< Daniyel 4 >

1 Daga sarki Nebukadnezzar. Zuwa ga mutane da al’ummai da kuma kowane yare, da suke zama a duniya. Salama mai yawa ta tabbata a gare ku!
Nebuchadnezzar, the king, to all peoples, nations, and languages, who dwell in the whole world, may peace be increased with you.
2 Ina murna in shaida muku game da alamu da al’ajabai waɗanda Allah Mafi Ɗaukaka ya yi ta wurina.
The supreme God has accomplished signs and wonders with me. Therefore, it has pleased me to proclaim
3 Alamunsa da girma suke,
his signs, which are great, and his wonders, which are mighty. For his kingdom is an everlasting kingdom, and his power continues from generation to generation.
4 Ni, Nebukadnezzar, ina zaune a gidana cikin fadata, ina jin daɗi ina bunkasa.
I, Nebuchadnezzar, was content in my house and prospering in my palace.
5 Na yi mafarkin da ya ba ni tsoro. A sa’ad da nake kwance a gadona, siffofi da wahayoyi da suka bi ta cikin tunanina sun firgita ni.
I saw a dream that terrified me, and my thoughts on my bed and the visions in my head disturbed me.
6 Don haka na ba da umarni a tattaro dukan masu hikima na Babilon su bayyana a gabana domin su fassara mini mafarkin.
And so a decree was established by me, that all of the wise men of Babylon should be brought in before me, and that they should reveal to me the answer to the dream.
7 Sa’ad da masu sihiri, da masu dabo, da masanan taurari da masu duba suka zo, na faɗa musu mafarkin, amma ba su iya fassarta mini mafarkin ba.
Then the seers, the astrologers, the Chaldeans, and the soothsayers entered, and I explained about the dream in their presence, but they did not reveal its answer to me.
8 A ƙarshe, sai Daniyel ya zo gabana na kuma faɗa masa mafarkin. (Ana ce da shi Belteshazar, wanda aka ba shi sunan allahna kuma ruhun alloli masu tsarki suna a bisansa.)
And then their colleague came in before me, Daniel, (whose name is Belteshazzar according to the name of my god, ) who has the spirit of the holy gods within his very self, and I told the dream directly to him.
9 Na ce, “Belteshazar, shugaban masu sihiri, na san ruhun alloli suna a kanka, babu wani asirin da zai fi ƙarfin ganewarka. Ga dai mafarkin da na yi, sai ka fassara mini.
Belteshazzar, leader of the seers, since I know that you have in you the spirit of the holy gods, and that no mystery is unreachable to you, explain to me the visions of my dreams, which I saw, and the solution to them.
10 Waɗannan su ne wahayin da na gani a lokacin da nake kwance a gadona, na duba, a gabana kuwa ga wani itace a kafe a tsakiyar duniya, yana da tsawo ƙwarai.
This was the vision of my head on my bed. I looked, and behold, a tree in the middle of the earth, and its height was exceedingly great.
11 Itacen ya yi girma ya kuma yi ƙarfi, har tsayinsa ya taɓa sarari sama; ana iya ganinsa a ko’ina a duniya.
The tree was great and strong, and its height reached up to heaven. It could be seen all the way to the ends of the entire earth.
12 Ganyayensa suna da kyau, yana da’ya’ya jingim, abinci kuma domin kowa da kowa. A ƙarƙashinsa namun jeji suke samun wurin hutawa, kuma tsuntsayen sama suna zaune a bisa rassansa; daga cikinsa kowace halitta take cin abinci.
Its leaves were very beautiful, and its fruit was very abundant, and in it was food for the whole world. Under it, animals and beasts were dwelling, and in its branches, the birds of the sky were sheltered, and from it, all flesh was fed.
13 “A cikin wahayin da gani sa’ad da nake kwance a kan gadona, Na duba, a gabana kuwa ga wani ɗan saƙo, mai tsarki, yana saukowa daga sama.
I saw in the vision of my head upon my blanket, and behold, a watcher and a holy one descended from heaven.
14 Sai ya yi kira da babbar murya ya ce, ‘A sare itacen a kuma yayyanka rassansa; a karkaɗe ganyensa a kuma warwatsar da’ya’yansa. Bari dabbobi su tashi daga ƙarƙashinsa da kuma tsuntsayen da suke a rassansa.
He cried out loudly, and he said this: “Cut down the tree and prune its branches; shake off its leaves and scatter its fruits; let flee the beasts, which are under it, and the birds from its branches.
15 Amma a bar kututturen da kuma saiwoyinsa, a daure shi da ƙarfe da kuma tagulla, a bar shi a cikin ƙasa, a cikin ciyayin filaye. “‘Bari yă jiƙu da raɓar, bari yă zauna cikin dabbobi tare da tsire-tsiren duniya.
Nevertheless, leave the stump of its roots in the earth, and let it be bound with a band of iron and brass among the plants, which are close by, and let it be touched by the dew of heaven, and let its place be with the wild animals among the plants of the earth.
16 Bari a canja tunaninsa irin na mutane a ba shi tunani irin na dabbobi, har sau bakwai su wuce a kansa.
Let his heart be changed from being human, and let the heart of a wild animal be given to him, and let seven periods of time pass over him.
17 “‘An sanar da wannan matsayi ne ta bakin’yan saƙo, masu tsarki ne kuwa suka sanar da hukuncin, domin masu rai su sani Mafi Ɗaukaka ne mai iko duka a bisa kowane mulkin mutane, yakan kuma ba wa duk wanda ya ga dama, yakan sanya talaka yă zama sarki.’
This is the decree from the judgment of the watchers, and the decision and proclamation of the holy ones, until the living shall know that the Supreme One is ruler in the kingdom of men, and that he will give it to whomever he wills, and he will appoint the lowest man over it.”
18 “Wannan shi ne mafarkin da ni, Nebukadnezzar, na yi. Yanzu Belteshazar, sai ka faɗa mini abin da yake nufi, domin babu wani a cikin masu hikima a mulkina da ya iya fassara mini shi. Amma za ka iya, domin ruhun alloli masu tsarki yana a bisanka.”
I, king Nebuchadnezzar, saw this dream. And so you, Belteshazzar, must quickly explain to me the interpretation because all the wise men of my kingdom are not able to declare the meaning of it to me. But you are able because the spirit of the holy gods is in you.
19 Sai Daniyel (wanda ake kira Belteshazar) ya tsaya zugum na ɗan lokaci, tunaninsa ya ba shi tsoro. Saboda haka sarki ya ce, “Belteshazar, kada ka bar mafarkin ko ma’anarsa ta tayar maka da hankali.” Belteshazar ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, in dai har mafarkin zai tsaya a kan abokan gābanka da ma’anarsa kuma ta faɗa kan maƙiyan!
Then Daniel, whose name was Belteshazzar, began silently to think within himself for about one hour, and his thoughts troubled him. But the king responded, saying, “Belteshazzar, do not let the dream and its interpretation disturb you.” Belteshazzar answered and said, “My lord, the dream is for those who hate you, and its interpretation may be for your enemies.
20 Itacen da ka gani; wanda ya yi girma da ƙarfe, da tsayinsa ya taɓa sararin sama, wanda ana ganinsa ko’ina a duniya,
The tree that you saw was lofty and strong; its height reached toward heaven, and it could be seen throughout the whole world.
21 wanda ganyayensa masu kyau ne yana da’ya’yan itace da yawa, wanda yake ba da abinci ga duka, yana ba da wurin hutu ga namun jeji, kuma rassansa suna ɗauke da sheƙar tsuntsayen sama.
And its branches were very beautiful, and its fruit very abundant, and in it was food for all. Under it, dwelt the beasts of the field, and in its branches, the birds of the air stayed.
22 Ya sarki kai ne itacen nan! Ka yi girma da ƙarfi; girmanka kuma ta kai har sama, mulkinka kuma ya kai ko’ina a duniya.
It is you, O king, who has been greatly esteemed, and you have grown strong. And you have increased your power, and it reaches towards heaven, and your rule is to the ends of the whole earth.
23 “Ya sarki ka ga ɗan saƙon mai tsarkin nan, yana saukowa daga sama yana cewa, ‘A sare itacen a hallaka shi, amma a bar kututturensa daure da ƙarfe da tagulla, a bar shi can a ɗanyar ciyawar filaye, ya jiƙe da raɓa, ya zauna tare da namun jeji har shekara bakwai.’
Yet the king also saw a watcher and a holy one descend from heaven and say: ‘Cut down the tree and scatter it; however, leave the stump of its roots in the earth, and let it be bound with iron and brass, among the surrounding plants, and let it be sprinkled with the dew of heaven, and let his feeding be with the wild beasts, until seven periods of time pass over him.’
24 “Ga fassarar, ya sarki, wannan ita ce doka wadda Mafi Ɗaukaka ya bayar a kan ranka yă daɗe, sarkina.
This is the interpretation of the judgment of the Most High, which has reached my lord, the king.
25 Za a kore ka daga cikin mutane, za ka kuma zauna cikin namun jeji; za ka ci ciyawa kamar shanu, za ka jiƙe da raɓa har shekara bakwai cif sa’an nan za ka sani cewa Mafi Ɗaukaka ne mai iko duka a kan dukan mulkoki a duniya, yake kuma ba da mulki ga duk wanda ya ga dama.
They will expel you from among men, and your dwelling will be with the beasts and the wild animals, and you will eat hay like an ox, and you will be drenched with the dew of heaven. Likewise, seven periods of time will pass over you, until you know that the Supreme One rules over the kingdom of men, and he gives it to whomever he wills.
26 Umarni na barin kututturen itacen da saiwoyinsa yana nufin cewa za a maido maka da mulkinka a lokacin da ka gane cewa Mai sama ne yake mulki.
But, since he commanded that the stump of its roots, that is, of the tree, should be left behind, your kingdom will be left for you, after you have realized that power is from divinity.
27 Saboda haka, ya sarki, ina roƙonka ka karɓi shawarar da zan ba ka; ka furta zunubanka ta wurin yin abin da yake daidai. Ka bar muguntarka, ka aikata alheri ga waɗanda ake wulaƙantawa, wataƙila za a ƙara tsawon kwanakinka da salama.”
Because of this, O king, let my counsel be acceptable to you. And redeem your sins with alms, and your iniquities with mercy towards the poor. Perhaps he will forgive your offenses.”
28 Duk wannan kuwa ya faru da sarki Nebukadnezzar.
All these things came upon king Nebuchadnezzar.
29 Bayan wata goma sha biyu, a sa’ad da sarki yake takawa a bisan saman ɗakin fadar Babilon,
After the end of twelve months, he was taking a walk in the palace of Babylon.
30 sai ya ce, “Ba wannan ita ce Babilon babba da na gina domin wurin zaman sarautar Babilon, da ikona kuma domin ɗaukakar darajata ba?”
And the king spoke out loud, saying, “Isn’t this the great Babylon, which I have built, as the home of the kingdom, by the strength of my power and in the glory of my excellence?”
31 Tun kalmomin suna cikin bakinsa sai ya ji murya daga sama tana cewa, “Wannan shi ne abin da aka zartar a kanka, Sarki Nebukadnezzar. An karɓe ikon mulkinka.
And while the words were still in the king’s mouth, a voice rushed down from heaven, “To you, O king Nebuchadnezzar, it is said: ‘Your kingdom will be taken away from you,
32 Za a kore ka daga cikin mutane za ka kuma yi rayuwa tare da namun jeji. Za ka ci ciyawa kamar sa har shekara bakwai cif, sa’an nan za ka gane Mafi Ɗaukaka ne mai iko duka a kan dukan mulkoki a duniya, yake kuma ba da mulki ga duk wanda ya ga dama.”
and they will expel you from among men, and your dwelling will be with the beasts and the wild animals. You will eat hay like an ox, and seven times will pass over you, until you know that the Supreme One rules in the kingdom of men, and he gives it to whomever he wills.’”
33 Nan da nan abin da aka faɗa a kan Nebukadnezzar tabbatarsa ya cika. Aka kore shi daga cikin mutane ya kuma shiga cin ciyawa kamar shanu. Jikinsa ya jiƙe da raɓa, har gashinsa ya yi tsawo kamar fikafikan gaggafa, kumbarsa kuma suka yi tsawo kamar na tsuntsu.
The same hour, the sentence was fulfilled upon Nebuchadnezzar, and he was driven away from among men, and he ate hay like an ox, and his body was drenched with the dew of heaven, until his hair increased like the feathers of eagles, and his nails like those of birds.
34 A ƙarshen waɗannan kwanaki, ni, Nebukadnezzar, na ɗaga idanuna sama, sai hankalina ya komo mini. Na kuwa yabi Maɗaukaki, na girmama shi, na ɗaukaka shi wanda yake rayayye har abada.
Therefore, at the end of these days, I, Nebuchadnezzar, lifted up my eyes to heaven, and my mind was restored to me. And I blessed the Most High, and I praised and glorified him who lives forever. For his power is an everlasting power, and his kingdom is from generation to generation.
35 Dukan mutanen duniya
And all the inhabitants of the earth are reputed as nothing before him. For he acts according to his own will, with the inhabitants of the earth just as with the holy inhabitants of heaven. And there is no one who can resist his hand, or say to him, “Why have you done this?”
36 A lokacin nan hankalina ya komo mini, sai aka mayar mini da masarautata mai daraja, da martabata, da girmana.’Yan majalisata da fadawana suka nemo ni. Aka maido ni kan gadon sarautata da daraja fiye da ta dā.
At the same time, my mind returned to me, and I arrived at the honor and glory of my kingdom. And my appearance was given back to me. And my nobles and my magistrates needed me. And I was restored to my kingdom, and even greater majesty was added to me.
37 Yanzu ni, Nebukadnezzar, ina yabon Sarkin sama, ina waƙa ina kuma darjanta shi, saboda dukan abin da ya yi mini, mai kyau ne kuma dukan hanyoyinsa gaskiya ne. Kuma duk masu tafiya da girman kai zai ƙasƙantar da su.
Therefore I, Nebuchadnezzar, now praise, and magnify, and glorify the King of heaven, because all his works and the judgments of his way are true, and those who go forth in arrogance, he is able to bring low.

< Daniyel 4 >