< Daniyel 2 >
1 A shekara ta biyu ta mulkinsa, Nebukadnezzar ya yi mafarkai; hankalinsa ya tashi har ya kāsa barci.
А друге године царовања Навуходоносоровог усни Навуходоносор сан, и узнемири му се дух и сан га прође.
2 Sai sarki ya sa aka tattara masa masu sihiri da masu dabo da bokaye da masanan taurari domin su faɗi abin da ya yi mafarki a kai. Da suka shigo suka tsaya a gaban sarki,
И рече цар да дозову враче и звездаре и гатаре и Халдеје да кажу цару сан његов. И дођоше и сташе пред царем.
3 sai ya ce musu, “Na yi mafarkin da ya dame ni kuma ina so in san me yake nufi.”
И рече им цар: Усних сан, и узнемири ми се дух како бих дознао шта сам снио.
4 Sai masanan taurarin suka amsa wa sarki da Arameyanci “Ran sarki yă daɗe! Ka faɗa wa bayinka mafarkin, mu kuma sai mu fassara.”
А Халдеји рекоше цару сирски: Царе, да си жив довека! Приповеди сан слугама својим, па ћемо ти казати шта значи.
5 Sai sarki ya amsa wa masanan taurarin ya ce, “Na mance da abin, idan ba ku tuno mini mafarkin, duk da fassararsa ba, to, za a daddatse ku gunduwa-gunduwa, a mai da gidajenku juji.
А цар одговори и рече Халдејима: Заборавио сам, ако ми не кажете шта сам снио и шта значи, бићете исечени и куће ће ваше бити буњишта.
6 Amma in har kuka faɗa mini mafarkina kuka kuma bayyana fassararsa, za ku sami lada mai girma. Saboda haka ku faɗa mini mafarkin da kuma fassararsa.”
Ако ли ми кажете шта сам снио и шта значи, добићете од мене даре и поклоне и велику част; кажите ми дакле шта сам снио и шта значи.
7 Sai suka sāke amsa masa suka ce, “Ran sarki yă daɗe, faɗa wa bayinka mafarkin, mu kuma za mu fassara shi.”
Одговорише опет и рекоше: Нека цар приповеди сан слугама својим, па ћемо казати шта значи.
8 Sai sarki ya amsa ya ce, “Na gane cewa kuna ƙoƙari ku ɓata lokaci ne kawai domin ku ga na manta da abin.
Цар одговори и рече: Доиста видим да хоћете времена да добијете; јер видите да сам заборавио.
9 In ba ku faɗa mini mafarkin ba, akwai hukunci guda ɗaya kurum dominku. Kun haɗa baki domin ku faɗa mini munanan al’amura domin ku ruɗe ni har lokaci yă wuce. Sai ku faɗa mini mafarkin, ta haka kuwa zan sani za ku iya yi mini fassararsa.”
Али ако ми не кажете шта сам снио и шта значи, један вам је суд; јер сте се договорили да кажете преда мном лаж и превару док се промени време; зато кажите ми сан, па ћу видети да ми можете казати шта значи.
10 Sai masanan taurarin suka amsa wa sarki suka ce, “Babu wani mutum a duniyan nan da zai iya yin abin da sarki yake nema! Babu wani sarki mai daraja da girma wanda ya taɓa yin irin wannan tambaya ga masu sihiri ko masu dabo ko masanan taurari.
Одговорише Халдеји цару и рекоше: Нема човека на земљи који би могао казати цару то шта иште; зато ниједан цар ни кнез ни властелин није никада искао такво шта од врача или звездара или Халдејца.
11 Abin da sarki yake nema yana da wuya matuƙa. Babu wani da zai iya bayyana wannan ga sarki sai dai alloli; kuma ba su zama tare da’yan adam.”
И шта цар иште врло је тешко; нити има другог који би могао казати цару осим богова, који не живе међу људима.
12 Wannan ya sa sarki ya fusata ƙwarai, ya ba da umarni a tafi da dukan masu hikima na Babilon a kashe su.
Зато се цар разљути и разгневи врло, и заповеди да се погубе сви мудраци вавилонски.
13 Sai aka ba da dokar da za a kashe masu hikima, sa’an nan aka aika mutane su je su nemo Daniyel da abokansa domin a kashe su.
И кад изиђе заповест, те убијаху мудраце, тражаху и Данила и другове његове да их убију.
14 Sa’ad da Ariyok, shugaban ƙungiyar matsaran sarki, ya fita domin yă kashe masu hikima na Babilon, sai Daniyel ya yi masa magana cikin hikima da dabara.
Тада Данило одговори мудро и разумно Ариоху заповеднику стражарском, који беше изашао да убија мудраце вавилонске;
15 Ya tambayi mai tsaro na sarki, “Me ya sa sarki ya fitar da wannan doka haka da fushi?” Sai Ariyok ya yi wa Daniyel bayanin batun.
Одговори и рече Ариоху, властелину царевом: Зашто је тако нагла заповест од цара? Тада Ариох каза ствар Данилу.
16 Da jin haka sai Daniyel ya tafi wurin sarki ya nemi ƙarin lokaci, domin yă bayyana wa sarki mafarkin da kuma fassararsa.
А Данило отиде и замоли цара да му остави времена, па ће казати цару шта сан значи.
17 Sa’an nan Daniyel ya komo gida ya kuma sanar wa abokansa Hananiya, Mishayel da Azariya, batun nan duka.
Потом отиде Данило кући својој, и каза ствар Ананији, Мисаилу и Азарији, друговима својим,
18 Ya roƙe su su roƙi jinƙan Allah na sama domin wannan mafarki, saboda kada a kashe shi da abokansa tare da sauran masu hikima na Babilon.
Да се моле за милост Богу небеском ради те тајне, да не би погинули Данило и другови му с осталим мудрацима вавилонским.
19 A wannan dare sai aka bayyana wa Daniyel mafarkin cikin wahayi. Daniyel kuwa ya ɗaukaka Allah na sama.
И објави се тајна Данилу, у ноћној утвари; тада Данило благослови Бога небеског.
20 Ya ce, “Yabo ya tabbata ga sunan Allah har abada abadin; hikima da iko nasa ne.
Проговори Данило и рече: Да је благословено име Господње од века до века; јер је Његова мудрост и сила;
21 Yana sāke lokuta, yana tuɓe sarakuna yana kuma naɗa waɗansu. Yana ba da hikima ga masu hikima kuma ilimi ga masu basira.
И Он мења времена и часе; смеће цареве, и поставља цареве; даје мудрост мудрима и разум разумнима.
22 Yakan bayyana zurfafa da ɓoyayyun abubuwa; ya san abin da yake cikin dare, haske kuwa yana zaune tare da shi.
Он открива шта је дубоко и сакривено, зна шта је у мраку, и светлост код Њега станује.
23 Na gode maka ina yabonka, Allah na kakannina. Kai ka san hikima da iko, ka sanar da ni abin da muka tambaye ka, ka kuma sanar da mu mafarkin sarki.”
Тебе, Боже отаца мојих, хвалим и славим, шта си ми дао мудрост и силу, и шта си ми објавио за шта Те молисмо објавив нам ствар цареву.
24 Sai Daniyel ya tafi wurin Ariyok, wanda sarki ya sa yă kashe masu hikiman Babilon, ya kuma ce masa, “Kada ka kashe masu hikiman Babilon ka kai ni wurin sarki, ni kuma zan fassara masa mafarkinsa.”
Тада отиде Данило к Ариоху, ког цар беше одредио да погуби мудраце вавилонске; и дошав овако му рече: Не губи мудраца вавилонских; изведи ме пред цара да кажем цару шта сан значи.
25 Sai Ariyok ya kai Daniyel wurin sarki nan take ya ce masa, “Na gano wani mutum daga cikin kamammun kabilar Yahuda wanda zai faɗa wa sarki abin da mafarkin yake nufi.”
Тада Ариох брже изведе Данила пред цара, и овако му рече: Нађох човека између робља Јудиног, који ће казати цару шта сан значи.
26 Sarki ya tambayi Daniyel (wanda ake kira Belteshazar), za ka iya faɗa mini mafarkin da na yi ka kuma fassara shi?
А цар проговори и рече Данилу, који се зваше Валтасар: Можеш ли ми казати сан који сам снио и шта значи?
27 Daniyel ya amsa, “Babu wani mai hikima, ko mai sihiri, ko mai dabo ko mai duban da zai iya warware wa sarki wannan matsala da ta dame shi,
Одговори Данило цару и рече: Тајну коју цар иште не могу казати цару мудраци ни звездари ни врачи ни гатари.
28 amma akwai Allahn da yake a sama wanda yake bayyana asirai, ya nuna wa sarki Nebukadnezzar abin da zai faru a kwanaki masu zuwa. Mafarkinka da wahayin da ya wuce cikin tunaninka a sa’ad da kake kwance a gadonka su ne,
Него има Бог на небу који открива тајне и јавља цару Навуходоносору шта ће бити до краја. Сан твој и шта ти је видела глава на постељи твојој ово је:
29 “A sa’ad da kake kwance, ya sarki, tunaninka ya ga al’amuran da suke zuwa, kuma shi mai bayyana al’amuran ya bayyana maka asiran abubuwan da za su faru.
Теби, царе, дођоше мисли на постељи шта ће бити после, и Онај који објављује тајне показа ти шта ће бити.
30 Amma ba a bayyana mini wannan asiri saboda ina da wata hikima fiye da sauran mutane ba, sai dai domin a sanar wa sarki da fassarar, ka kuma san tunanin da ya shiga zuciyarka.
А мени се ова тајна није објавила мудрошћу која би у мене била мимо све живе, него зато да се јави цару шта сан значи и да дознаш мисли срца свог.
31 “Ya sarki, ka ga wata babbar siffa, mai girma, siffa ce mai haske, abar bantsoro tana tsaye a gabanka.
Ти, царе, виде, а то лик велик; велик беше лик и светлост му силна, и стајаше према теби, и страшан беше на очима.
32 An yi kan wannan siffa da zinariya zalla, ƙirjinta da kuma hannuwanta an yi su da azurfa, cikinta da kuma cinyarta da tagulla ne.
Глава том лику беше од чистог злата, прси и мишице од сребра, трбух и бедра од бронзе,
33 An yi ƙafafun da ƙarfe, tafin ƙafafunta kuma an yi rabi da ƙarfe rabi kuma da yumɓu.
Ноге му од гвожђа, а стопала које од гвожђа које од земље.
34 A lokacin da kake dubawa, sai aka yanko wani dutse, amma ba da hannun mutum ba. Ya fāɗa a kan ƙafafun siffar na ƙarfen da aka haɗa da yumɓu aka kuma ragargaje su.
Ти гледаше докле се одвали камен без руку, и удари лик у стопала бронзана и земљана, и сатре их.
35 Sai ƙarfen da yambun da tagulla da azurfan da kuma zinariyan suka ragargaje a lokaci ɗaya ya zama kamar ƙaiƙayi a masussuka a lokacin kaka. Sai iska ta kwashe su ta tafi, har ba a iya ganin ko alamarsu. Amma dutsen da ya fāɗo a siffar ya girke ya zama tsauni ya kuma cika dukan duniya.
Тада се сатре и гвожђе и земља и бронза и сребро и злато, и поста као плева на гумну у лето, те однесе ветар, и не нађе му се место; а камен, који удари лик, поста гора велика и испуни сву земљу.
36 “Wannan shi ne mafarkin, yanzu kuma za mu fassara ta wa sarki.
То је сан; а сада ћемо казати цару шта значи.
37 Ya, sarki, kai ne sarkin sarakuna. Allah na sama ya ba ka iko da girma da suna;
Ти си, царе, цар над царевима, јер ти Бог небески даде царство, силу и крепост и славу,
38 a cikin hannunka ya sanya ɗan adam, da namun jeji da tsuntsayen sama. A duk inda suke zaune, ya maishe ka ka yi mulki a bisansu kai ne kan zinariyan nan na siffar.
И где год живе синови људски, звери пољске и птице небеске, дао ти је у руке, и поставио те господарем над свим тим. Ти си она глава златна.
39 “A bayanka, za a yi wani mulki, wanda bai kai naka ba. A gaba kuma, za a yi mulki na uku wanda yake na tagulla, zai yi mulkin dukan duniya.
А након тебе настаће друго царство, мање од твог; а потом треће царство, бронзано, које ће владати по свој земљи.
40 A ƙarshe, za a yi mulki na huɗu, mai ƙarfi kamar ƙarfe, Da yake baƙin ƙarfe yakan kakkarya, ya ragargaje abubuwa, haka nan wannan mulki zai ragargaje sauran mulkoki
А четврто ће царство бити тврдо као гвожђе, јер гвожђе сатире и троши све, и као гвожђе што све ломи, тако ће сатрти и поломити.
41 Ka kuma ga an yi ƙafafun da yatsotsin da baƙin ƙarfe gauraye da yumɓu, wato, mulkin zai rabu, amma zai kasance da ƙarfi kamar na baƙin ƙarfe da yake gauraye da yumɓu.
А што си видео стопала и прсте које од кала лончарског које од гвожђа, биће царство раздељено, али ће бити у њему тврђе од гвожђа, јер си видео гвожђе помешано с калом лончарским.
42 Kamar yadda yatsotsin rabi na ƙarfe rabi kuma na yumɓu ne, haka wannan mulki zai zama rabi mai ƙarfi rabi kuma marar ƙarfi.
И што прсти на ногама беху које од гвожђа које од кала, царство ће бити нешто јако, а нешто трошно.
43 Kamar dai yadda ka ga ƙarfen ya gauraye da yumɓu, haka mutanen za su zama a gauraye amma ba za su haɗu da juna ba, kamar yadda baƙin ƙarfe da yumɓu ba su haɗuwa.
А што си видео гвожђе помешано са калом лончарским, то ће се они помешати са семеном човечијим, али неће прионути један за другог као што се гвожђе не може смешати с калом.
44 “A lokacin mulkin waɗannan sarakunan, Allah na sama zai kafa mulki da ba zai taɓa rushewa ba, ba kuma za a ba ma waɗansu mutane ba. Zai ragargaje waɗannan mulkokin da kuma kawo su ga ƙarshe, amma shi wannan mulki zai dawwama har abada.
А у време тих царева Бог ће небески подигнути царство које се до века неће расути, и то се царство неће оставити другом народу; оно ће сатрти и укинути сва та царства, а само ће стајати до века.
45 Wannan shi ne ma’anar wannan wahayin da ka gani na dutsen da aka yanko daga jikin tsaunin, amma ba da hannun ɗan adam ba, dutsen da ya ragargaza ƙarfen, da tagullar, da yumɓun da azurfar da kuma zinariyar. “Allah mai girma ya nuna wa sarki abin da zai faru nan gaba. Mafarkin gaskiya ne, fassararsa kuma abin dogara ne.”
Како си видео где се од горе одвали камен без руку и сатре гвожђе, бронзу, као, сребро и злато. Бог велики јави цару шта ће бити после; сан је истинит, и тумачење му верно.
46 Sai sarki Nebukadnezzar ya fāɗi da fuskarsa har ƙasa a gaban Daniyel domin ya girmama shi ya kuma umarta a miƙa hadaya da kuma hadayar ƙonawa ta turare ga Daniyel.
Тада цар Навуходоносор паде на лице своје, и поклони се Данилу, и заповеди да му принесу принос и кад.
47 Sarki ya kuma ce wa Daniyel, “Tabbatacce Allahnka shi ne Allahn alloli da kuma Sarkin sarakuna da mai bayyana asirai, gama ka iya bayyana wannan asiri.”
Цар проговори Данилу и рече: Доиста, ваш је Бог Бог над боговима и Господар над царевима, и који објављује тајне, кад си могао открити ову тајну.
48 Sai sarki ya ɗora Daniyel a babban matsayi ya kuma sanya shi mai mulki a kan dukan yankin ƙasar Babilon; ya kuma ɗora shi yă zama mai kula da duk masu hikima.
Тада цар узвиси Данила, и даде му многе велике дарове и учини га господарем свој земљи вавилонској и поглаварем над свим мудрацима вавилонским.
49 Bugu da ƙari, bisa ga bukatar Daniyel sai sarki yă naɗa Shadrak da Meshak da Abednego su zama masu kula da harkokin lardin Babilon, amma Daniyel kuma ya tsaya a fadar sarki.
И Данило измоли у цара, те постави над пословима земље вавилонске Седраха, Мисаха и Авденага, а Данило оста на двору царевом.