< Daniyel 3 >

1 Sarki Nebukadnezzar ya yi gunkin zinariya, tsawonsa kamu tasa’in, fāɗinsa kuma kamu tara ne, ya kafa shi a filin Dura a yankin Babilon.
Kral Nebukadnessar altın bir heykel yaptı; boyu altmış, eni altı arşındı. Onu Babil İli'nde, Dura Ovası'na dikti.
2 Sa’an nan ya aika a kira hakimai da wakilai da gwamnoni da mashawarta, da ma’aji, da alƙalai, da marubutan kotu, da dukan sauran ma’aikatan yankunan, suka hallara domin a rusuna wa wannan siffar da ya kafa.
Satrapları, kaymakamları, valileri, danışmanları, haznedarları, yargıçları, güvenlik görevlilerini ve illerin bütün öbür yüksek memurlarını diktiği heykeli adama törenine çağırttı.
3 Saboda haka sai hakimai, da wakilai da gwamnoni, mashawarta da ma’aji da alƙalai, da marubutan alƙalai, da kuma dukan ma’aikatan yankunan suka tattaru domin kaddamar da siffar da Nebukadnezzar ya kafa, suka kuma tsaya a gabansa.
Böylece satraplar, kaymakamlar, valiler, danışmanlar, haznedarlar, yargıçlar, güvenlik görevlileri ve illerin bütün öbür yüksek memurları Kral Nebukadnessar'ın diktiği heykeli adama töreni için toplanarak heykelin önünde durdular.
4 Sai mai shela ya daga murya da ƙarfi ya ce, “Wannan shi ne abin da aka umarce ku ku yi, ya ku mutane da al’umma da kowane yare.
Sonra haberci yüksek sesle bağırdı: “Ey halklar, uluslar, her dilden insanlar, size şöyle yapmanız buyruluyor:
5 Da zarar kuka ji karar ƙaho, da sarewa, da garaya da goge da molo da algaita da kowane irin kaɗe-kaɗe da bushe-bushe ku rusuna ku yi sujada ga wannan gunkin da sarki Nebukadnezzar ya kafa.
Boru, ney, lir, kanun, arp, davul ve her çeşit çalgı sesini duyar duymaz yere kapanıp Kral Nebukadnessar'ın dikmiş olduğu altın heykele tapınacaksınız.
6 Duk wanda bai rusuna ya yi sujada ba, nan take za a jefa shi a cikin tendarun wuta.”
Her kim yere kapanıp tapınmazsa hemen kızgın fırına atılacaktır.”
7 Saboda haka, da zarar suka ji karar ƙaho, da sarewa, garaya da goge da kowane irin kaɗe-kaɗe da bushe-bushe da kowane irin kaɗe-kaɗe kowane mutum da ko wace al’umma da kowane irin yare suka sunkuya suka yi sujada ga wannan siffa ta zinariya da sarki Nebukadnezzar ya kafa.
Bu yüzden ne zaman boru, ney, lir, kanun, arp ve her çeşit çalgı sesi duyulsa, bütün halklar, uluslar, her dilden insanlar yere kapanıp Kral Nebukadnessar'ın diktiği altın heykele tapındılar.
8 A wannan lokaci sai waɗansu masanan taurari suka zo gaba suka yi karar Yahudawa.
Bunun üzerine bazı Kildaniler yaklaşıp Yahudiler'i suçladılar.
9 Suka ce wa sarki Nebukadnezzar, “Ran sarki yă daɗe,
Kral Nebukadnessar'a, “Ey kral, sen çok yaşa!” dediler,
10 Ya sarki, ka fitar da doka, cewa duk wanda ya ji karar ƙaho, da sarewa, da garayu da goge, da molo da algaita da kowane irin kayan kaɗe-kaɗe da bushe-bushe sai yă rusuna yă yi sujada ga siffar zinariya,
“Boru, ney, lir, kanun, arp, davul ve her çeşit çalgı sesini duyan herkes yere kapanıp altın heykele tapınacak; kim yere kapanıp tapınmazsa kızgın fırına atılacak diye bir buyruk çıkardın, ey kral.
11 kuma cewa duk wanda bai rusuna ya yi sujadar ba za a jefa shi cikin tanderun wuta.
12 Amma sai ga waɗansu Yahudawa waɗanda ka ɗora su a kan harkokin yankin Babilon, wato, Shadrak, Meshak da Abednego waɗanda ba su kula da umarninka ba, ya sarki. Ba su bauta wa allolin ba balle su yi sujada ga gunkin zinariya da ka kafa.”
Oysa Babil İli'nde yüksek görevlere atadığın Şadrak, Meşak, Abed-Nego adında bazı Yahudiler var. Bu adamlar seni saymadılar, ey kral. Senin ilahlarına kulluk etmiyor, diktiğin altın heykele tapınmıyorlar.”
13 Cikin fushi da hasala, Nebukadnezzar ya aika a kira Shadrak, Meshak da Abednego. Aka kawo waɗannan mutane a gaban sarki,
Büyük öfkeye kapılan Nebukadnessar, Şadrak'ı, Meşak'ı, Abed-Nego'yu çağırttı. Bu kişiler kralın yanına getirildiler.
14 sai Nebukadnezzar ya ce musu, “Gaskiya ne Shadrak, Meshak da Abednego, cewa kun ƙi ku bauta wa alloli kuka kuma ƙi yi sujada ga gunkin da na kafa?
Nebukadnessar, “Ey Şadrak, Meşak, Abed-Nego, ilahlarıma kulluk etmediğiniz, diktiğim altın heykele tapınmadığınız doğru mu?” diye sordu,
15 Yanzu sa’ad da kuka ji karar ƙaho, da sarewa, da garaya, da goge, da molo da algaita da kowane irin kaɗe-kaɗe da bushe-bushe, in kuna a shirye ku rusuna ƙasa ku yi wa wannan gunkin da na yi sujada, to, da kyau. Amma in ba ku yi sujada ba, za a je fa ku yanzu a cikin tanderun wutar nan. In ga kowane ne allahn nan da zai kuɓutar da ku daga hannuna?”
“Şimdi boru, ney, lir, kanun, arp, davul ve her çeşit çalgı sesini duyar duymaz yere kapanıp yaptığım heykele tapınmaya hazırsanız ne iyi! Ama ona tapınmazsanız, hemen kızgın fırına atılacaksınız. O zaman bakalım hangi ilah sizi elimden kurtaracak?”
16 Sai Shadrak, Meshak da Abednego suka amsa wa sarki suka ce, “Ya Nebukadnezzar, ba mu bukata mu kāre kanmu a gabanka a kan wannan batu.
Şadrak, Meşak, Abed-Nego, “Bu konuda kendimizi savunma gereğini duymuyoruz” diye karşılık verdiler,
17 In an jefa mu cikin tanderun wutar nan, Allahn da muke bauta wa zai iya cetonmu daga ita, kuma ya sarki, zai cece mu daga hannunka.
“Kızgın fırına atılsak bile, ey kral, kendisine kulluk ettiğimiz Tanrı bizi kızgın fırından kurtarabilir; senin elinden de bizi kurtaracaktır.
18 Amma ko da bai cece mu ba, muna so ka sani, ya sarki; cewa ba za mu bauta wa allolinka ba ko kuma mu yi sujada ga gunkin zinariyar da ka kafa ba.”
Ama bizi kurtarmasa bile bil ki, ey kral, ilahlarına kulluk etmeyiz, diktiğin altın heykele tapınmayız.”
19 Sai Nebukadnezzar ya husata da Shadrak, Meshak da Abednego, sai al’amuransa a kansu ya canja. Sai ya umarta a ƙara zuga wutar har sau bakwai domin tă yi zafi fiye da yadda take a dā.
Nebukadnessar Şadrak, Meşak, Abed-Nego'ya çok öfkelendi; onlara karşı tutumu değişti. Fırının her zamankinden yedi kat daha çok ısıtılmasını buyurdu.
20 Kuma ya umarci waɗansu ƙarfafan sojoji a cikin rundunarsa su daure Shadrak, Meshak da Abednego su jefa su cikin tanderun wutar.
Sonra ordusundaki bazı güçlü askerlere Şadrak'ı, Meşak'ı, Abed-Nego'yu bağlayıp kızgın fırına atmalarını buyurdu.
21 Waɗannan mutanen suna sanye da riguna, da wanduna, da rawani da waɗansu kayan sawa, aka daure su, aka jefa su cikin tanderun wuta.
Böylece bu kişiler, şalvarları, kaftanları, sarıkları ve öbür giysileriyle birlikte bağlanıp kızgın fırına atıldılar.
22 Sarki ya ba da umarnin da gaggawa kuma wutar ta yi zafi ƙwarai har harshen wutar ya kashe sojojin nan da suka ɗauki Shadrak, Meshak da Abednego,
Kralın buyruğu çok sıkı, fırın da çok ısıtılmış olduğundan, Şadrak'ı, Meşak'ı, Abed-Nego'yu götüren adamları ateşin alevleri yakıp öldürdü.
23 waɗannan mutane uku kuma a daure, suka fāɗa cikin tanderun wutar.
Üç adamsa –Şadrak, Meşak, Abed-Nego– bağlı olarak kızgın fırına düştüler.
24 Sai Sarki Nebukadnezzar ya miƙe tsaye, cike da mamaki ya tambayi mashawartansa, “Shin ba mutum uku ba ne muka daure muka jefa cikin wutar?” Suka amsa, “Tabbatacce haka yake ya sarki.”
O zaman Kral Nebukadnessar şaşkınlık içinde birden ayağa kalktı. Danışmanlarına, “Biz ateşin içine bağlı üç kişi atmadık mı?” diye sordu. Danışmanlar, “Kuşkusuz, ey kral” diye karşılık verdiler.
25 Sai ya ce, “Ku duba ina ganin mutum huɗu suna tafiya suna yawo a cikin wutar, a sake kuma babu abin da ya same su, na huɗun sai ka ce ɗan alloli.”
Kral, “Ben dört kişi görüyorum” dedi, “Ateşin içinde yürüyorlar, bağlarından çözülmüş, hiçbir zarara uğramamışlar. Dördüncünün görünümü de bir ilahi varlığa benziyor.”
26 Sai Nebukadnezzar ya matsa kusa da ƙofar tanderun wutar ya yi kira da ƙarfi, “Shedrak, Meshak da Abednego, bayin Allah Mafi Ɗaukaka ku fito! Ku zo nan!” Sai Shadrak, Meshak da Abednego suka fita daga cikin wutar,
Sonra kızgın fırının kapısına yaklaşarak, “Ey Yüce Tanrı'nın kulları Şadrak, Meşak, Abed-Nego, dışarı çıkıp buraya gelin!” diye seslendi. Bunun üzerine Şadrak, Meşak, Abed-Nego ateşin içinden çıktılar.
27 Sa’an nan hakimai, da wakilai, da gwamnoni da masu ba wa sarki shawara suka kewaya su. Suka ga wutar ba tă yi musu wani lahani a jikinsu ba, babu ko gashin kansu da ya ƙuna; ko warin wuta ma ba su yi ba.
Satraplar, kaymakamlar, valiler, kralın danışmanları onların çevresinde toplandılar. Adamların bedenlerinde ateşin hiçbir etkisi olmadığını gördüler. Başlarındaki tek saç yanmamış, giysileri değişmemiş, ateşin kokusu üzerlerine sinmemişti.
28 Sa’an nan Nebukadnezzar ya ce, “Yabo ya tabbata ga Allahn Shadrak, Meshak da Abednego wanda ya aiko da mala’ikansa ya ceci bayinsa da suka dogara matuƙa a gare shi, suka ki bin umarnin sarki kuma su na a shirye domin su ba da ransu da suka ƙi bauta ko su yi sujada ga wani allah sai dai Allahnsu.
Bunun üzerine Nebukadnessar, “Şadrak, Meşak ve Abed-Nego'nun Tanrısı'na övgüler olsun!” dedi, “Meleğini gönderip kendisine güvenen kullarını kurtardı. Onlar buyruğuma karşı geldiler, kendi Tanrıları'ndan başka bir ilaha kulluk edip tapınmamak için canlarını tehlikeye attılar.
29 Domin haka ina ba da doka cewa duk mutane da kowace al’umma ko kowane yaren da ya ce wani abu mummuna a kan Allahn Shadrak, Meshak da Abednego za a yanka shi gunduwa-gunduwa kuma gidansu zai zama wurin zuba shara, domin babu wani allahn da zai iya ceto ta irin wannan hanya.”
İşte buyuruyorum: Hangi halktan, ulustan ya da dilden olursa olsun, Şadrak, Meşak ve Abed-Nego'nun Tanrısı'ndan saygısızca söz eden herkes paramparça edilecek, evleri çöplüğe çevrilecek. Çünkü böyle kurtarabilen başka bir tanrı yoktur.”
30 Sa’an nan sarki ya ƙara wa su Shadrak, Meshak da Abednego girma a yankin Babilon.
Sonra Şadrak'ı, Meşak'ı, Abed-Nego'yu Babil İli'nde daha yüksek görevlere atadı.

< Daniyel 3 >