< Daniyel 4 >
1 Daga sarki Nebukadnezzar. Zuwa ga mutane da al’ummai da kuma kowane yare, da suke zama a duniya. Salama mai yawa ta tabbata a gare ku!
Nebuchadnezzar the king unto all the peoples, nations, and languages, that dwell in all the earth: Peace be multiplied unto you.
2 Ina murna in shaida muku game da alamu da al’ajabai waɗanda Allah Mafi Ɗaukaka ya yi ta wurina.
It hath seemed good unto me to declare the signs and wonders that the Most High God hath wrought toward me.
3 Alamunsa da girma suke,
How great are his signs! and how mighty are his wonders! His kingdom is an everlasting kingdom, and his dominion is from generation to generation.
4 Ni, Nebukadnezzar, ina zaune a gidana cikin fadata, ina jin daɗi ina bunkasa.
I Nebuchadnezzar was at rest in my house, and flourishing in my palace.
5 Na yi mafarkin da ya ba ni tsoro. A sa’ad da nake kwance a gadona, siffofi da wahayoyi da suka bi ta cikin tunanina sun firgita ni.
I saw a dream which made me afraid, and the thoughts upon my bed and the visions of my head troubled me.
6 Don haka na ba da umarni a tattaro dukan masu hikima na Babilon su bayyana a gabana domin su fassara mini mafarkin.
And I made a decree to bring in all the wise men of Babylon before me, that they might make known unto me the interpretation of the dream.
7 Sa’ad da masu sihiri, da masu dabo, da masanan taurari da masu duba suka zo, na faɗa musu mafarkin, amma ba su iya fassarta mini mafarkin ba.
Then came in the scribes, the magicians, the Chaldeans, and the astrologers; and I told the dream before them; but they did not make known unto me the interpretation of it.
8 A ƙarshe, sai Daniyel ya zo gabana na kuma faɗa masa mafarkin. (Ana ce da shi Belteshazar, wanda aka ba shi sunan allahna kuma ruhun alloli masu tsarki suna a bisansa.)
But at the last Daniel came in before me, whose name is Belteshazzar, according to the name of my god, and in whom is the spirit of the holy gods; and before him I told the dream:
9 Na ce, “Belteshazar, shugaban masu sihiri, na san ruhun alloli suna a kanka, babu wani asirin da zai fi ƙarfin ganewarka. Ga dai mafarkin da na yi, sai ka fassara mini.
O Belteshazzar, master of the scribes, because I know that the spirit of the holy gods is in thee, and no secret is too hard for thee, tell me the visions of my dream which I have seen, and the interpretation of it.
10 Waɗannan su ne wahayin da na gani a lokacin da nake kwance a gadona, na duba, a gabana kuwa ga wani itace a kafe a tsakiyar duniya, yana da tsawo ƙwarai.
Thus were the visions of my head upon my bed: I saw, and behold a tree in the midst of the earth, and its height was great.
11 Itacen ya yi girma ya kuma yi ƙarfi, har tsayinsa ya taɓa sarari sama; ana iya ganinsa a ko’ina a duniya.
The tree grew, and was strong, and its height reached unto the heavens, and the sight thereof to the end of all the earth.
12 Ganyayensa suna da kyau, yana da’ya’ya jingim, abinci kuma domin kowa da kowa. A ƙarƙashinsa namun jeji suke samun wurin hutawa, kuma tsuntsayen sama suna zaune a bisa rassansa; daga cikinsa kowace halitta take cin abinci.
Its leaves were beautiful, and its fruit abundant, and in it was food for all: the beasts of the field found shade under it, and the birds of the heavens dwelt in its branches, and all flesh was fed from it.
13 “A cikin wahayin da gani sa’ad da nake kwance a kan gadona, Na duba, a gabana kuwa ga wani ɗan saƙo, mai tsarki, yana saukowa daga sama.
I saw in the visions of my head upon my bed, and behold, a watcher and a holy one came down from the heavens;
14 Sai ya yi kira da babbar murya ya ce, ‘A sare itacen a kuma yayyanka rassansa; a karkaɗe ganyensa a kuma warwatsar da’ya’yansa. Bari dabbobi su tashi daga ƙarƙashinsa da kuma tsuntsayen da suke a rassansa.
he cried aloud, and said thus: Hew down the tree, and cut off its branches, shake off its leaves, and scatter its fruit; let the beasts get away from under it, and the birds from its branches.
15 Amma a bar kututturen da kuma saiwoyinsa, a daure shi da ƙarfe da kuma tagulla, a bar shi a cikin ƙasa, a cikin ciyayin filaye. “‘Bari yă jiƙu da raɓar, bari yă zauna cikin dabbobi tare da tsire-tsiren duniya.
Nevertheless leave the stump of its roots in the earth, even with a band of iron and brass, in the tender grass of the field; and let it be bathed with the dew of heaven, and let his portion be with the beasts in the grass of the earth.
16 Bari a canja tunaninsa irin na mutane a ba shi tunani irin na dabbobi, har sau bakwai su wuce a kansa.
Let his heart be changed from man's, and let a beast's heart be given unto him; and let seven times pass over him.
17 “‘An sanar da wannan matsayi ne ta bakin’yan saƙo, masu tsarki ne kuwa suka sanar da hukuncin, domin masu rai su sani Mafi Ɗaukaka ne mai iko duka a bisa kowane mulkin mutane, yakan kuma ba wa duk wanda ya ga dama, yakan sanya talaka yă zama sarki.’
This sentence is by the decree of the watchers, and the decision by the word of the holy ones: that the living may know that the Most High ruleth over the kingdom of men, and giveth it to whomsoever he will, and setteth up over it the basest of men.
18 “Wannan shi ne mafarkin da ni, Nebukadnezzar, na yi. Yanzu Belteshazar, sai ka faɗa mini abin da yake nufi, domin babu wani a cikin masu hikima a mulkina da ya iya fassara mini shi. Amma za ka iya, domin ruhun alloli masu tsarki yana a bisanka.”
This dream I, king Nebuchadnezzar, have seen; and thou, Belteshazzar, tell the interpretation, forasmuch as all the wise men of my kingdom are not able to make known unto me the interpretation; but thou art able, for the spirit of the holy gods is in thee.
19 Sai Daniyel (wanda ake kira Belteshazar) ya tsaya zugum na ɗan lokaci, tunaninsa ya ba shi tsoro. Saboda haka sarki ya ce, “Belteshazar, kada ka bar mafarkin ko ma’anarsa ta tayar maka da hankali.” Belteshazar ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, in dai har mafarkin zai tsaya a kan abokan gābanka da ma’anarsa kuma ta faɗa kan maƙiyan!
Then Daniel, whose name is Belteshazzar, was astonied for one hour, and his thoughts troubled him. The king spoke and said, Belteshazzar, let not the dream, nor its interpretation, trouble thee. Belteshazzar answered and said, My lord, the dream be to them that hate thee, and its interpretation to thine enemies!
20 Itacen da ka gani; wanda ya yi girma da ƙarfe, da tsayinsa ya taɓa sararin sama, wanda ana ganinsa ko’ina a duniya,
The tree that thou sawest, which grew and was strong, whose height reached unto the heavens, and the sight of it to all the earth;
21 wanda ganyayensa masu kyau ne yana da’ya’yan itace da yawa, wanda yake ba da abinci ga duka, yana ba da wurin hutu ga namun jeji, kuma rassansa suna ɗauke da sheƙar tsuntsayen sama.
whose leaves were beautiful, and its fruit abundant, and in it was food for all; under which the beasts of the field dwelt, and in whose branches the birds of the heavens had their habitation:
22 Ya sarki kai ne itacen nan! Ka yi girma da ƙarfi; girmanka kuma ta kai har sama, mulkinka kuma ya kai ko’ina a duniya.
it is thou, O king, who art grown and become strong; for thy greatness is grown, and reacheth unto the heavens, and thy dominion to the end of the earth.
23 “Ya sarki ka ga ɗan saƙon mai tsarkin nan, yana saukowa daga sama yana cewa, ‘A sare itacen a hallaka shi, amma a bar kututturensa daure da ƙarfe da tagulla, a bar shi can a ɗanyar ciyawar filaye, ya jiƙe da raɓa, ya zauna tare da namun jeji har shekara bakwai.’
And whereas the king saw a watcher and a holy one coming down from the heavens, and saying, Hew the tree down, and destroy it; nevertheless leave the stump of its roots in the earth, even with a band of iron and brass, in the tender grass of the field; and let it be bathed with the dew of heaven, and let his portion be with the beasts of the field, till seven times pass over him:
24 “Ga fassarar, ya sarki, wannan ita ce doka wadda Mafi Ɗaukaka ya bayar a kan ranka yă daɗe, sarkina.
this is the interpretation, O king, and it is the decree of the Most High, which cometh upon my lord the king:
25 Za a kore ka daga cikin mutane, za ka kuma zauna cikin namun jeji; za ka ci ciyawa kamar shanu, za ka jiƙe da raɓa har shekara bakwai cif sa’an nan za ka sani cewa Mafi Ɗaukaka ne mai iko duka a kan dukan mulkoki a duniya, yake kuma ba da mulki ga duk wanda ya ga dama.
They shall drive thee from men, and thy dwelling shall be with the beasts of the field, and they shall make thee to eat grass as oxen, and thou shalt be bathed with the dew of heaven; and seven times shall pass over thee, till thou know that the Most High ruleth over the kingdom of men, and giveth it to whomsoever he will.
26 Umarni na barin kututturen itacen da saiwoyinsa yana nufin cewa za a maido maka da mulkinka a lokacin da ka gane cewa Mai sama ne yake mulki.
And whereas it was commanded to leave the stump of the roots of the tree; thy kingdom shall remain unto thee, after that thou shalt know that the heavens do rule.
27 Saboda haka, ya sarki, ina roƙonka ka karɓi shawarar da zan ba ka; ka furta zunubanka ta wurin yin abin da yake daidai. Ka bar muguntarka, ka aikata alheri ga waɗanda ake wulaƙantawa, wataƙila za a ƙara tsawon kwanakinka da salama.”
Therefore, O king, let my counsel be acceptable unto thee, and break off thy sins by righteousness, and thine iniquities by shewing mercy to the poor; if it may be a lengthening of thy tranquillity.
28 Duk wannan kuwa ya faru da sarki Nebukadnezzar.
All this came upon king Nebuchadnezzar.
29 Bayan wata goma sha biyu, a sa’ad da sarki yake takawa a bisan saman ɗakin fadar Babilon,
At the end of twelve months he was walking upon the royal palace of Babylon:
30 sai ya ce, “Ba wannan ita ce Babilon babba da na gina domin wurin zaman sarautar Babilon, da ikona kuma domin ɗaukakar darajata ba?”
the king spoke and said, Is not this great Babylon, that I have built for the house of the kingdom by the might of my power and for the glory of my majesty?
31 Tun kalmomin suna cikin bakinsa sai ya ji murya daga sama tana cewa, “Wannan shi ne abin da aka zartar a kanka, Sarki Nebukadnezzar. An karɓe ikon mulkinka.
While the word was in the king's mouth, there fell a voice from the heavens: King Nebuchadnezzar, to thee it is spoken: The kingdom is departed from thee;
32 Za a kore ka daga cikin mutane za ka kuma yi rayuwa tare da namun jeji. Za ka ci ciyawa kamar sa har shekara bakwai cif, sa’an nan za ka gane Mafi Ɗaukaka ne mai iko duka a kan dukan mulkoki a duniya, yake kuma ba da mulki ga duk wanda ya ga dama.”
and they shall drive thee from men, and thy dwelling shall be with the beasts of the field; they shall make thee to eat grass as oxen, and seven times shall pass over thee, until thou know that the Most High ruleth over the kingdom of men, and giveth it to whomsoever he will.
33 Nan da nan abin da aka faɗa a kan Nebukadnezzar tabbatarsa ya cika. Aka kore shi daga cikin mutane ya kuma shiga cin ciyawa kamar shanu. Jikinsa ya jiƙe da raɓa, har gashinsa ya yi tsawo kamar fikafikan gaggafa, kumbarsa kuma suka yi tsawo kamar na tsuntsu.
The same hour was the word fulfilled upon Nebuchadnezzar; and he was driven from men, and ate grass as oxen; and his body was bathed with the dew of heaven, till his hair grew like eagles' [feathers], and his nails like birds' [claws].
34 A ƙarshen waɗannan kwanaki, ni, Nebukadnezzar, na ɗaga idanuna sama, sai hankalina ya komo mini. Na kuwa yabi Maɗaukaki, na girmama shi, na ɗaukaka shi wanda yake rayayye har abada.
And at the end of the days I Nebuchadnezzar lifted up mine eyes unto the heavens, and mine understanding returned unto me, and I blessed the Most High, and I praised and honoured him that liveth for ever, whose dominion is an everlasting dominion, and his kingdom is from generation to generation.
And all the inhabitants of the earth are reputed as nothing; and he doeth according to his will in the army of the heavens, and among the inhabitants of the earth; and none can stay his hand, or say unto him, What doest thou?
36 A lokacin nan hankalina ya komo mini, sai aka mayar mini da masarautata mai daraja, da martabata, da girmana.’Yan majalisata da fadawana suka nemo ni. Aka maido ni kan gadon sarautata da daraja fiye da ta dā.
At the same time mine understanding returned unto me; and for the glory of my kingdom, my majesty and brightness returned unto me; and my counsellors and my nobles sought me; and I was established in my kingdom, and excellent greatness was added unto me.
37 Yanzu ni, Nebukadnezzar, ina yabon Sarkin sama, ina waƙa ina kuma darjanta shi, saboda dukan abin da ya yi mini, mai kyau ne kuma dukan hanyoyinsa gaskiya ne. Kuma duk masu tafiya da girman kai zai ƙasƙantar da su.
Now I Nebuchadnezzar praise and extol and honour the King of the heavens, all whose works are truth, and his paths judgment: and those that walk in pride he is able to abase.