulki ga duk wanda ya ga dama.”
And, from among men, are they going to drive, thee, forth, and, with the wild beast of the field, shall be thy dwelling, grass—like oxen, will they suffer, thee, to eat, and, seven seasons, shall pass over thee, —until that thou come to know that the Most High, hath dominion, over the kingdom of men, and, to whomsoever he pleaseth, he giveth it.
33 Nan da nan abin da aka faɗa a kan Nebukadnezzar tabbatarsa ya cika. Aka kore shi daga cikin mutane ya kuma shiga cin ciyawa kamar shanu. Jikinsa ya jiƙe da raɓa, har gashinsa ya yi tsawo kamar fikafikan gaggafa, kumbarsa kuma suka yi tsawo kamar na tsuntsu.
Immediately, the word, was fulfilled upon Nebuchadnezzar, and, from among men, was he driven forth, and, grass—like oxen, did he eat, and, with the dew of the heavens, his body was drenched, —until that, his hair, like to eagles’ feathers, was grown, and his nails, like birds’ claws.
34 A ƙarshen waɗannan kwanaki, ni, Nebukadnezzar, na ɗaga idanuna sama, sai hankalina ya komo mini. Na kuwa yabi Maɗaukaki, na girmama shi, na ɗaukaka shi wanda yake rayayye har abada.
And, at the end of the days, I, Nebuchadnezzar, mine eyes unto the heavens, did uplift, and, mine understanding, unto me, returned, and, the Most High, I blessed, and, to him that liveth age-abidingly, I rendered praise and honour, —whose dominion, is an age-abiding dominion, and, his kingdom, lasteth from generation to generation;
35 Dukan mutanen duniya
And, all the inhabitants of the earth, as nothing, are accounted, and, according to his own pleasure, dealeth he—with the army of the heavens, and the inhabitants of the earth, —and none there is who can smite upon his hand, or say to him, What hast thou done?
36 A lokacin nan hankalina ya komo mini, sai aka mayar mini da masarautata mai daraja, da martabata, da girmana.’Yan majalisata da fadawana suka nemo ni. Aka maido ni kan gadon sarautata da daraja fiye da ta dā.
At the same time, mine understanding, returned unto me, and, for the dignity of my kingdom, my majesty and my brightness, returned unto me, and, unto me, my nearest friends and my nobles, did seek, —and, over my kingdom, was I restored, and, surpassing greatness, was added unto me.
37 Yanzu ni, Nebukadnezzar, ina yabon Sarkin sama, ina waƙa ina kuma darjanta shi, saboda dukan abin da ya yi mini, mai kyau ne kuma dukan hanyoyinsa gaskiya ne. Kuma duk masu tafiya da girman kai zai ƙasƙantar da su.
Now, I, Nebuchadnezzar, am praising and extolling and honouring the King of the Heavens, all whose works, are truth, and, his ways, right; and, them who walk in pride, he is able to abase,

< Daniyel 4 >