< Daniyel 3 >

1 Sarki Nebukadnezzar ya yi gunkin zinariya, tsawonsa kamu tasa’in, fāɗinsa kuma kamu tara ne, ya kafa shi a filin Dura a yankin Babilon.
نبوکدنصر پادشاه تمثالی از طلا که ارتفاعش شصت ذراع و عرضش شش ذراع بود ساخت و آن را در همواری دورا درولایت بابل نصب کرد.۱
2 Sa’an nan ya aika a kira hakimai da wakilai da gwamnoni da mashawarta, da ma’aji, da alƙalai, da marubutan kotu, da dukan sauran ma’aikatan yankunan, suka hallara domin a rusuna wa wannan siffar da ya kafa.
و نبوکدنصر پادشاه فرستاد که امرا و روسا و والیان و داوران وخزانه‌داران و مشیران و وکیلان و جمیع سروران ولایتها را جمع کنند تا به جهت تبرک تمثالی که نبوکدنصر پادشاه نصب نموده بود بیایند.۲
3 Saboda haka sai hakimai, da wakilai da gwamnoni, mashawarta da ma’aji da alƙalai, da marubutan alƙalai, da kuma dukan ma’aikatan yankunan suka tattaru domin kaddamar da siffar da Nebukadnezzar ya kafa, suka kuma tsaya a gabansa.
پس امرا و روسا و والیان و داوران و خزانه‌داران ومشیران و وکیلان و جمیع سروران ولایتها به جهت تبرک تمثالی که نبوکدنصر پادشاه نصب نموده بود جمع شده، پیش تمثالی که نبوکدنصرنصب کرده بود ایستادند.۳
4 Sai mai shela ya daga murya da ƙarfi ya ce, “Wannan shi ne abin da aka umarce ku ku yi, ya ku mutane da al’umma da kowane yare.
و منادی به آواز بلندندا کرده، می‌گفت: «ای قومها و امت‌ها و زبانهابرای شما حکم است؛۴
5 Da zarar kuka ji karar ƙaho, da sarewa, da garaya da goge da molo da algaita da kowane irin kaɗe-kaɗe da bushe-bushe ku rusuna ku yi sujada ga wannan gunkin da sarki Nebukadnezzar ya kafa.
که چون آواز کرنا و سرناو عود و بربط و سنتور و کمانچه و هر قسم آلات موسیقی را بشنوید، آنگاه به رو افتاده، تمثال طلارا که نبوکدنصر پادشاه نصب کرده است سجده نمایید.۵
6 Duk wanda bai rusuna ya yi sujada ba, nan take za a jefa shi a cikin tendarun wuta.”
و هر‌که به رو نیفتد و سجده ننماید درهمان ساعت در میان تون آتش ملتهب افکنده خواهد شد.»۶
7 Saboda haka, da zarar suka ji karar ƙaho, da sarewa, garaya da goge da kowane irin kaɗe-kaɗe da bushe-bushe da kowane irin kaɗe-kaɗe kowane mutum da ko wace al’umma da kowane irin yare suka sunkuya suka yi sujada ga wannan siffa ta zinariya da sarki Nebukadnezzar ya kafa.
لهذا چون همه قومها آواز کرنا و سرنا و عودو بربط و سنتور و هر قسم آلات موسیقی راشنیدند، همه قومها و امت‌ها و زبانها به رو افتاده، تمثال طلا را که نبوکدنصر پادشاه نصب کرده بودسجده نمودند.۷
8 A wannan lokaci sai waɗansu masanan taurari suka zo gaba suka yi karar Yahudawa.
اما در آنوقت بعضی کلدانیان نزدیک آمده، بر یهودیان شکایت آوردند،۸
9 Suka ce wa sarki Nebukadnezzar, “Ran sarki yă daɗe,
و به نبوکدنصر پادشاه عرض کرده، گفتند: «ای پادشاه تا به ابد زنده باش!۹
10 Ya sarki, ka fitar da doka, cewa duk wanda ya ji karar ƙaho, da sarewa, da garayu da goge, da molo da algaita da kowane irin kayan kaɗe-kaɗe da bushe-bushe sai yă rusuna yă yi sujada ga siffar zinariya,
تو‌ای پادشاه فرمانی صادرنمودی که هر‌که آواز کرنا و سرنا و عود و بربط وسنتور و کمانچه و هر قسم آلات موسیقی رابشنود به رو افتاده، تمثال طلا را سجده نماید.۱۰
11 kuma cewa duk wanda bai rusuna ya yi sujadar ba za a jefa shi cikin tanderun wuta.
و هر‌که به رو نیفتد و سجده ننماید در میان تون آتش ملتهب افکنده شود.۱۱
12 Amma sai ga waɗansu Yahudawa waɗanda ka ɗora su a kan harkokin yankin Babilon, wato, Shadrak, Meshak da Abednego waɗanda ba su kula da umarninka ba, ya sarki. Ba su bauta wa allolin ba balle su yi sujada ga gunkin zinariya da ka kafa.”
پس چند نفر یهودکه ایشان را بر کارهای ولایت بابل گماشته‌ای هستند، یعنی شدرک و میشک و عبدنغو. این اشخاص‌ای پادشاه، تو را احترام نمی نمایند وخدایان تو را عبادت نمی کنند و تمثال طلا را که نصب نموده‌ای سجده نمی نمایند.»۱۲
13 Cikin fushi da hasala, Nebukadnezzar ya aika a kira Shadrak, Meshak da Abednego. Aka kawo waɗannan mutane a gaban sarki,
آنگاه نبوکدنصر با خشم و غضب فرمود تاشدرک و میشک و عبدنغو را حاضر کنند. پس این اشخاص را در حضور پادشاه آوردند.۱۳
14 sai Nebukadnezzar ya ce musu, “Gaskiya ne Shadrak, Meshak da Abednego, cewa kun ƙi ku bauta wa alloli kuka kuma ƙi yi sujada ga gunkin da na kafa?
پس نبوکدنصر ایشان را خطاب کرده، گفت: «ای شدرک و میشک و عبدنغو! آیا شما عمد خدایان مرا نمی پرستید وتمثال طلا را که نصب نموده‌ام سجده نمی کنید؟۱۴
15 Yanzu sa’ad da kuka ji karar ƙaho, da sarewa, da garaya, da goge, da molo da algaita da kowane irin kaɗe-kaɗe da bushe-bushe, in kuna a shirye ku rusuna ƙasa ku yi wa wannan gunkin da na yi sujada, to, da kyau. Amma in ba ku yi sujada ba, za a je fa ku yanzu a cikin tanderun wutar nan. In ga kowane ne allahn nan da zai kuɓutar da ku daga hannuna?”
الان اگر مستعد بشوید که چون آواز کرنا و سرنا و عود و بربط و سنتور وکمانچه و هر قسم آلات موسیقی را بشنوید به روافتاده، تمثالی را که ساخته‌ام سجده نمایید، (فبها) و اما اگر سجده ننمایید، در همان ساعت در میان تون آتش ملتهب انداخته خواهید شد وکدام خدایی است که شما را از دست من رهایی دهد.»۱۵
16 Sai Shadrak, Meshak da Abednego suka amsa wa sarki suka ce, “Ya Nebukadnezzar, ba mu bukata mu kāre kanmu a gabanka a kan wannan batu.
شدرک و میشک و عبدنغو در جواب پادشاه گفتند: «ای نبوکدنصر! درباره این امر ما راباکی نیست که تو را جواب دهیم.۱۶
17 In an jefa mu cikin tanderun wutar nan, Allahn da muke bauta wa zai iya cetonmu daga ita, kuma ya sarki, zai cece mu daga hannunka.
اگر چنین است، خدای ما که او را می‌پرستیم قادر است که ما را از تون آتش ملتهب برهاند و او ما را از دست تو‌ای پادشاه خواهد رهانید.۱۷
18 Amma ko da bai cece mu ba, muna so ka sani, ya sarki; cewa ba za mu bauta wa allolinka ba ko kuma mu yi sujada ga gunkin zinariyar da ka kafa ba.”
و اگر نه، ای پادشاه تو را معلوم باد که خدایان تو را عبادت نخواهیم کرد و تمثال طلا را که نصب نموده‌ای سجده نخواهیم نمود.»۱۸
19 Sai Nebukadnezzar ya husata da Shadrak, Meshak da Abednego, sai al’amuransa a kansu ya canja. Sai ya umarta a ƙara zuga wutar har sau bakwai domin tă yi zafi fiye da yadda take a dā.
آنگاه نبوکدنصر از خشم مملو گردید وهیئت چهره‌اش بر شدرک و میشک و عبدنغومتغیر گشت و متکلم شده، فرمود تا تون را هفت چندان زیاده تر از عادتش بتابند.۱۹
20 Kuma ya umarci waɗansu ƙarfafan sojoji a cikin rundunarsa su daure Shadrak, Meshak da Abednego su jefa su cikin tanderun wutar.
و به قویترین شجاعان لشکر خود فرمود که شدرک و میشک وعبدنغو را ببندند و در تون آتش ملتهب بیندازند.۲۰
21 Waɗannan mutanen suna sanye da riguna, da wanduna, da rawani da waɗansu kayan sawa, aka daure su, aka jefa su cikin tanderun wuta.
پس این اشخاص را در رداها و جبه‌ها وعمامه‌ها و سایر لباسهای ایشان بستند و در میان تون آتش ملتهب افکندند.۲۱
22 Sarki ya ba da umarnin da gaggawa kuma wutar ta yi zafi ƙwarai har harshen wutar ya kashe sojojin nan da suka ɗauki Shadrak, Meshak da Abednego,
و چونکه فرمان پادشاه سخت بود و تون بی‌نهایت تابیده شده، شعله آتش آن کسان را که شدرک و میشک وعبدنغو را برداشته بودند کشت.۲۲
23 waɗannan mutane uku kuma a daure, suka fāɗa cikin tanderun wutar.
و این سه مردیعنی شدرک و میشک و عبدنغو در میان تون آتش ملتهب بسته افتادند.۲۳
24 Sai Sarki Nebukadnezzar ya miƙe tsaye, cike da mamaki ya tambayi mashawartansa, “Shin ba mutum uku ba ne muka daure muka jefa cikin wutar?” Suka amsa, “Tabbatacce haka yake ya sarki.”
آنگاه نبوکدنصر پادشاه در حیرت افتاد وبزودی هر‌چه تمامتر برخاست و مشیران خود راخطاب کرده، گفت: «آیا سه شخص نبستیم و درمیان آتش نینداختیم؟» ایشان در جواب پادشاه عرض کردند که «صحیح است‌ای پادشاه!»۲۴
25 Sai ya ce, “Ku duba ina ganin mutum huɗu suna tafiya suna yawo a cikin wutar, a sake kuma babu abin da ya same su, na huɗun sai ka ce ɗan alloli.”
اودر جواب گفت: «اینک من چهار مرد می‌بینم که گشاده در میان آتش می‌خرامند و ضرری به ایشان نرسیده است و منظر چهارمین شبیه پسرخدا است.»۲۵
26 Sai Nebukadnezzar ya matsa kusa da ƙofar tanderun wutar ya yi kira da ƙarfi, “Shedrak, Meshak da Abednego, bayin Allah Mafi Ɗaukaka ku fito! Ku zo nan!” Sai Shadrak, Meshak da Abednego suka fita daga cikin wutar,
پس نبوکدنصر به دهنه تون آتش ملتهب نزدیک آمد و خطاب کرده، گفت: «ای شدرک و میشک و عبدنغو! ای بندگان خدای تعالی بیرون شوید و بیایید.» پس شدرک و میشک و عبدنغو از میان آتش بیرون آمدند.۲۶
27 Sa’an nan hakimai, da wakilai, da gwamnoni da masu ba wa sarki shawara suka kewaya su. Suka ga wutar ba tă yi musu wani lahani a jikinsu ba, babu ko gashin kansu da ya ƙuna; ko warin wuta ma ba su yi ba.
و امرا وروسا و والیان و مشیران پادشاه جمع شده، آن مردان را دیدند که آتش به بدنهای ایشان اثری نکرده و مویی از سر ایشان نسوخته و رنگ ردای ایشان تبدیل نشده، بلکه بوی آتش به ایشان نرسیده است.۲۷
28 Sa’an nan Nebukadnezzar ya ce, “Yabo ya tabbata ga Allahn Shadrak, Meshak da Abednego wanda ya aiko da mala’ikansa ya ceci bayinsa da suka dogara matuƙa a gare shi, suka ki bin umarnin sarki kuma su na a shirye domin su ba da ransu da suka ƙi bauta ko su yi sujada ga wani allah sai dai Allahnsu.
آنگاه نبوکدنصر متکلم شده، گفت: «متبارک باد خدای شدرک و میشک و عبدنغو که فرشته خود را فرستاد و بندگان خویش را که بر اوتوکل داشتند و به فرمان پادشاه مخالفت ورزیدندو بدنهای خود را تسلیم نمودند تا خدای دیگری سوای خدای خویش را عبادت و سجده ننمایند، رهایی داده است.۲۸
29 Domin haka ina ba da doka cewa duk mutane da kowace al’umma ko kowane yaren da ya ce wani abu mummuna a kan Allahn Shadrak, Meshak da Abednego za a yanka shi gunduwa-gunduwa kuma gidansu zai zama wurin zuba shara, domin babu wani allahn da zai iya ceto ta irin wannan hanya.”
بنابراین فرمانی از من صادرشد که هر قوم و امت و زبان که حرف ناشایسته‌ای به ضد خدای شدرک و میشک و عبدنغو بگویند، پاره پاره شوند و خانه های ایشان به مزبله مبدل گردد، زیرا خدایی دیگر نیست که بدین منوال رهایی تواند داد.»۲۹
30 Sa’an nan sarki ya ƙara wa su Shadrak, Meshak da Abednego girma a yankin Babilon.
آنگاه پادشاه (منصب ) شدرک و میشک و عبدنغو را در ولایت بابل برتری داد.۳۰

< Daniyel 3 >