< Daniyel 2 >

1 A shekara ta biyu ta mulkinsa, Nebukadnezzar ya yi mafarkai; hankalinsa ya tashi har ya kāsa barci.
Dans la deuxième année du règne de Nabuchodonosor, celui-ci eut des songes; son esprit en fut troublé et il perdit le sommeil.
2 Sai sarki ya sa aka tattara masa masu sihiri da masu dabo da bokaye da masanan taurari domin su faɗi abin da ya yi mafarki a kai. Da suka shigo suka tsaya a gaban sarki,
Le roi ordonna de mander devins, magiciens, sorciers et astrologues, afin qu’ils révélassent au roi ses songes. Quand ils furent venus et mis en présence du roi,
3 sai ya ce musu, “Na yi mafarkin da ya dame ni kuma ina so in san me yake nufi.”
celui-ci leur dit: "J’Ai eu un songe, et mon esprit est anxieux de connaître ce songe."
4 Sai masanan taurarin suka amsa wa sarki da Arameyanci “Ran sarki yă daɗe! Ka faɗa wa bayinka mafarkin, mu kuma sai mu fassara.”
Les astrologues répondirent au roi en araméen: "O roi, puisses-tu vivre éternellement! Expose le songe à tes serviteurs, et nous t’en donnerons l’explication."
5 Sai sarki ya amsa wa masanan taurarin ya ce, “Na mance da abin, idan ba ku tuno mini mafarkin, duk da fassararsa ba, to, za a daddatse ku gunduwa-gunduwa, a mai da gidajenku juji.
Le roi répliqua en disant aux astrologues: "C’Est une chose décidée par moi: si vous ne me faites pas connaître le songe et son interprétation, vous serez taillés en pièces, et vos maisons seront converties en cloaques.
6 Amma in har kuka faɗa mini mafarkina kuka kuma bayyana fassararsa, za ku sami lada mai girma. Saboda haka ku faɗa mini mafarkin da kuma fassararsa.”
Si, au contraire, vous révélez le songe et sa signification, vous recevrez de moi des dons, de riches présents et de grands honneurs; donc dévoilez-moi le songe et sa signification."
7 Sai suka sāke amsa masa suka ce, “Ran sarki yă daɗe, faɗa wa bayinka mafarkin, mu kuma za mu fassara shi.”
Eux de répondre pour la seconde fois: "Que le roi, dirent-ils, expose le songe à ses serviteurs, et nous en donnerons l’explication."
8 Sai sarki ya amsa ya ce, “Na gane cewa kuna ƙoƙari ku ɓata lokaci ne kawai domin ku ga na manta da abin.
A cela le roi répliqua: "Je sais parfaitement que vous voulez gagner du temps, parce que vous voyez que ma résolution est bien arrêtée.
9 In ba ku faɗa mini mafarkin ba, akwai hukunci guda ɗaya kurum dominku. Kun haɗa baki domin ku faɗa mini munanan al’amura domin ku ruɗe ni har lokaci yă wuce. Sai ku faɗa mini mafarkin, ta haka kuwa zan sani za ku iya yi mini fassararsa.”
Si donc vous ne me faites connaître le songe, un même arrêt vous atteindra. Vous vous êtes arrangés pour m’adresser des paroles fausses et mensongères, espérant que les circonstances pourront changer; c’est pourquoi dites-moi le songe, et je saurai que vous pourrez aussi m’en fournir l’explication."
10 Sai masanan taurarin suka amsa wa sarki suka ce, “Babu wani mutum a duniyan nan da zai iya yin abin da sarki yake nema! Babu wani sarki mai daraja da girma wanda ya taɓa yin irin wannan tambaya ga masu sihiri ko masu dabo ko masanan taurari.
Les astrologues reprirent la parole devant le roi et dirent: "II n’est nul homme sur la terre qui soit capable de dévoiler ce que demande le roi; aussi bien, jamais roi grand et puissant n’a exigé pareille chose d’aucun devin, ni magicien, ni astrologue.
11 Abin da sarki yake nema yana da wuya matuƙa. Babu wani da zai iya bayyana wannan ga sarki sai dai alloli; kuma ba su zama tare da’yan adam.”
La chose que demande le roi est malaisée, et il n’est personne d’autre capable de la dévoiler au roi que les dieux, qui ne séjournent pas au milieu des mortels."
12 Wannan ya sa sarki ya fusata ƙwarai, ya ba da umarni a tafi da dukan masu hikima na Babilon a kashe su.
Là-dessus, le roi s’irrita et entra dans une violente colère, et il ordonna de faire périr tous les sages de Babylone.
13 Sai aka ba da dokar da za a kashe masu hikima, sa’an nan aka aika mutane su je su nemo Daniyel da abokansa domin a kashe su.
L’Ordre fut publié et les sages allaient être mis à mort: on chercha aussi Daniel et ses compagnons pour les tuer.
14 Sa’ad da Ariyok, shugaban ƙungiyar matsaran sarki, ya fita domin yă kashe masu hikima na Babilon, sai Daniyel ya yi masa magana cikin hikima da dabara.
Alors Daniel répondit avec prudence et mesure à Arioc, chef des exécuteurs du roi, qui était sorti pour mettre à mort les sages de Babylone.
15 Ya tambayi mai tsaro na sarki, “Me ya sa sarki ya fitar da wannan doka haka da fushi?” Sai Ariyok ya yi wa Daniyel bayanin batun.
Il prit la parole et dit à Arioc, l’officier du roi: "Pourquoi cet édit rigoureux a-t-il été rendu par le roi?" Alors Arioc fit connaître l’affaire à Daniel.
16 Da jin haka sai Daniyel ya tafi wurin sarki ya nemi ƙarin lokaci, domin yă bayyana wa sarki mafarkin da kuma fassararsa.
Aussitôt Daniel alla demander au roi de lui accorder un délai qui lui permît de donner l’explication au roi.
17 Sa’an nan Daniyel ya komo gida ya kuma sanar wa abokansa Hananiya, Mishayel da Azariya, batun nan duka.
Puis, Daniel se rendit dans sa demeure et raconta la chose à ses compagnons, Hanania, Misaël et Azaria,
18 Ya roƙe su su roƙi jinƙan Allah na sama domin wannan mafarki, saboda kada a kashe shi da abokansa tare da sauran masu hikima na Babilon.
leur demandant d’implorer la miséricorde du Dieu du ciel au sujet de ce mystère, afin que Daniel et ses compagnons ne subissent pas la mort avec les autres sages de Babylone.
19 A wannan dare sai aka bayyana wa Daniyel mafarkin cikin wahayi. Daniyel kuwa ya ɗaukaka Allah na sama.
Alors le mystère fut dévoilé à Daniel dans une vision nocturne, et Daniel bénit le Dieu du ciel.
20 Ya ce, “Yabo ya tabbata ga sunan Allah har abada abadin; hikima da iko nasa ne.
Daniel prit la parole et dit: "Que le nom de Dieu soit béni d’éternité en éternité! Car à lui appartiennent la sagesse et la puissance.
21 Yana sāke lokuta, yana tuɓe sarakuna yana kuma naɗa waɗansu. Yana ba da hikima ga masu hikima kuma ilimi ga masu basira.
C’Est lui qui modifie les temps et les époques, qui tour à tour renverse les rois et élève les rois, qui donne la sagesse aux sages et la science à ceux qui savent comprendre.
22 Yakan bayyana zurfafa da ɓoyayyun abubuwa; ya san abin da yake cikin dare, haske kuwa yana zaune tare da shi.
C’Est lui qui révèle les choses profondes et cachées; il connaît ce que recèlent les ténèbres, et la lumière réside avec lui.
23 Na gode maka ina yabonka, Allah na kakannina. Kai ka san hikima da iko, ka sanar da ni abin da muka tambaye ka, ka kuma sanar da mu mafarkin sarki.”
C’Est toi, Dieu de mes pères, que je remercie et exalte pour m’avoir donné sagesse et force; et à l’heure présente, tu m’as fait connaître ce que nous t’avons demandé: ce qui préoccupe le roi, tu nous l’as fait connaître."
24 Sai Daniyel ya tafi wurin Ariyok, wanda sarki ya sa yă kashe masu hikiman Babilon, ya kuma ce masa, “Kada ka kashe masu hikiman Babilon ka kai ni wurin sarki, ni kuma zan fassara masa mafarkinsa.”
Sur cela, Daniel se rendit auprès d’Arioc, que le roi avait chargé d’exécuter les sages de Babylone; il alla et lui parla de la sorte: "Ne fais point mourir les sages de Babylone: introduis-moi auprès du roi, et je révélerai au roi l’interprétation de son songe."
25 Sai Ariyok ya kai Daniyel wurin sarki nan take ya ce masa, “Na gano wani mutum daga cikin kamammun kabilar Yahuda wanda zai faɗa wa sarki abin da mafarkin yake nufi.”
Aussitôt Arioc, en toute hâte, introduisit Daniel auprès du roi et lui dit: "J’Ai trouvé un homme parmi les exilés de Juda, qui fera connaître au roi l’interprétation de son songe."
26 Sarki ya tambayi Daniyel (wanda ake kira Belteshazar), za ka iya faɗa mini mafarkin da na yi ka kuma fassara shi?
Le roi prit la parole et dit à Daniel, qui portait le nom de Beltchaçar: "Est-il vrai que tu sois capable de me faire connaître le songe que j’ai eu et son explication?"
27 Daniyel ya amsa, “Babu wani mai hikima, ko mai sihiri, ko mai dabo ko mai duban da zai iya warware wa sarki wannan matsala da ta dame shi,
Daniel répliqua au roi: "Le mystère, dit-il, que veut éclaircir le roi, ni sages, ni devins, ni magiciens, ni astrologues ne peuvent le révéler au roi.
28 amma akwai Allahn da yake a sama wanda yake bayyana asirai, ya nuna wa sarki Nebukadnezzar abin da zai faru a kwanaki masu zuwa. Mafarkinka da wahayin da ya wuce cikin tunaninka a sa’ad da kake kwance a gadonka su ne,
Mais il est un Dieu au ciel, qui dévoile les secrets; c’est lui qui a révélé au roi ce qui arrivera dans la suite des temps. Ton songe et les visions qui ont frappé ton esprit sur ta couche, les voici:
29 “A sa’ad da kake kwance, ya sarki, tunaninka ya ga al’amuran da suke zuwa, kuma shi mai bayyana al’amuran ya bayyana maka asiran abubuwan da za su faru.
O roi, il a surgi en toi, sur ta couche, des pensées touchant ce qui arrivera dans la suite, et celui qui révèle les mystères t’a annoncé ce qui sera.
30 Amma ba a bayyana mini wannan asiri saboda ina da wata hikima fiye da sauran mutane ba, sai dai domin a sanar wa sarki da fassarar, ka kuma san tunanin da ya shiga zuciyarka.
Quant à moi, si ce mystère m’a été découvert, ce n’est pas que je possède une sagesse refusée à tous les vivants; mais c’est aux seules fins qu’on en apprenne la signification au roi, et que tu connaisses les pensées de ton cœur.
31 “Ya sarki, ka ga wata babbar siffa, mai girma, siffa ce mai haske, abar bantsoro tana tsaye a gabanka.
Toi, ô roi, tu regardais, et voilà qu’une formidable statue se dressait devant toi: cette statue était grande, d’un éclat extraordinaire et d’un aspect effrayant.
32 An yi kan wannan siffa da zinariya zalla, ƙirjinta da kuma hannuwanta an yi su da azurfa, cikinta da kuma cinyarta da tagulla ne.
Cette statue avait la tête d’or fin, la poitrine et les bras d’argent, le ventre et les cuisses d’airain,
33 An yi ƙafafun da ƙarfe, tafin ƙafafunta kuma an yi rabi da ƙarfe rabi kuma da yumɓu.
les jambes de fer et les pieds en partie de fer et en partie d’argile.
34 A lokacin da kake dubawa, sai aka yanko wani dutse, amma ba da hannun mutum ba. Ya fāɗa a kan ƙafafun siffar na ƙarfen da aka haɗa da yumɓu aka kuma ragargaje su.
Tu la regardais, quand une pierre, se détachant, sans l’intervention d’aucune main, vint frapper les pieds qui étaient de fer et d’argile et les broya.
35 Sai ƙarfen da yambun da tagulla da azurfan da kuma zinariyan suka ragargaje a lokaci ɗaya ya zama kamar ƙaiƙayi a masussuka a lokacin kaka. Sai iska ta kwashe su ta tafi, har ba a iya ganin ko alamarsu. Amma dutsen da ya fāɗo a siffar ya girke ya zama tsauni ya kuma cika dukan duniya.
Alors, du même coup, furent broyés le fer, l’argile, l’argent et l’or; ils devinrent comme la balle qui s’envole des aires de blé, et furent emportés par le vent, sans qu’il en restât aucun vestige; mais la pierre qui avait frappé la statue se changea en une grande montagne et remplit toute la terre.
36 “Wannan shi ne mafarkin, yanzu kuma za mu fassara ta wa sarki.
Tel était le songe; et ce qu’il signifie, nous allons le dire au roi:
37 Ya, sarki, kai ne sarkin sarakuna. Allah na sama ya ba ka iko da girma da suna;
Toi, ô roi, le roi des rois, à qui le Dieu du ciel a donné royauté et force, puissance et gloire;
38 a cikin hannunka ya sanya ɗan adam, da namun jeji da tsuntsayen sama. A duk inda suke zaune, ya maishe ka ka yi mulki a bisansu kai ne kan zinariyan nan na siffar.
toi, aux mains de qui il a livré tout ce qui habite sur la terre, les hommes, les bêtes des champs et les oiseaux du ciel, et qu’il a rendu maître de toutes choses, tu es la tête d’or.
39 “A bayanka, za a yi wani mulki, wanda bai kai naka ba. A gaba kuma, za a yi mulki na uku wanda yake na tagulla, zai yi mulkin dukan duniya.
Après toi, s’élèvera un autre empire, inférieur au tien; puis un troisième empire, qui sera d’airain et qui dominera sur toute la terre,
40 A ƙarshe, za a yi mulki na huɗu, mai ƙarfi kamar ƙarfe, Da yake baƙin ƙarfe yakan kakkarya, ya ragargaje abubuwa, haka nan wannan mulki zai ragargaje sauran mulkoki
puis viendra un quatrième empire, puissant comme le fer; puisque le fer broie et écrase tout, cet empire, pareil au fer qui brise tout le reste, ne fera qu’écraser et causer des ruines.
41 Ka kuma ga an yi ƙafafun da yatsotsin da baƙin ƙarfe gauraye da yumɓu, wato, mulkin zai rabu, amma zai kasance da ƙarfi kamar na baƙin ƙarfe da yake gauraye da yumɓu.
Et si tu as vu que tes pieds et les orteils étaient partie en argile de potier et partie en fer, c’est que ce sera un empire divisé; toutefois il aura en lui quelque chose de la solidité du fer, en raison de ce que tu as vu du fer mêlé avec de l’argile boueuse.
42 Kamar yadda yatsotsin rabi na ƙarfe rabi kuma na yumɓu ne, haka wannan mulki zai zama rabi mai ƙarfi rabi kuma marar ƙarfi.
Les orteils des pieds étaient partie de fer et partie d’argile: c’est que cet empire sera en partie fort et en partie fragile.
43 Kamar dai yadda ka ga ƙarfen ya gauraye da yumɓu, haka mutanen za su zama a gauraye amma ba za su haɗu da juna ba, kamar yadda baƙin ƙarfe da yumɓu ba su haɗuwa.
Et si tu as vu le fer mêlé avec de l’argile boueuse, c’est que ces deux parties se mêleront par des alliances humaines, mais sans qu’elles s’attachent solidement l’une à l’autre, pas plus que le fer ne s’amalgame avec l’argile.
44 “A lokacin mulkin waɗannan sarakunan, Allah na sama zai kafa mulki da ba zai taɓa rushewa ba, ba kuma za a ba ma waɗansu mutane ba. Zai ragargaje waɗannan mulkokin da kuma kawo su ga ƙarshe, amma shi wannan mulki zai dawwama har abada.
Et du temps de ces rois-là, le Dieu du ciel suscitera un empire qui ne sera jamais détruit, un empire qui ne cédera la place à aucun autre peuple: il écrasera et anéantira tous les autres empires et subsistera lui-même éternellement,
45 Wannan shi ne ma’anar wannan wahayin da ka gani na dutsen da aka yanko daga jikin tsaunin, amma ba da hannun ɗan adam ba, dutsen da ya ragargaza ƙarfen, da tagullar, da yumɓun da azurfar da kuma zinariyar. “Allah mai girma ya nuna wa sarki abin da zai faru nan gaba. Mafarkin gaskiya ne, fassararsa kuma abin dogara ne.”
tout comme tu as vu que de la montagne s’est détachée une pierre, sans l’intervention d’aucune main, et qu’elle a broyé le fer, l’airain, l’argile, l’argent et l’or. Un grand Dieu a révélé au roi ce qui arrivera dans la suite: certain est le songe et digne de foi son interprétation!"
46 Sai sarki Nebukadnezzar ya fāɗi da fuskarsa har ƙasa a gaban Daniyel domin ya girmama shi ya kuma umarta a miƙa hadaya da kuma hadayar ƙonawa ta turare ga Daniyel.
Alors le roi Nabuchodonosor se prosterna contre terre, puis s’agenouilla devant Daniel et ordonna de lui présenter des offrandes et des parfums.
47 Sarki ya kuma ce wa Daniyel, “Tabbatacce Allahnka shi ne Allahn alloli da kuma Sarkin sarakuna da mai bayyana asirai, gama ka iya bayyana wannan asiri.”
S’Adressant ensuite à Daniel, le roi lui dit: "En vérité, votre Dieu est le Dieu des dieux, le souverain des rois, le révélateur des mystères, puisque tu as pu dévoiler ce mystère-là."
48 Sai sarki ya ɗora Daniyel a babban matsayi ya kuma sanya shi mai mulki a kan dukan yankin ƙasar Babilon; ya kuma ɗora shi yă zama mai kula da duk masu hikima.
Alors le roi rendit de grands honneurs à Daniel, le combla de nombreux et riches présents, et l’institua gouverneur de toute la province de Babylone et chef suprême de tous les sages de Babylone.
49 Bugu da ƙari, bisa ga bukatar Daniyel sai sarki yă naɗa Shadrak da Meshak da Abednego su zama masu kula da harkokin lardin Babilon, amma Daniyel kuma ya tsaya a fadar sarki.
Et Daniel en ayant fait la demande au roi, celui-ci préposa Chadrac, Mêchac, et Abêd-Nego aux affaires de la province de Babylone, tandis que Daniel restait à la cour du roi.

< Daniyel 2 >